Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 283

۞وَإِن كُنتُمۡ عَلَىٰ سَفَرٖ وَلَمۡ تَجِدُواْ كَاتِبٗا فَرِهَٰنٞ مَّقۡبُوضَةٞۖ فَإِنۡ أَمِنَ بَعۡضُكُم بَعۡضٗا فَلۡيُؤَدِّ ٱلَّذِي ٱؤۡتُمِنَ أَمَٰنَتَهُۥ وَلۡيَتَّقِ ٱللَّهَ رَبَّهُۥۗ وَلَا تَكۡتُمُواْ ٱلشَّهَٰدَةَۚ وَمَن يَكۡتُمۡهَا فَإِنَّهُۥٓ ءَاثِمٞ قَلۡبُهُۥۗ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ عَلِيمٞ

Kuma idan kun kasance a halin tafiya, kuma ba ku sami marubuci ba, to sai a ba da jingina da za a karva, kuma idan sashinku ya amince wa sashi, to shi wanda aka amincewan ya bayar da amanarsa, kuma ya kiyayi Allah Ubangijinsa. Kuma kada ku voye shaida; duk wanda ya voye ta kuwa, to lalle shi zuciyarsa a cike take da savo. Kuma Allah Masanin abin da kuke aikatawa ne



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 284

لِّلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۗ وَإِن تُبۡدُواْ مَا فِيٓ أَنفُسِكُمۡ أَوۡ تُخۡفُوهُ يُحَاسِبۡكُم بِهِ ٱللَّهُۖ فَيَغۡفِرُ لِمَن يَشَآءُ وَيُعَذِّبُ مَن يَشَآءُۗ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ

Duk abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa na Allah ne. Kuma in har kuka bayyana abin da yake cikin zukatanku ko kuka voye shi, Allah zai yi muku hisabi a kansa, sai Ya yi gafara ga wanda Ya ga dama, Ya kuma yi azaba ga wanda Ya ga dama. Kuma Allah Mai iko ne a kan komai



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 285

ءَامَنَ ٱلرَّسُولُ بِمَآ أُنزِلَ إِلَيۡهِ مِن رَّبِّهِۦ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَۚ كُلٌّ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَمَلَـٰٓئِكَتِهِۦ وَكُتُبِهِۦ وَرُسُلِهِۦ لَا نُفَرِّقُ بَيۡنَ أَحَدٖ مِّن رُّسُلِهِۦۚ وَقَالُواْ سَمِعۡنَا وَأَطَعۡنَاۖ غُفۡرَانَكَ رَبَّنَا وَإِلَيۡكَ ٱلۡمَصِيرُ

Manzon ya yi imani da abin da aka saukar masa daga Ubangijinsa, muminai ma haka, kowanne ya yi imani da Allah da mala’ikunsa da littattafansa da manzanninsa, (suna cewa) : “Ba ma nuna bambanci tsakanin xaya daga cikin manzanninsa.” Kuma suka ce: “Mun ji kuma mun bi ; muna neman gafararka ya Ubangijinmu, kuma zuwa gare Ka ne makoma take



Capítulo: Suratul Baqara

Verso : 286

لَا يُكَلِّفُ ٱللَّهُ نَفۡسًا إِلَّا وُسۡعَهَاۚ لَهَا مَا كَسَبَتۡ وَعَلَيۡهَا مَا ٱكۡتَسَبَتۡۗ رَبَّنَا لَا تُؤَاخِذۡنَآ إِن نَّسِينَآ أَوۡ أَخۡطَأۡنَاۚ رَبَّنَا وَلَا تَحۡمِلۡ عَلَيۡنَآ إِصۡرٗا كَمَا حَمَلۡتَهُۥ عَلَى ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِنَاۚ رَبَّنَا وَلَا تُحَمِّلۡنَا مَا لَا طَاقَةَ لَنَا بِهِۦۖ وَٱعۡفُ عَنَّا وَٱغۡفِرۡ لَنَا وَٱرۡحَمۡنَآۚ أَنتَ مَوۡلَىٰنَا فَٱنصُرۡنَا عَلَى ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Allah ba Ya kallafa wa rai sai abin da zai iya. Abin da ya aikata (na alheri) nasa ne, hakanan sakamakon abin da ya aikata (na sharri) shi ma nasa ne. Ya Ubangijinmu, kada Ka riqe mu da laifi idan mun yi mantuwa ko mun yi kuskure. Ya Ubangijinmu, kada kuma Ka xora mana wani nauyi irin wanda ka xora wa waxanda suke gabaninmu. Ya Ubangijinmu, kada kuma Ka xora mana abin da ba mu da iko a kansa, kuma Ka yi mana afuwa, kuma Ka yi mana gafara, kuma Ka ji qan mu; Kai ne Majivincin lamarinmu, don haka Ka taimake mu a kan mutane kafirai



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 1

الٓمٓ

ALIF LAAM MIIM[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 2

ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ ٱلۡحَيُّ ٱلۡقَيُّومُ

Allah, babu wani abin bautawa da gaskiya sai Shi, Shi Rayayye ne, Tsayayye da Zatinsa



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 3

نَزَّلَ عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ مُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِ وَأَنزَلَ ٱلتَّوۡرَىٰةَ وَٱلۡإِنجِيلَ

Ya saukar maka da Littafi da gaskiya, yana mai gaskata abin da ya gabace shi, kuma Ya saukar da Attaura da Linjila



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 4

مِن قَبۡلُ هُدٗى لِّلنَّاسِ وَأَنزَلَ ٱلۡفُرۡقَانَۗ إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ لَهُمۡ عَذَابٞ شَدِيدٞۗ وَٱللَّهُ عَزِيزٞ ذُو ٱنتِقَامٍ

Tun kafin (Alqur’ani), (don su zama) shiriya ga mutane, kuma Ya saukar da mai rarrabewa (tsakanin qarya da gaskiya). Lalle waxanda suka kafirce wa ayoyin Allah, suna da azaba mai tsanani, kuma Allah Mabuwayi ne, Ma’abocin xaukar fansa



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 5

إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَخۡفَىٰ عَلَيۡهِ شَيۡءٞ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا فِي ٱلسَّمَآءِ

Lalle Allah babu abin da yake voyuwa a gare Shi a qasa ko a sama



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 6

هُوَ ٱلَّذِي يُصَوِّرُكُمۡ فِي ٱلۡأَرۡحَامِ كَيۡفَ يَشَآءُۚ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Shi ne wanda Yake suranta ku a cikin mahaifu irin yadda Ya ga dama, babu abin bauta wa da gaskiya sai Shi, Shi ne Mabuwayi, Mai hikima



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 7

هُوَ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ مِنۡهُ ءَايَٰتٞ مُّحۡكَمَٰتٌ هُنَّ أُمُّ ٱلