Sourate: Suratul Anfal

Verset : 45

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِذَا لَقِيتُمۡ فِئَةٗ فَٱثۡبُتُواْ وَٱذۡكُرُواْ ٱللَّهَ كَثِيرٗا لَّعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka haxu da wata qungiya (ta mayaqa), to sai ku dage, ku kuma ambaci Allah da yawa, don ku rabauta



Sourate: Suratul Anfal

Verset : 46

وَأَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ وَلَا تَنَٰزَعُواْ فَتَفۡشَلُواْ وَتَذۡهَبَ رِيحُكُمۡۖ وَٱصۡبِرُوٓاْۚ إِنَّ ٱللَّهَ مَعَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

Kuma ku bi Allah da Manzonsa, kada ku rarrabu sai ku zama matsorata kuma qarfinku ya tafi; ku kuma yi haquri. Lalle Allah Yana tare da masu haquri



Sourate: Suratul Anfal

Verset : 55

إِنَّ شَرَّ ٱلدَّوَآبِّ عِندَ ٱللَّهِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Lalle mafi sharrin masu tafiya a bayan qasa a wurin Allah (su ne) waxanda suka kafirta, don haka kuma su ba sa yin imani



Sourate: Suratul Anfal

Verset : 56

ٱلَّذِينَ عَٰهَدتَّ مِنۡهُمۡ ثُمَّ يَنقُضُونَ عَهۡدَهُمۡ فِي كُلِّ مَرَّةٖ وَهُمۡ لَا يَتَّقُونَ

Waxanda idan ka yi alqawari da su sai su warware alqawarinsu ko da yaushe, ba sa kuma kiyaye dokokin Allah (dangane da alqawari)



Sourate: Suratul Anfal

Verset : 57

فَإِمَّا تَثۡقَفَنَّهُمۡ فِي ٱلۡحَرۡبِ فَشَرِّدۡ بِهِم مَّنۡ خَلۡفَهُمۡ لَعَلَّهُمۡ يَذَّكَّرُونَ

Sannan idan ka haxu da su a wurin yaqi, to sai ka fatattaki na bayansu da su, don su (na bayan) sa wa’azantu



Sourate: Suratul Anfal

Verset : 60

وَأَعِدُّواْ لَهُم مَّا ٱسۡتَطَعۡتُم مِّن قُوَّةٖ وَمِن رِّبَاطِ ٱلۡخَيۡلِ تُرۡهِبُونَ بِهِۦ عَدُوَّ ٱللَّهِ وَعَدُوَّكُمۡ وَءَاخَرِينَ مِن دُونِهِمۡ لَا تَعۡلَمُونَهُمُ ٱللَّهُ يَعۡلَمُهُمۡۚ وَمَا تُنفِقُواْ مِن شَيۡءٖ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ يُوَفَّ إِلَيۡكُمۡ وَأَنتُمۡ لَا تُظۡلَمُونَ

Ku yi musu tanadin abin da kuke iyawa na qarfi da kuma tanadin xaurarrun dawakai, kuna tsorata maqiya Allah kuma maqiyanku da shi (tanadin), har kuma da wasu ban da su da ba ku san su ba, Allah ne kawai Ya san su. Kuma duk irin abin da kuka ciyar cikin hanyar Allah za a cika muku (ladanku) ba kuwa za a zalunce ku ba



Sourate: Suratul Anfal

Verset : 61

۞وَإِن جَنَحُواْ لِلسَّلۡمِ فَٱجۡنَحۡ لَهَا وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱللَّهِۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Idan kuma suka karkato ga sulhu, to sai kai ma ka karkato gare shi, ka kuma dogara ga Allah. Lalle Shi Mai ji ne Masani



Sourate: Suratul Anfal

Verset : 62

وَإِن يُرِيدُوٓاْ أَن يَخۡدَعُوكَ فَإِنَّ حَسۡبَكَ ٱللَّهُۚ هُوَ ٱلَّذِيٓ أَيَّدَكَ بِنَصۡرِهِۦ وَبِٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Idan kuma suka yi niyyar yaudarar ka, to lalle Allah Ya ishe ka. Shi ne wanda Ya qarfafe ka da taimakonsa da kuma muminai



