يُولِجُ ٱلَّيۡلَ فِي ٱلنَّهَارِ وَيُولِجُ ٱلنَّهَارَ فِي ٱلَّيۡلِ وَسَخَّرَ ٱلشَّمۡسَ وَٱلۡقَمَرَۖ كُلّٞ يَجۡرِي لِأَجَلٖ مُّسَمّٗىۚ ذَٰلِكُمُ ٱللَّهُ رَبُّكُمۡ لَهُ ٱلۡمُلۡكُۚ وَٱلَّذِينَ تَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ مَا يَمۡلِكُونَ مِن قِطۡمِيرٍ
Yana shigar da dare cikin yini, Yana kuma shigar da yini cikin dare, Ya kuma hore rana da wata kowannensu yana tafiya zuwa ga ajali iyakantacce. (Mai yin wannan kuwa) Shi ne Allah Ubangijinku, mulki (kuwa) nasa ne. Waxanda kuwa kuke bauta wa ba Shi ba, ba su mallaki ko da rigar qwallon dabino ba
۞إِنَّ ٱللَّهَ يُمۡسِكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ أَن تَزُولَاۚ وَلَئِن زَالَتَآ إِنۡ أَمۡسَكَهُمَا مِنۡ أَحَدٖ مِّنۢ بَعۡدِهِۦٓۚ إِنَّهُۥ كَانَ حَلِيمًا غَفُورٗا
Lalle Allah ne Yake riqe da sammai da qasa don kada su ruguje. Lallai kuwa idan da za su ruguje, to ba wani mai riqe su in ba Shi ba. Lalle Shi (Allah) Ya kasance Mai haquri ne, Mai gafara
وَءَايَةٞ لَّهُمُ ٱلَّيۡلُ نَسۡلَخُ مِنۡهُ ٱلنَّهَارَ فَإِذَا هُم مُّظۡلِمُونَ
Dare ma aya ne a gare su, wanda Muka savule yini daga gare shi[1], sai ga su cikin duhu
1- Watau Allah () yana gusar da rana daga dare sai kawai mutane su gan su cikin duhu.
وَٱلشَّمۡسُ تَجۡرِي لِمُسۡتَقَرّٖ لَّهَاۚ ذَٰلِكَ تَقۡدِيرُ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡعَلِيمِ
Rana kuma tana gudu zuwa wurin da aka iyakance mata. Wannan tsari ne na (Allah) Mabuwayi, Masani
وَٱلۡقَمَرَ قَدَّرۡنَٰهُ مَنَازِلَ حَتَّىٰ عَادَ كَٱلۡعُرۡجُونِ ٱلۡقَدِيمِ
Wata kuma Mun qaddara masa masaukai, har ya koma kamar tsohuwar zarbar dabino
لَا ٱلشَّمۡسُ يَنۢبَغِي لَهَآ أَن تُدۡرِكَ ٱلۡقَمَرَ وَلَا ٱلَّيۡلُ سَابِقُ ٱلنَّهَارِۚ وَكُلّٞ فِي فَلَكٖ يَسۡبَحُونَ
Ba zai yiwu rana ta riski wata ba, dare kuma ba zai riga yini ba. Kowanne kuwa yana iyo ne a cikin falaki
إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنۡيَا بِزِينَةٍ ٱلۡكَوَاكِبِ
Lalle Mun qawata sama ta kusa da ado na taurari
وَحِفۡظٗا مِّن كُلِّ شَيۡطَٰنٖ مَّارِدٖ
Da kuma tsaro daga dukkan wani shaixan mai tsaurin kai
لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلۡمَلَإِ ٱلۡأَعۡلَىٰ وَيُقۡذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٖ
Ba kuma za su iya jiyowa ba (daga asirin) mala’iku na sama, sai a yi ta jifan su ta kowane vangare
دُحُورٗاۖ وَلَهُمۡ عَذَابٞ وَاصِبٌ
Don kora; suna kuma da wata azaba dawwamamma
إِلَّا مَنۡ خَطِفَ ٱلۡخَطۡفَةَ فَأَتۡبَعَهُۥ شِهَابٞ ثَاقِبٞ
Sai dai wanda ya yi fautowar jin, to sai wani tauraro mai haske da quna ya biyo shi
خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۖ يُكَوِّرُ ٱلَّيۡلَ عَلَى ٱلنَّهَارِ وَيُكَوِّرُ ٱلنَّهَارَ عَلَى ٱلَّيۡلِۖ وَسَخَّرَ ٱلشَّمۡسَ وَٱلۡقَمَرَۖ كُلّٞ يَجۡرِي لِأَجَلٖ مُّسَمًّىۗ أَلَا هُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡغَفَّـٰرُ
Ya halicci sammai da qasa da gaskiya; Yana naxa dare a kan yini, Ya kuma naxa yini a kan dare; kuma Ya hore rana da wata; kowane yana tafiya zuwa wani lokaci qayyadajje. Ku saurara! Shi ne Mabuwayi, Mai yawan gafara
لَخَلۡقُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ أَكۡبَرُ مِنۡ خَلۡقِ ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ
Tabbas halittar sammai da qasa ta fi girma a kan halittar mutane, sai dai kuma yawancin mutane ba sa sanin (haka)
وَمِنۡ ءَايَٰتِهِ ٱلَّيۡلُ وَٱلنَّهَارُ وَٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُۚ لَا تَسۡجُدُواْ لِلشَّمۡسِ وَلَا لِلۡقَمَرِ وَٱسۡجُدُواْۤ لِلَّهِۤ ٱلَّذِي خَلَقَهُنَّ إِن كُنتُمۡ إِيَّاهُ تَعۡبُدُونَ
Kuma dare da wuni da rana da wata suna daga ayoyinsa. Kada ku yi sujjada ga rana ko ga wata, ku yi sujjada ga Allah Wanda Ya halicce su idan har kun kasance Shi kaxai kuke bauta wa
تَكَادُ ٱلسَّمَٰوَٰتُ يَتَفَطَّرۡنَ مِن فَوۡقِهِنَّۚ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ يُسَبِّحُونَ بِحَمۡدِ رَبِّهِمۡ وَيَسۡتَغۡفِرُونَ لِمَن فِي ٱلۡأَرۡضِۗ أَلَآ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ
Sammai suna neman su tsattsage ta samansu (don girmansa). Mala’iku kuma suna yin tasbihi da yabon Ubangijinsu, suna kuma neman gafara ga waxanda suke cikin qasa. Ku saurara, Lalle Allah Shi ne Mai gafara, Mai rahama
أَفَلَمۡ يَنظُرُوٓاْ إِلَى ٱلسَّمَآءِ فَوۡقَهُمۡ كَيۡفَ بَنَيۡنَٰهَا وَزَيَّنَّـٰهَا وَمَا لَهَا مِن فُرُوجٖ
Yanzu ba sa duban sama da take sama da su (su ga) yadda Muka gina ta, Muka kuma qawata ta, ba ta kuma da wasu tsage-tsage?
