Sourate: Suratul Baqara

Verset : 100

أَوَكُلَّمَا عَٰهَدُواْ عَهۡدٗا نَّبَذَهُۥ فَرِيقٞ مِّنۡهُمۚ بَلۡ أَكۡثَرُهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Yanzu ashe duk sa’adda suka qulla wani alqawari sai wani vangare daga cikinsu ya yi watsi da shi?! Bari! Yawancinsu ba sa yin imani



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 101

وَلَمَّا جَآءَهُمۡ رَسُولٞ مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِ مُصَدِّقٞ لِّمَا مَعَهُمۡ نَبَذَ فَرِيقٞ مِّنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ كِتَٰبَ ٱللَّهِ وَرَآءَ ظُهُورِهِمۡ كَأَنَّهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Yayin da wani manzo daga Allah ya zo musu yana mai gaskata abin da yake tare da su (na Littafin Attaura), sai wani vangare daga cikinsu suka jefar da littafin Allah a bayansu kamar ba su san komai ba



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 102

وَٱتَّبَعُواْ مَا تَتۡلُواْ ٱلشَّيَٰطِينُ عَلَىٰ مُلۡكِ سُلَيۡمَٰنَۖ وَمَا كَفَرَ سُلَيۡمَٰنُ وَلَٰكِنَّ ٱلشَّيَٰطِينَ كَفَرُواْ يُعَلِّمُونَ ٱلنَّاسَ ٱلسِّحۡرَ وَمَآ أُنزِلَ عَلَى ٱلۡمَلَكَيۡنِ بِبَابِلَ هَٰرُوتَ وَمَٰرُوتَۚ وَمَا يُعَلِّمَانِ مِنۡ أَحَدٍ حَتَّىٰ يَقُولَآ إِنَّمَا نَحۡنُ فِتۡنَةٞ فَلَا تَكۡفُرۡۖ فَيَتَعَلَّمُونَ مِنۡهُمَا مَا يُفَرِّقُونَ بِهِۦ بَيۡنَ ٱلۡمَرۡءِ وَزَوۡجِهِۦۚ وَمَا هُم بِضَآرِّينَ بِهِۦ مِنۡ أَحَدٍ إِلَّا بِإِذۡنِ ٱللَّهِۚ وَيَتَعَلَّمُونَ مَا يَضُرُّهُمۡ وَلَا يَنفَعُهُمۡۚ وَلَقَدۡ عَلِمُواْ لَمَنِ ٱشۡتَرَىٰهُ مَا لَهُۥ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ مِنۡ خَلَٰقٖۚ وَلَبِئۡسَ مَا شَرَوۡاْ بِهِۦٓ أَنفُسَهُمۡۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Sai suka bi abin da shexanu suke karantawa a (zamanin) mulkin Sulaimanu; kuma Sulaimanu bai kafirta ba, sai dai shexanun su ne suka kafirta; suna koya wa mutane tsafi da abin da aka saukar wa mala’iku biyu, Haruta da Maruta, a garin Babila. Kuma ba sa koya wa wani (tsafin) har sai sun faxa masa cewa: “Mu fa jarraba ce, don haka kada ka kafirta”. Sai (mutane) suka riqa koyo daga wajensu su biyu abin da suke raba tsakanin miji da matarsa da shi. Kuma ba za su iya cutar da wani da shi ba sai da izinin Allah. Sai su koyi abin da zai cutar da su kuma ba zai amfane su ba. Kuma haqiqa sun san cewa, tabbas duk wanda ya zavi (sihiri) ba shi da wani rabo a lahira. Kuma lalle tir da abin da suka sayar da kawunansu da shi, da a ce sun san (haqiqanin makomarsu)



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 103

وَلَوۡ أَنَّهُمۡ ءَامَنُواْ وَٱتَّقَوۡاْ لَمَثُوبَةٞ مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِ خَيۡرٞۚ لَّوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Da a ce su sun yi imani kuma sun yi taqawa, haqiqa da sakamakon (da za su samu) daga Allah shi ne mafi alheri, da a ce sun sani



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 122

يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتِيَ ٱلَّتِيٓ أَنۡعَمۡتُ عَلَيۡكُمۡ وَأَنِّي فَضَّلۡتُكُمۡ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ya ku Banu Isra’ila, ku tuna ni’imar da Na yi muku, kuma lalle Ni Na fifita ku a kan sauran mutanen duniya (na zamaninku)