Sourate: Suratul Anfal

Verset : 74

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَهَاجَرُواْ وَجَٰهَدُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَٱلَّذِينَ ءَاوَواْ وَّنَصَرُوٓاْ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ حَقّٗاۚ لَّهُم مَّغۡفِرَةٞ وَرِزۡقٞ كَرِيمٞ

Waxanda kuma suka yi imani kuma suka yi hijira suka kuma yi yaqi saboda Allah, da waxanda kuma suka sauki (masu hijira) suka kuma taimaka, waxannan su ne muminai na gaskiya. Suna da (sakamakon) gafara da kuma arziki na karamci



Sourate: Suratul Anfal

Verset : 75

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مِنۢ بَعۡدُ وَهَاجَرُواْ وَجَٰهَدُواْ مَعَكُمۡ فَأُوْلَـٰٓئِكَ مِنكُمۡۚ وَأُوْلُواْ ٱلۡأَرۡحَامِ بَعۡضُهُمۡ أَوۡلَىٰ بِبَعۡضٖ فِي كِتَٰبِ ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمُۢ

Waxanda kuma suka yi imani daga baya, suka kuma yi hijira, suka kuma yi yaqi tare da ku, to waxannan suna cikinku. ‘Yan’uwa na jini kuma su ne suka fi cancantar (gadon) junansu a cikin Littafin Allah. Lalle Allah Masani ne ga komai



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 5

فَإِذَا ٱنسَلَخَ ٱلۡأَشۡهُرُ ٱلۡحُرُمُ فَٱقۡتُلُواْ ٱلۡمُشۡرِكِينَ حَيۡثُ وَجَدتُّمُوهُمۡ وَخُذُوهُمۡ وَٱحۡصُرُوهُمۡ وَٱقۡعُدُواْ لَهُمۡ كُلَّ مَرۡصَدٖۚ فَإِن تَابُواْ وَأَقَامُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتَوُاْ ٱلزَّكَوٰةَ فَخَلُّواْ سَبِيلَهُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

To idan watanni masu alfarma suka wuce[1] sai ku yaqi mushrikai a duk inda kuka same su, ku kuma kama su ku tsare su ku kuma toshe musu kowace hanya. To amma idan sun tuba sun kuma tsai da salla kuma sun ba da zakka, to sai ku qyale su. Lalle Allah Mai gafara ne Mai jin qai


1- Su ne watanni huxu masu alfarma, watau Zulqi’ida da Zulhijja da Al-Muharram da Rajab.


Sourate: Suratut Tauba

Verset : 6

وَإِنۡ أَحَدٞ مِّنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ ٱسۡتَجَارَكَ فَأَجِرۡهُ حَتَّىٰ يَسۡمَعَ كَلَٰمَ ٱللَّهِ ثُمَّ أَبۡلِغۡهُ مَأۡمَنَهُۥۚ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ قَوۡمٞ لَّا يَعۡلَمُونَ

Kuma idan wani daga mushrikai ya nemi mafaka a wurinka to sai ka ba shi mafaka har ya samu damar jin zancen Allah, sannan ka isar da shi wurin amincewarsa. Wannan kuwa saboda lalle su mutane ne da ba sa sanin (gaskiya)



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 12

وَإِن نَّكَثُوٓاْ أَيۡمَٰنَهُم مِّنۢ بَعۡدِ عَهۡدِهِمۡ وَطَعَنُواْ فِي دِينِكُمۡ فَقَٰتِلُوٓاْ أَئِمَّةَ ٱلۡكُفۡرِ إِنَّهُمۡ لَآ أَيۡمَٰنَ لَهُمۡ لَعَلَّهُمۡ يَنتَهُونَ

Idan kuma suka warware rantsuwarsu bayan xaukar alqawarinsu, suka kuma soki addininku, to sai ku yaqi shugabannin kafirci, don kuwa ba su da alqawari, ko yin haka zai sa su daina



