Sourate: Suratus Saff 

Verset : 10

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ هَلۡ أَدُلُّكُمۡ عَلَىٰ تِجَٰرَةٖ تُنجِيكُم مِّنۡ عَذَابٍ أَلِيمٖ

Ya ku waxanda suka yi imani, yanzu ba Na nuna muku ku wani ciniki da zai tserar da ku daga azaba mai raxaxi ba?



Sourate: Suratus Saff 

Verset : 11

تُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَتُجَٰهِدُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ بِأَمۡوَٰلِكُمۡ وَأَنفُسِكُمۡۚ ذَٰلِكُمۡ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

(Shi ne) ku yi imani da Allah da Manzonsa ku kuma yi jihadi don Allah da dukiyoyinku da rayukanku. Wannan shi ne ya fiye muku alheri, idan kun kasance kuna sane (da haka)



Sourate: Suratus Saff 

Verset : 12

يَغۡفِرۡ لَكُمۡ ذُنُوبَكُمۡ وَيُدۡخِلۡكُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ وَمَسَٰكِنَ طَيِّبَةٗ فِي جَنَّـٰتِ عَدۡنٖۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

(Idan kun yi haka) zai gafarta muku zunubanku Ya kuma shigar da ku gidajen Aljanna (waxanda) qoramu suke gudana ta qarqashinsu da kuma wuraren zama masu kyau, a cikin gidajen Aljanna na dawwama. Wannan shi ne babban rabo



Sourate: Suratus Saff 

Verset : 13

وَأُخۡرَىٰ تُحِبُّونَهَاۖ نَصۡرٞ مِّنَ ٱللَّهِ وَفَتۡحٞ قَرِيبٞۗ وَبَشِّرِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Da kuma wata xayar da kuke so; (watau) nasara daga Allah da kuma buxi a kusa. Ka kuma yi wa muminai albishir



Sourate: Suratus Saff 

Verset : 14

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ كُونُوٓاْ أَنصَارَ ٱللَّهِ كَمَا قَالَ عِيسَى ٱبۡنُ مَرۡيَمَ لِلۡحَوَارِيِّـۧنَ مَنۡ أَنصَارِيٓ إِلَى ٱللَّهِۖ قَالَ ٱلۡحَوَارِيُّونَ نَحۡنُ أَنصَارُ ٱللَّهِۖ فَـَٔامَنَت طَّآئِفَةٞ مِّنۢ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ وَكَفَرَت طَّآئِفَةٞۖ فَأَيَّدۡنَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ عَلَىٰ عَدُوِّهِمۡ فَأَصۡبَحُواْ ظَٰهِرِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku zama masu taimaka wa (addinin) Allah, kamar yadda Isa xan Maryamu ya ce da Hawariyawa[1]: “Su wane ne masu taimaka mini zuwa ga Allah?” Hawariyawan suka ce: “Mu ne masu taimaka wa Allah.” Sai wata qungiya daga Bani Isra’ila suka yi imani, wata qungiya kuma ta kafirta, sai Muka qarfafa waxanda suka yi imani a kan maqiyansu, sai suka wayi gari suna masu cin nasara


1- Su ne almajiransa da suka yi imani da shi.


Sourate: Suratut Tahrim

Verset : 9

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ جَٰهِدِ ٱلۡكُفَّارَ وَٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱغۡلُظۡ عَلَيۡهِمۡۚ وَمَأۡوَىٰهُمۡ جَهَنَّمُۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Ya kai wannan Annabi, ka yaqi kafirai da munafukai, ka kuma tsananta musu. Makomarsu kuma Jahannama ce; makoma kuwa ta munana



Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 1

وَٱلۡعَٰدِيَٰتِ ضَبۡحٗا

Na rantse da (dawaki) masu sukuwa suna kukan ciki



Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 2

فَٱلۡمُورِيَٰتِ قَدۡحٗا

Sannan masu bugun qyastu da kofatai[1]


1- Watau suna qyasta wuta da kofatansu idan suka daki duwatsu da su.


Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 3

فَٱلۡمُغِيرَٰتِ صُبۡحٗا

Sannan masu kai hari da asuba



Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 4

فَأَثَرۡنَ بِهِۦ نَقۡعٗا

Sai suka tayar da qura da ita (sukawar tasu)



Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 5

فَوَسَطۡنَ بِهِۦ جَمۡعًا

Sai kuma suka shiga tsakiyar taro (da mahayansu)