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 123

وَٱتَّقُواْ يَوۡمٗا لَّا تَجۡزِي نَفۡسٌ عَن نَّفۡسٖ شَيۡـٔٗا وَلَا يُقۡبَلُ مِنۡهَا عَدۡلٞ وَلَا تَنفَعُهَا شَفَٰعَةٞ وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ

Kuma ku kiyayi wani yini da wani rai ba zai isar wa da wani rai komai ba, kuma ba za a karvi wata fansa daga gare shi ba, kuma ceto ba zai amfane shi ba, kuma su ba za a taimaka musu ba



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 246

أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلۡمَلَإِ مِنۢ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ مِنۢ بَعۡدِ مُوسَىٰٓ إِذۡ قَالُواْ لِنَبِيّٖ لَّهُمُ ٱبۡعَثۡ لَنَا مَلِكٗا نُّقَٰتِلۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ قَالَ هَلۡ عَسَيۡتُمۡ إِن كُتِبَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡقِتَالُ أَلَّا تُقَٰتِلُواْۖ قَالُواْ وَمَا لَنَآ أَلَّا نُقَٰتِلَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَقَدۡ أُخۡرِجۡنَا مِن دِيَٰرِنَا وَأَبۡنَآئِنَاۖ فَلَمَّا كُتِبَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقِتَالُ تَوَلَّوۡاْ إِلَّا قَلِيلٗا مِّنۡهُمۡۚ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلظَّـٰلِمِينَ

Shin ba ka ga wasu manyan mutane ba daga cikin Banu Isra’ila bayan (mutuwar) Musa yayin da suka faxa wa Annabinsu: “Ka naxa mana wani sarki, wanda za mu yi yaqi (tare da shi) don xaukaka kalmar Allah?” Sai ya ce: “Shin ba kwa tsammanin idan an wajabta muku yaqi, ba za ku yi yaqin ba?” Sai suka ce: “Me zai sa ba za mu yi yaqi don xaukaka kalmar Allah ba, alhali kuwa an fitar da mu daga gidajenmu da ‘ya’yanmu?” To yayin da aka wajabta musu yaqin sai suka juya baya sai ‘yan kaxan daga cikinsu. Kuma Allah Masanin azzalumai ne



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 247

وَقَالَ لَهُمۡ نَبِيُّهُمۡ إِنَّ ٱللَّهَ قَدۡ بَعَثَ لَكُمۡ طَالُوتَ مَلِكٗاۚ قَالُوٓاْ أَنَّىٰ يَكُونُ لَهُ ٱلۡمُلۡكُ عَلَيۡنَا وَنَحۡنُ أَحَقُّ بِٱلۡمُلۡكِ مِنۡهُ وَلَمۡ يُؤۡتَ سَعَةٗ مِّنَ ٱلۡمَالِۚ قَالَ إِنَّ ٱللَّهَ ٱصۡطَفَىٰهُ عَلَيۡكُمۡ وَزَادَهُۥ بَسۡطَةٗ فِي ٱلۡعِلۡمِ وَٱلۡجِسۡمِۖ وَٱللَّهُ يُؤۡتِي مُلۡكَهُۥ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ وَٰسِعٌ عَلِيمٞ

Kuma Annabinsu ya ce da su: “Lalle haqiqa Allah Ya naxa Xalutu ya zama Sarki gare ku.” Sai suka ce: “Ta yaya zai samu sarauta a kanmu, alhalin mun fi shi cancatar sarauta, kuma ba a ba shi yalwar dukiya ba?” Sai ya ce: “Lalle Allah Ya zave shi a kanku, kuma Ya qare shi da yalwar ilimi da ta girman jiki, kuma Allah Yana bayar da mulkinsa ga wanda Ya ga dama, kuma Allah Mai yalwa ne, Masani.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 248

وَقَالَ لَهُمۡ نَبِيُّهُمۡ إِنَّ ءَايَةَ مُلۡكِهِۦٓ أَن يَأۡتِيَكُمُ ٱلتَّابُوتُ فِيهِ سَكِينَةٞ مِّن رَّبِّكُمۡ وَبَقِيَّةٞ مِّمَّا تَرَكَ ءَالُ مُوسَىٰ وَءَالُ هَٰرُونَ تَحۡمِلُهُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لَّكُمۡ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Sai Annabinsu ya ce da su: “Lalle alamar (cancantar) mulkinsa ita ce akwatin nan da zai zo muku wanda a cikinsa akwai nutsuwa daga Ubangijinku da kuma sauran abin da iyalin Musa suka bari da iyalin Haruna; mala’iku na xauke da shi. Lalle a cikin wannan tabbas akwai aya a gare ku, in kun kasance muminai.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 249

فَلَمَّا فَصَلَ طَالُوتُ بِٱلۡجُنُودِ قَالَ إِنَّ ٱللَّهَ مُبۡتَلِيكُم بِنَهَرٖ فَمَن شَرِبَ مِنۡهُ فَلَيۡسَ مِنِّي وَمَن لَّمۡ يَطۡعَمۡهُ فَإِنَّهُۥ مِنِّيٓ إِلَّا مَنِ ٱغۡتَرَفَ غُرۡفَةَۢ بِيَدِهِۦۚ فَشَرِبُواْ مِنۡهُ إِلَّا قَلِيلٗا مِّنۡهُمۡۚ فَلَمَّا جَاوَزَهُۥ هُوَ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ قَالُواْ لَا طَاقَةَ لَنَا ٱلۡيَوۡمَ بِجَالُوتَ وَجُنُودِهِۦۚ قَالَ ٱلَّذِينَ يَظُنُّونَ أَنَّهُم مُّلَٰقُواْ ٱللَّهِ كَم مِّن فِئَةٖ قَلِيلَةٍ غَلَبَتۡ فِئَةٗ كَثِيرَةَۢ بِإِذۡنِ ٱللَّهِۗ وَٱللَّهُ مَعَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

To yayin da Xalutu ya fita (bayan gari) da rundunarsa, sai ya ce: “Lalle Allah zai jarrabe ku da wata qorama, to duk wanda ya sha daga gare ta, to ba ya tare da ni, duk wanda kuwa bai sha ba, to wannan yana tare da ni, sai dai wanda ya kamfata sau xaya da (tafin) hannunsa.” Gaba xayansu sai suka sha daga cikinta sai ‘yan kaxan daga cikinsu (su ne ba su sha ba). To yayin da ya qetare shi, shi da waxanda suka yi imani tare da shi, sai suka ce: “A yau kam ba mu da iko wajen fuskantar Jalutu da rundunarsa.” Sai waxanda suke da yaqinin cewa za su haxu da Allah suka ce: “Sau da yawa wata runduna ‘yan kaxan takan yi rinjaye a kan wata runduna mai yawa da izinin Allah. Kuma Allah Yana tare da masu haquri.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 250

وَلَمَّا بَرَزُواْ لِجَالُوتَ وَجُنُودِهِۦ قَالُواْ رَبَّنَآ أَفۡرِغۡ عَلَيۡنَا صَبۡرٗا وَثَبِّتۡ أَقۡدَامَنَا وَٱنصُرۡنَا عَلَى ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma yayin da suka yi fito-na-fito da Jalutu da rundunarsa, sai suka ce: “Ya Ubangijinmu, Ka zubo mana haquri na musamman, kuma Ka tabbatar da dugaduganmu, kuma Ka taimake mu a kan mutane kafirai.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 251

فَهَزَمُوهُم بِإِذۡنِ ٱللَّهِ وَقَتَلَ دَاوُۥدُ جَالُوتَ وَءَاتَىٰهُ ٱللَّهُ ٱلۡمُلۡكَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَعَلَّمَهُۥ مِمَّا يَشَآءُۗ وَلَوۡلَا دَفۡعُ ٱللَّهِ ٱلنَّاسَ بَعۡضَهُم بِبَعۡضٖ لَّفَسَدَتِ ٱلۡأَرۡضُ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ ذُو فَضۡلٍ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Sai suka murqushe su da izinin Allah, kuma Dawudu ya kashe Jalutu, sai Allah Ya ba shi mulki da hikima, kuma Ya sanar da shi irin abin da Ya ga dama. Ba don yadda Allah Yake kare wani sashin mutane da wani sashi ba, to lalle da qasa ta lalace, sai dai kuma Allah Ma’abocin falala ne ga talikai



Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 93

۞كُلُّ ٱلطَّعَامِ كَانَ حِلّٗا لِّبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ إِلَّا مَا حَرَّمَ إِسۡرَـٰٓءِيلُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ مِن قَبۡلِ أَن تُنَزَّلَ ٱلتَّوۡرَىٰةُۚ قُلۡ فَأۡتُواْ بِٱلتَّوۡرَىٰةِ فَٱتۡلُوهَآ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Duk wani abinci ya kasance halal ne ga Banu Israila sai abin da shi Isra’ilu[1] ya haramta wa kansa tun kafin a saukar da Attaura. Ka ce: “To ku zo da Attaura, sai ku karanta ta in kun kasance masu gaskiya.”