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 13

أَلَا تُقَٰتِلُونَ قَوۡمٗا نَّكَثُوٓاْ أَيۡمَٰنَهُمۡ وَهَمُّواْ بِإِخۡرَاجِ ٱلرَّسُولِ وَهُم بَدَءُوكُمۡ أَوَّلَ مَرَّةٍۚ أَتَخۡشَوۡنَهُمۡۚ فَٱللَّهُ أَحَقُّ أَن تَخۡشَوۡهُ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Yanzu ba za ku yaqi mutanen da suka warware alqawarinsu ba, kuma (tun farko) sun yi nufin fitar da Manzo (daga Makka), su ne kuma suka fara far muku da yaqi? Yanzu kwa riqa tsoron su? To Allah ne Ya fi cancantar ku ji tsoron Sa idan kun kasance muminai



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 14

قَٰتِلُوهُمۡ يُعَذِّبۡهُمُ ٱللَّهُ بِأَيۡدِيكُمۡ وَيُخۡزِهِمۡ وَيَنصُرۡكُمۡ عَلَيۡهِمۡ وَيَشۡفِ صُدُورَ قَوۡمٖ مُّؤۡمِنِينَ

Ku yaqe su, Allah zai azabtar da su ta hannayenku, Ya kuma kunyatar da su, kuma Ya taimake ku a kansu, Ya kuma warkar da zukatan muminai



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 15

وَيُذۡهِبۡ غَيۡظَ قُلُوبِهِمۡۗ وَيَتُوبُ ٱللَّهُ عَلَىٰ مَن يَشَآءُۗ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٌ

Ya kuma tafiyar da vacin ransu. Allah kuma Ya karvi tuban duk wanda Ya ga dama. Allah kuwa Masani ne, Mai hikima



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 16

أَمۡ حَسِبۡتُمۡ أَن تُتۡرَكُواْ وَلَمَّا يَعۡلَمِ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ جَٰهَدُواْ مِنكُمۡ وَلَمۡ يَتَّخِذُواْ مِن دُونِ ٱللَّهِ وَلَا رَسُولِهِۦ وَلَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَلِيجَةٗۚ وَٱللَّهُ خَبِيرُۢ بِمَا تَعۡمَلُونَ

Ko kuwa kuna tsammanin za a qyale ku ne (sakaka) alhali kuwa har yanzu Allah bai tantance waxanda suka yi jihadi ba a cikinku, ba su kuma riqi wasu masoya ba banda Allah da Manzonsa da muminai? Allah Mai cikakken sanin abin da kuke aikatawa ne



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 20

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَهَاجَرُواْ وَجَٰهَدُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡ أَعۡظَمُ دَرَجَةً عِندَ ٱللَّهِۚ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡفَآئِزُونَ

Waxanda suka yi imani kuma suka yi hijira suka yi jihadi saboda Allah da dukiyoyinsu da kawunansu su suka fi girman daraja a wurin Allah kuma waxannan su ne marabauta



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 24

قُلۡ إِن كَانَ ءَابَآؤُكُمۡ وَأَبۡنَآؤُكُمۡ وَإِخۡوَٰنُكُمۡ وَأَزۡوَٰجُكُمۡ وَعَشِيرَتُكُمۡ وَأَمۡوَٰلٌ ٱقۡتَرَفۡتُمُوهَا وَتِجَٰرَةٞ تَخۡشَوۡنَ كَسَادَهَا وَمَسَٰكِنُ تَرۡضَوۡنَهَآ أَحَبَّ إِلَيۡكُم مِّنَ ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَجِهَادٖ فِي سَبِيلِهِۦ فَتَرَبَّصُواْ حَتَّىٰ يَأۡتِيَ ٱللَّهُ بِأَمۡرِهِۦۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡفَٰسِقِينَ

Ka ce: “Idan iyayenku da ‘ya’yanku da matanku da danginku da dukiyoyin da kuka tara da kasuwanci da kuke tsoron gurguncewarsa da kuma gidajen da kuke sha’awa; idan har su kuka fi so fiye da Allah da Manzonsa da kuma jihadi saboda Shi, to sai ku saurara har Allah Ya zo da al’amarinsa. Allah kuwa ba Ya shiryar da mutane fasiqai.”



