لَّا تَجۡعَلُواْ دُعَآءَ ٱلرَّسُولِ بَيۡنَكُمۡ كَدُعَآءِ بَعۡضِكُم بَعۡضٗاۚ قَدۡ يَعۡلَمُ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ يَتَسَلَّلُونَ مِنكُمۡ لِوَاذٗاۚ فَلۡيَحۡذَرِ ٱلَّذِينَ يُخَالِفُونَ عَنۡ أَمۡرِهِۦٓ أَن تُصِيبَهُمۡ فِتۡنَةٌ أَوۡ يُصِيبَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٌ
Kada ku mayar da kiran Manzo a tsakaninku kamar kiran junanku ga juna[1]. Haqiqa Allah Yana sane da waxanda suke zare jiki daga cikinku a voye. To lalle waxanda suke sava wa umarninsa su ji tsoron kada wata fitina ta shafe su ko kuma wata azaba mai raxaxi ta same su
1- Watau xayansu ya riqa cewa: “Ya Muhammadu” ko “Ya Muhammadu xan Abdullahi” ko “Ya xan Abdullahi”. Sai dai su ce: “Ya Manzon Allah” ko “Ya Annabin Allah”.
أَلَآ إِنَّ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ قَدۡ يَعۡلَمُ مَآ أَنتُمۡ عَلَيۡهِ وَيَوۡمَ يُرۡجَعُونَ إِلَيۡهِ فَيُنَبِّئُهُم بِمَا عَمِلُواْۗ وَٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمُۢ
Ku saurara, lalle abin da yake sammai da qasa na Allah ne; haqiqa Yana sane da abin da ku kuke kansa, da kuma ranar da za a komar da su zuwa gare Shi, sannan Ya ba su labarin abin da suka aikata. Allah Masanin komai ne
تَبَارَكَ ٱلَّذِي نَزَّلَ ٱلۡفُرۡقَانَ عَلَىٰ عَبۡدِهِۦ لِيَكُونَ لِلۡعَٰلَمِينَ نَذِيرًا
(Allah) Wanda Ya saukar wa Bawansa Alqur’ani don ya zamo mai gargaxi ga talikai albarkatunsa sun yawaita
ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَلَمۡ يَتَّخِذۡ وَلَدٗا وَلَمۡ يَكُن لَّهُۥ شَرِيكٞ فِي ٱلۡمُلۡكِ وَخَلَقَ كُلَّ شَيۡءٖ فَقَدَّرَهُۥ تَقۡدِيرٗا
(Shi ne) Wanda mulkin sammai da qasa nasa ne, kuma bai riqi wani xa ba, ba kuma Shi da wani abokin tarayya a cikin mulkin, Ya kuma halicci kowanne abu, sannan Ya ajiye shi a irin gwargwadon da ya dace da shi
وَٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ ءَالِهَةٗ لَّا يَخۡلُقُونَ شَيۡـٔٗا وَهُمۡ يُخۡلَقُونَ وَلَا يَمۡلِكُونَ لِأَنفُسِهِمۡ ضَرّٗا وَلَا نَفۡعٗا وَلَا يَمۡلِكُونَ مَوۡتٗا وَلَا حَيَوٰةٗ وَلَا نُشُورٗا
Kuma suka riqi ababen bauta ba Shi ba, ba sa halittar komai, alhali kuwa su ake halittawa, kuma ba sa mallakar cuta ko amfani ga kawunansu, ba sa kuma mallakar kashewa ko rayawa ko tashi (bayan mutuwa)
وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّآ إِفۡكٌ ٱفۡتَرَىٰهُ وَأَعَانَهُۥ عَلَيۡهِ قَوۡمٌ ءَاخَرُونَۖ فَقَدۡ جَآءُو ظُلۡمٗا وَزُورٗا
Waxanda kuma suka kafirta suka ce: “Wannan (Alqur’ani) ba komai ba ne sai qarya da ya qage ta kuma wasu mutane daban suka taimake shi a kansa.” To haqiqa sun zo da zalunci da kuma qarya
وَقَالُوٓاْ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ ٱكۡتَتَبَهَا فَهِيَ تُمۡلَىٰ عَلَيۡهِ بُكۡرَةٗ وَأَصِيلٗا
Suka kuma ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko ne da ya rubuta su, waxanda ake masa shiftar su safe da yamma.”
قُلۡ أَنزَلَهُ ٱلَّذِي يَعۡلَمُ ٱلسِّرَّ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ إِنَّهُۥ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا
Ka ce (da su): “Wanda Yake sane da asirin sammai da qasa Shi Ya saukar da shi. Lalle Shi Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai.”
وَقَالُواْ مَالِ هَٰذَا ٱلرَّسُولِ يَأۡكُلُ ٱلطَّعَامَ وَيَمۡشِي فِي ٱلۡأَسۡوَاقِ لَوۡلَآ أُنزِلَ إِلَيۡهِ مَلَكٞ فَيَكُونَ مَعَهُۥ نَذِيرًا
Suka kuma ce: “Me ya sa wannan Manzo yake cin abinci kuma yake tafiya cikin kasuwanni? Me ya hana a saukar masa da mala’ika, sai ya zama mai gargaxi tare da shi?
أَوۡ يُلۡقَىٰٓ إِلَيۡهِ كَنزٌ أَوۡ تَكُونُ لَهُۥ جَنَّةٞ يَأۡكُلُ مِنۡهَاۚ وَقَالَ ٱلظَّـٰلِمُونَ إِن تَتَّبِعُونَ إِلَّا رَجُلٗا مَّسۡحُورًا
Ko a jefo masa wata taskar dukiya ko ya zama yana da wani lambu wanda daga gare shi zai riqa ci?” Sai azzalumai suka ce “Ba wanda kuke bi sai wani mutum wanda aka yi wa sihiri!”
ٱنظُرۡ كَيۡفَ ضَرَبُواْ لَكَ ٱلۡأَمۡثَٰلَ فَضَلُّواْ فَلَا يَسۡتَطِيعُونَ سَبِيلٗا
To ka dubi yadda suka riqa buga maka misali[1], sai suka vata, don haka ba za su iya bin hanyar shiriya ba
1- Watau wani lokaci su ce masa mai sihiri, wani lokaci kuma su ce mawaqi, ko su ce boka, ko mai tavin hankali.
تَبَارَكَ ٱلَّذِيٓ إِن شَآءَ جَعَلَ لَكَ خَيۡرٗا مِّن ذَٰلِكَ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ وَيَجۡعَل لَّكَ قُصُورَۢا
Albarkatun (Allah) sun yawaita, wanda idan Ya ga dama sai Ya sanya maka alheri fiye da waxannan: (su ne) gonakai waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, Ya kuma sanya maka maka-makan gidaje
بَلۡ كَذَّبُواْ بِٱلسَّاعَةِۖ وَأَعۡتَدۡنَا لِمَن كَذَّبَ بِٱلسَّاعَةِ سَعِيرًا
Ba haka ba ne, sun dai qaryata tashin alqiyama ne; Mun kuwa tanadi (wutar) Sa’ira ga wanda ya qaryata tashin alqiyama
إِذَا رَأَتۡهُم مِّن مَّكَانِۭ بَعِيدٖ سَمِعُواْ لَهَا تَغَيُّظٗا وَزَفِيرٗا
Idan (wutar) ta hango su daga wuri mai nisa sai su ji tafarfasa da gurnaninta
وَإِذَآ أُلۡقُواْ مِنۡهَا مَكَانٗا ضَيِّقٗا مُّقَرَّنِينَ دَعَوۡاْ هُنَالِكَ ثُبُورٗا
Idan kuwa aka jefa su cikinta a wani wuri quntatacce nata, suna ququnce, sai su riqa kiran hallaka a can
لَّا تَدۡعُواْ ٱلۡيَوۡمَ ثُبُورٗا وَٰحِدٗا وَٱدۡعُواْ ثُبُورٗا كَثِيرٗا
(Sai a ce da su): “A yau kada ku kirawo hallaka xaya kawai, ku kirawo hallaka da yawa!”