1- Isra’ilu: shi ne Annabi Ya’aqub (). Ya haramta wa kansa ne cin naman raquma da shan nononsu. Sannan daga baya su ma ‘ya’yansa suka yi koyi da shi.


Sourate: Suratu Ali-Imran

Verset : 94

فَمَنِ ٱفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ ٱلۡكَذِبَ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

To duk wanda ya qirqiri qarya ya jingina wa Allah bayan wannan, to waxannan su ne azzalumai



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 12

۞وَلَقَدۡ أَخَذَ ٱللَّهُ مِيثَٰقَ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ وَبَعَثۡنَا مِنۡهُمُ ٱثۡنَيۡ عَشَرَ نَقِيبٗاۖ وَقَالَ ٱللَّهُ إِنِّي مَعَكُمۡۖ لَئِنۡ أَقَمۡتُمُ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتَيۡتُمُ ٱلزَّكَوٰةَ وَءَامَنتُم بِرُسُلِي وَعَزَّرۡتُمُوهُمۡ وَأَقۡرَضۡتُمُ ٱللَّهَ قَرۡضًا حَسَنٗا لَّأُكَفِّرَنَّ عَنكُمۡ سَيِّـَٔاتِكُمۡ وَلَأُدۡخِلَنَّكُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ فَمَن كَفَرَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ مِنكُمۡ فَقَدۡ ضَلَّ سَوَآءَ ٱلسَّبِيلِ

Kuma lalle haqiqa Allah Ya xauki alqawari (daga) Banu-Isra’ila, kuma Mun aiko musu wakilai goma sha biyu daga cikinsu; kuma Allah Ya ce: “Lalle Ni Ina tare da ku; tabbas idan har kuka tsayar da salla, kuma kuka bayar da zakka, kuma kuka yi imani da manzannina, kuma kuka qarfafe su, kuma kuka bai wa Allah kyakkyawan rance, to lalle zan kankare muku kurakuranku, kuma zan shigar da ku gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. To duk wanda ya kafirce daga cikinku bayan haka, to haqiqa ya vace wa tafarki madaidaici.”



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 13

فَبِمَا نَقۡضِهِم مِّيثَٰقَهُمۡ لَعَنَّـٰهُمۡ وَجَعَلۡنَا قُلُوبَهُمۡ قَٰسِيَةٗۖ يُحَرِّفُونَ ٱلۡكَلِمَ عَن مَّوَاضِعِهِۦ وَنَسُواْ حَظّٗا مِّمَّا ذُكِّرُواْ بِهِۦۚ وَلَا تَزَالُ تَطَّلِعُ عَلَىٰ خَآئِنَةٖ مِّنۡهُمۡ إِلَّا قَلِيلٗا مِّنۡهُمۡۖ فَٱعۡفُ عَنۡهُمۡ وَٱصۡفَحۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Saboda yadda suke warware alqawarin da aka yi da su, sai Muka la’ance su, kuma Muka sanya zukatansu suka zamo qeqasassu; suna jirkita magana daga wurinta, kuma sun bar wani rabo na abin da aka yi musu wa’azi da shi. Kuma ba za ka gushe ba kana ganin ha’inci daga gare su, sai ‘yan kaxan daga cikinsu. To sai ka yi musu afuwa, kuma ka kawar da kai, lalle Allah Yana son masu kyautatawa



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 20

وَإِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦ يَٰقَوۡمِ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَةَ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ إِذۡ جَعَلَ فِيكُمۡ أَنۢبِيَآءَ وَجَعَلَكُم مُّلُوكٗا وَءَاتَىٰكُم مَّا لَمۡ يُؤۡتِ أَحَدٗا مِّنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Kuma (ka tuna) lokacin da Musa ya ce wa mutanensa: “Ya ku mutanena, ku tuna ni’imar Allah da Ya yi muku, yayin da Ya sanya annabawa da yawa a cikinku, kuma Ya sanya ku sarakuna, kuma Ya ba ku irin abin da bai ba wa wani cikin talikai ba



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 21

يَٰقَوۡمِ ٱدۡخُلُواْ ٱلۡأَرۡضَ ٱلۡمُقَدَّسَةَ ٱلَّتِي كَتَبَ ٱللَّهُ لَكُمۡ وَلَا تَرۡتَدُّواْ عَلَىٰٓ أَدۡبَارِكُمۡ فَتَنقَلِبُواْ خَٰسِرِينَ

“Ya ku mutanena, ku shiga qasar nan mai tsarki[1], wadda Allah Ya wajabta muku (shigarta), kuma kada ku yarda ku juya baya, sai ku komo kuna hasararru.”


1- Qasa mai tsarki ita ce Baitul Maqdis.


Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 22

قَالُواْ يَٰمُوسَىٰٓ إِنَّ فِيهَا قَوۡمٗا جَبَّارِينَ وَإِنَّا لَن نَّدۡخُلَهَا حَتَّىٰ يَخۡرُجُواْ مِنۡهَا فَإِن يَخۡرُجُواْ مِنۡهَا فَإِنَّا دَٰخِلُونَ

Suka ce, “Ya kai Musa, lalle a cikinta akwai waxansu mutane masu tsananin qarfi, kuma mu ba za mu shige ta ba har sai sun fita daga cikinta, don haka idan suka fita daga cikinta, to lalle za mu shiga.”



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 23

قَالَ رَجُلَانِ مِنَ ٱلَّذِينَ يَخَافُونَ أَنۡعَمَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمَا ٱدۡخُلُواْ عَلَيۡهِمُ ٱلۡبَابَ فَإِذَا دَخَلۡتُمُوهُ فَإِنَّكُمۡ غَٰلِبُونَۚ وَعَلَى ٱللَّهِ فَتَوَكَّلُوٓاْ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Waxansu mutane biyu daga cikin masu jin tsoron (Allah), waxanda Allah Ya yi musu ni’ima (ta imani), suka ce: “Ku shigar musu ta qofar (garin); idan har kun shige shi, to lalle ku masu cin nasara ne. Kuma ga Allah kaxai za ku dogara, idan kun kasance ku muminai ne.”



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 24

قَالُواْ يَٰمُوسَىٰٓ إِنَّا لَن نَّدۡخُلَهَآ أَبَدٗا مَّا دَامُواْ فِيهَا فَٱذۡهَبۡ أَنتَ وَرَبُّكَ فَقَٰتِلَآ إِنَّا هَٰهُنَا قَٰعِدُونَ

Suka ce; “Ya kai Musa, lalle mu fa ba za mu tava shigar ta ba har abada, matuqar suna cikinta; sai ka je kai da Ubangijinka ku yi yaqin, lalle mu kam muna nan a zaune.”



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 25

قَالَ رَبِّ إِنِّي لَآ أَمۡلِكُ إِلَّا نَفۡسِي وَأَخِيۖ فَٱفۡرُقۡ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡفَٰسِقِينَ

Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni ban mallaki kowa ba sai kaina da xan’uwana; don haka Ka yi hukunci tsakaninmu da mutanen da suke fasiqai.”



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 26

قَالَ فَإِنَّهَا مُحَرَّمَةٌ عَلَيۡهِمۡۛ أَرۡبَعِينَ سَنَةٗۛ يَتِيهُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ فَلَا تَأۡسَ عَلَى ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡفَٰسِقِينَ

Ya ce: “To lalle an haramta musu (shigarta) har tsawon shekara arba’in. Za su yi ta ximuwa a bayan qasa. Don haka kada ka yi baqin ciki a kan mutanen da suke fasiqai.”