وَفِي ٱلسَّمَآءِ رِزۡقُكُمۡ وَمَا تُوعَدُونَ
A cikin sammai kuma akwai arzikinku da kuma abin da aka yi muku alkawarinsa
وَٱلسَّمَآءَ بَنَيۡنَٰهَا بِأَيۡيْدٖ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ
Sama kuma Mun gina ta da qarfi, lalle kuma Mu tabbas Masu yalwatawa ne
۞وَكَم مِّن مَّلَكٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغۡنِي شَفَٰعَتُهُمۡ شَيۡـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ أَن يَأۡذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرۡضَىٰٓ
Mala’iku nawa ne a cikin sammai cetonsu ba ya amfanar da komai sai da izinin Allah ga waxanda Ya ga dama Ya kuma yarda (da shi)?
ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ بِحُسۡبَانٖ
Rana da wata (suna tafiya) a tsare
وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلۡمِيزَانَ
Sama kuma Ya xaga ta, Ya kuma kafa adalci
۞فَلَآ أُقۡسِمُ بِمَوَٰقِعِ ٱلنُّجُومِ
To ina yin rantsuwa da mafaxar taurari
وَإِنَّهُۥ لَقَسَمٞ لَّوۡ تَعۡلَمُونَ عَظِيمٌ
Lalle ita kuwa rantsuwa ce mai girma, da kuna ganewa.[1]
1- Domin taurari da tafiyarsu a sararin sama abu ne mai cike da ayoyi da darussa masu ximbin yawa.
وَلَقَدۡ زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنۡيَا بِمَصَٰبِيحَ وَجَعَلۡنَٰهَا رُجُومٗا لِّلشَّيَٰطِينِۖ وَأَعۡتَدۡنَا لَهُمۡ عَذَابَ ٱلسَّعِيرِ
Kuma haqiqa Mun qawata saman duniya da taurari Muka sanya su kuma ababan jifan shaixanu[1]; Muka kuma tanadar musu azabar (wutar) Sa’ira
1- Watau jifar shaixanu masu qoqarin satar ji su qona su.
أَلَمۡ تَرَوۡاْ كَيۡفَ خَلَقَ ٱللَّهُ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ طِبَاقٗا
“Shin ba kwa ganin yadda Allah Ya halicci sammai bakwai rufi-rufi?
وَجَعَلَ ٱلۡقَمَرَ فِيهِنَّ نُورٗا وَجَعَلَ ٱلشَّمۡسَ سِرَاجٗا
“Ya kuma sanya wata mai haske a cikinsu; rana kuma Ya sanya ta fitila?
وَأَنَّا لَمَسۡنَا ٱلسَّمَآءَ فَوَجَدۡنَٰهَا مُلِئَتۡ حَرَسٗا شَدِيدٗا وَشُهُبٗا
“Kuma lalle mu mun nemi hawa sama, sai muka same ta an cika ta da matsanancin tsaro da taurari (masu jifa da garwashi)
وَأَنَّا كُنَّا نَقۡعُدُ مِنۡهَا مَقَٰعِدَ لِلسَّمۡعِۖ فَمَن يَسۡتَمِعِ ٱلۡأٓنَ يَجِدۡ لَهُۥ شِهَابٗا رَّصَدٗا
“Lalle kuma mun zamanto a da muna hawa wasu wurare nata don yin sauraro[1]; to duk wanda ya nemi yin sauraro a yanzu zai sama wa kansa wani tauraro wanda aka tanada (don jifan sa)
1- Watau a da can lokacin jahiliyya aljannu sun saba hawa sama domin sato bayanan sirri daga tattaunawar mala’iku, suna isar da su ga bokaye a qasa.
ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا
Yanzu ku ne halittarku ta fi tsanani ko kuwa sama wadda Shi ne Ya gina ta?
رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا
Ya xaukaka rufinta Ya kuma daidaita ta[1]
1- Watau ya zama babu wata varaka ko tsagewa ko wani aibi tare da ita.