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 29

قَٰتِلُواْ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَلَا بِٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَلَا يُحَرِّمُونَ مَا حَرَّمَ ٱللَّهُ وَرَسُولُهُۥ وَلَا يَدِينُونَ دِينَ ٱلۡحَقِّ مِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ حَتَّىٰ يُعۡطُواْ ٱلۡجِزۡيَةَ عَن يَدٖ وَهُمۡ صَٰغِرُونَ

Ku yaqi waxanda ba sa yin imani da Allah da ranar lahira, ba kuma sa haramta abin da Allah da Manzonsa suka haramta, kuma ba sa yin addini na gaskiya, daga waxanda aka bai wa littafi har sai (sun yarda) za su ba da jizya[1] da hannunsu a qasqance


1- Jizya, ita ce dukiyar da ake karva daga hannun Yahudu da Nasara waxanda ake zaune da su lafiya a qasar Musulmi, domin xauke mu shiga rundunar Musulmi, sannan a ba su kariya daga abokan gaba. Ba a karvar zakka daga hannunsu, wannan haqqi ne da ya shafi Musulmi kaxai.


Sourate: Suratut Tauba

Verset : 36

إِنَّ عِدَّةَ ٱلشُّهُورِ عِندَ ٱللَّهِ ٱثۡنَا عَشَرَ شَهۡرٗا فِي كِتَٰبِ ٱللَّهِ يَوۡمَ خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ مِنۡهَآ أَرۡبَعَةٌ حُرُمٞۚ ذَٰلِكَ ٱلدِّينُ ٱلۡقَيِّمُۚ فَلَا تَظۡلِمُواْ فِيهِنَّ أَنفُسَكُمۡۚ وَقَٰتِلُواْ ٱلۡمُشۡرِكِينَ كَآفَّةٗ كَمَا يُقَٰتِلُونَكُمۡ كَآفَّةٗۚ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ مَعَ ٱلۡمُتَّقِينَ

Lalle adadin watanni a wurin Allah wata goma sha biyu ne a cikin littafin Allah, tun ranar da Ya halicci sammai da qasa, daga cikinsu akwai (wata) huxu masu alfarma[1]. Wannan shi ne addini madaidaici. To kada ku zalunci kanku a cikinsu[2], kuma ku yaqi mushrikai gaba xaya kamar yadda suke yaqar ku gaba xaya. Ku kuma sani cewa Allah Yana tare da masu taqawa


1- Su ne watan Zulqi’ida da Zulhijja da Al-Muharram da Rajab.


2- Watau ta hanyar shiga yaqi da wasu ko aikata miyagun laifuka.


Sourate: Suratut Tauba

Verset : 38

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَا لَكُمۡ إِذَا قِيلَ لَكُمُ ٱنفِرُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ ٱثَّاقَلۡتُمۡ إِلَى ٱلۡأَرۡضِۚ أَرَضِيتُم بِٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا مِنَ ٱلۡأٓخِرَةِۚ فَمَا مَتَٰعُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا فِي ٱلۡأٓخِرَةِ إِلَّا قَلِيلٌ

Ya ku waxanda suka yi imani, me ya same ku ne idan aka ce da ku ku fita yaqi saboda Allah sai ku yi nauyin jiki? Yanzu kun zavi rayuwar duniya a kan ta lahira? Ai jin daxin rayuwar duniya abu ne qanqani dangane da na lahira



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 39

إِلَّا تَنفِرُواْ يُعَذِّبۡكُمۡ عَذَابًا أَلِيمٗا وَيَسۡتَبۡدِلۡ قَوۡمًا غَيۡرَكُمۡ وَلَا تَضُرُّوهُ شَيۡـٔٗاۗ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ

Idan ba za ku fita (yaqi ba to (Allah) zai azabtar da ku da azaba mai raxaxi, Ya kuma canja wasu mutanen daban, ba kuwa za ku cutar da Shi da komai ba. Allah kuwa Mai iko ne a kan komai



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 40

إِلَّا تَنصُرُوهُ فَقَدۡ نَصَرَهُ ٱللَّهُ إِذۡ أَخۡرَجَهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ثَانِيَ ٱثۡنَيۡنِ إِذۡ هُمَا فِي ٱلۡغَارِ إِذۡ يَقُولُ لِصَٰحِبِهِۦ لَا تَحۡزَنۡ إِنَّ ٱللَّهَ مَعَنَاۖ فَأَنزَلَ ٱللَّهُ سَكِينَتَهُۥ عَلَيۡهِ وَأَيَّدَهُۥ بِجُنُودٖ لَّمۡ تَرَوۡهَا وَجَعَلَ كَلِمَةَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلسُّفۡلَىٰۗ وَكَلِمَةُ ٱللَّهِ هِيَ ٱلۡعُلۡيَاۗ وَٱللَّهُ عَزِيزٌ حَكِيمٌ