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 32

مِنۡ أَجۡلِ ذَٰلِكَ كَتَبۡنَا عَلَىٰ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ أَنَّهُۥ مَن قَتَلَ نَفۡسَۢا بِغَيۡرِ نَفۡسٍ أَوۡ فَسَادٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَكَأَنَّمَا قَتَلَ ٱلنَّاسَ جَمِيعٗا وَمَنۡ أَحۡيَاهَا فَكَأَنَّمَآ أَحۡيَا ٱلنَّاسَ جَمِيعٗاۚ وَلَقَدۡ جَآءَتۡهُمۡ رُسُلُنَا بِٱلۡبَيِّنَٰتِ ثُمَّ إِنَّ كَثِيرٗا مِّنۡهُم بَعۡدَ ذَٰلِكَ فِي ٱلۡأَرۡضِ لَمُسۡرِفُونَ

Saboda wannan ne muka wajabta wa Banu-Isra’ila cewa, duk wanda ya kashe wani rai ba tare da (laifin kisan) kai ba, ko kuma wata varna a bayan qasa, to kamar ya kashe mutane ne gaba xaya, wanda kuwa ya raya shi, to kamar ya raya mutane ne gaba xaya. Kuma lalle haqiqa manzanninmu sun zo musu da (hujjoji) mabayyana, amma sai ga shi da yawa daga cikinsu bayan hakan, lalle masu varna ne a bayan qasa



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 70

لَقَدۡ أَخَذۡنَا مِيثَٰقَ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ وَأَرۡسَلۡنَآ إِلَيۡهِمۡ رُسُلٗاۖ كُلَّمَا جَآءَهُمۡ رَسُولُۢ بِمَا لَا تَهۡوَىٰٓ أَنفُسُهُمۡ فَرِيقٗا كَذَّبُواْ وَفَرِيقٗا يَقۡتُلُونَ

Lalle haqiqa Mun xauki alqawari daga Bani-Isra’ila, kuma Muka aika musu da manzanni. Duk sa’adda wani manzo ya zo musu da abin da zukatansu ba sa so, sai su qaryata waxansu kuma su riqa kashe waxansu



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 71

وَحَسِبُوٓاْ أَلَّا تَكُونَ فِتۡنَةٞ فَعَمُواْ وَصَمُّواْ ثُمَّ تَابَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمۡ ثُمَّ عَمُواْ وَصَمُّواْ كَثِيرٞ مِّنۡهُمۡۚ وَٱللَّهُ بَصِيرُۢ بِمَا يَعۡمَلُونَ

Kuma sun zaci cewa, babu wata fitina da za ta auku, sai suka makance kuma suka kurumce, sannan Allah Ya karvi tubansu, sannan kuma da yawa daga cikinsu suka sake makancewa da kurumcewa. Allah kuma Mai ganin abin da suke aikatawa ne



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 78

لُعِنَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۢ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ عَلَىٰ لِسَانِ دَاوُۥدَ وَعِيسَى ٱبۡنِ مَرۡيَمَۚ ذَٰلِكَ بِمَا عَصَواْ وَّكَانُواْ يَعۡتَدُونَ

An la’anci waxanda suka kafirta daga cikin Bani-Isra’ila a bisa harshen Dawuda da kuma Isa xan Maryamu. Hakan kuwa saboda abin da suka riqa yi ne na savo, kuma sun kasance suna qetare iyaka



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 79

كَانُواْ لَا يَتَنَاهَوۡنَ عَن مُّنكَرٖ فَعَلُوهُۚ لَبِئۡسَ مَا كَانُواْ يَفۡعَلُونَ

Sun kasance ba sa hana junansu wani mummunan aikin da suka yi. Lalle tir da irin abin da suka kasance suna aikatawa



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 80

تَرَىٰ كَثِيرٗا مِّنۡهُمۡ يَتَوَلَّوۡنَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۚ لَبِئۡسَ مَا قَدَّمَتۡ لَهُمۡ أَنفُسُهُمۡ أَن سَخِطَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمۡ وَفِي ٱلۡعَذَابِ هُمۡ خَٰلِدُونَ

Za ka ga yawancinsu suna nuna qauna ga waxanda suka kafirta. Lalle tir da irin abin da kawunansu suka gabatar, don kuwa Allah Ya yi fushi da su, kuma su masu dawwama ne cikin azaba



Sourate: Suratul Ma’ida

Verset : 81

وَلَوۡ كَانُواْ يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلنَّبِيِّ وَمَآ أُنزِلَ إِلَيۡهِ مَا ٱتَّخَذُوهُمۡ أَوۡلِيَآءَ وَلَٰكِنَّ كَثِيرٗا مِّنۡهُمۡ فَٰسِقُونَ

Kuma da sun kasance suna imani da Allah da Annabi da abin da aka saukar masa, da ba su riqe su a matsayin masoya ba, sai dai kuma yawancinsu fasiqai ne