قُلۡ أَذَٰلِكَ خَيۡرٌ أَمۡ جَنَّةُ ٱلۡخُلۡدِ ٱلَّتِي وُعِدَ ٱلۡمُتَّقُونَۚ كَانَتۡ لَهُمۡ جَزَآءٗ وَمَصِيرٗا
Ka ce (da su): “Yanzu wannan ne ya fi alheri, ko kuwa Aljannar dawwama wadda aka yi wa masu taqawa alqawarinta, ta zama sakamako da makoma a gare su?”
لَّهُمۡ فِيهَا مَا يَشَآءُونَ خَٰلِدِينَۚ كَانَ عَلَىٰ رَبِّكَ وَعۡدٗا مَّسۡـُٔولٗا
Suna da duk abin da suka ga dama a cikinta, masu dawwama ne. (Wannan kuma) ya kasance alqawari ne abin tambaya a kan Ubangijnka
وَيَوۡمَ يَحۡشُرُهُمۡ وَمَا يَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ فَيَقُولُ ءَأَنتُمۡ أَضۡلَلۡتُمۡ عِبَادِي هَـٰٓؤُلَآءِ أَمۡ هُمۡ ضَلُّواْ ٱلسَّبِيلَ
(Ka tuna) kuma ranar da zai tara su da abin da suke bauta wa ba Allah ba, sai Ya ce (da su): “Shin yanzu ku ne kuka vatar da bayina waxannan, ko kuwa su ne suka vace wa hanya don kansu?”
قَالُواْ سُبۡحَٰنَكَ مَا كَانَ يَنۢبَغِي لَنَآ أَن نَّتَّخِذَ مِن دُونِكَ مِنۡ أَوۡلِيَآءَ وَلَٰكِن مَّتَّعۡتَهُمۡ وَءَابَآءَهُمۡ حَتَّىٰ نَسُواْ ٱلذِّكۡرَ وَكَانُواْ قَوۡمَۢا بُورٗا
Suka ce: “Tsarki ya tabbata gare Ka, bai zamanto ya dace da mu ba mu riqi wasu majivinta ba Kai ba, sai dai kuma Ka jiyar da su daxi ne tare da iyayensu har suka manta tuna Ka, suka kuwa kasance mutane hallakakku.”
فَقَدۡ كَذَّبُوكُم بِمَا تَقُولُونَ فَمَا تَسۡتَطِيعُونَ صَرۡفٗا وَلَا نَصۡرٗاۚ وَمَن يَظۡلِم مِّنكُمۡ نُذِقۡهُ عَذَابٗا كَبِيرٗا
To haqiqa sun qaryata ku game da abin da kuke faxa, to ba za ku samu wata makauta ba, ko kuma wani taimako. Duk wanda kuma ya yi zalunci daga cikinku za Mu xanxana masa azaba mai girma
وَمَآ أَرۡسَلۡنَا قَبۡلَكَ مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ إِلَّآ إِنَّهُمۡ لَيَأۡكُلُونَ ٱلطَّعَامَ وَيَمۡشُونَ فِي ٱلۡأَسۡوَاقِۗ وَجَعَلۡنَا بَعۡضَكُمۡ لِبَعۡضٖ فِتۡنَةً أَتَصۡبِرُونَۗ وَكَانَ رَبُّكَ بَصِيرٗا
Kuma ba Mu aiko manzanni ba gabaninka sai cewa lalle suna cin abinci kuma suna tafiya cikin kasuwanni. Mun kuwa sanya wasunku su zama fitina ga wasu. Shin za ku yi haquri? Ubangijinka kuwa Ya kasance Mai gani ne