Idan ba ku taimake shi ba (watau Manzon Allah) to haqiqa Allah Ya taimake shi lokacin da kafirai suka fitar da shi (daga Makka), alhalin suna su biyu, lokacin da suke a cikin kogo, yayin da yake ce wa abokinsa (Abubakar): “Kada ka damu, lalle Allah yana tare da mu,” sai Allah Ya saukar masa da nutsuwarsa Ya kuma qarfafe shi da runduna wadda ba ku gan ta ba, Ya kuma sanya kalmar waxanda suka kafirta ta zama qaskantacciya. Kalmar Allah kuwa ita ce maxaukakiya. Allah kuma Mabuwayi ne, Mai hikima



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 41

ٱنفِرُواْ خِفَافٗا وَثِقَالٗا وَجَٰهِدُواْ بِأَمۡوَٰلِكُمۡ وَأَنفُسِكُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۚ ذَٰلِكُمۡ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Ku fita yaqi kuna da kuzari ko ba ku da shi, ku kuma yi yaqi da dukiyoyinku da kawunanku saboda Allah. Wannan ya fi alheri a gare ku, in kun kasance kun san (haka)



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 44

لَا يَسۡتَـٔۡذِنُكَ ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ أَن يُجَٰهِدُواْ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡۗ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلۡمُتَّقِينَ

Waxanda suka yi imani da Allah da ranar lahira ba sa neman izininka don kada su yi yaqi da dukiyoyinsu da kawunansu. Allah kuwa yana sane da masu taqawa



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 73

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ جَٰهِدِ ٱلۡكُفَّارَ وَٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱغۡلُظۡ عَلَيۡهِمۡۚ وَمَأۡوَىٰهُمۡ جَهَنَّمُۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Ya kai wannan Annabi, ka yaqi kafirai da munafukai ka kuma tsananta musu. Jahannama ce kuma makomarsu. Makoma kuwa ta munana



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 88

لَٰكِنِ ٱلرَّسُولُ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ جَٰهَدُواْ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡۚ وَأُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمُ ٱلۡخَيۡرَٰتُۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

Sai dai shi Manzo da waxanda suka yi imani tare da shi sun yi yaqi da dukiyoyinsu da kuma kawunansu. Waxannan kuwa suna da alherai; kuma waxannan su ne marabauta



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 89

أَعَدَّ ٱللَّهُ لَهُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

Allah Ya tanadar musu da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, suna masu dawwama a cikinsu. Wannan shi ne rabo mai girma



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 111

۞إِنَّ ٱللَّهَ ٱشۡتَرَىٰ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ أَنفُسَهُمۡ وَأَمۡوَٰلَهُم بِأَنَّ لَهُمُ ٱلۡجَنَّةَۚ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ فَيَقۡتُلُونَ وَيُقۡتَلُونَۖ وَعۡدًا عَلَيۡهِ حَقّٗا فِي ٱلتَّوۡرَىٰةِ وَٱلۡإِنجِيلِ وَٱلۡقُرۡءَانِۚ وَمَنۡ أَوۡفَىٰ بِعَهۡدِهِۦ مِنَ ٱللَّهِۚ فَٱسۡتَبۡشِرُواْ بِبَيۡعِكُمُ ٱلَّذِي بَايَعۡتُم بِهِۦۚ وَذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

Lalle Allah Ya sayi rayuka da dukiyoyin muminai daga wurinsu cewa suna da Aljanna: Za su yi yaqi saboda Allah, sai su kashe su ma kuma a kashe su. Alqawari ne na gaskiya da Ya xaukar wa kansa a cikin Attaura da Linjila da Alqur’ani. Wane ne ya fi Allah cika alqawarinsa? Saboda haka sai ku yi farin ciki da cinikin nan naku da kuka yi da Shi. Wannan kuwa shi ne rabo mai girma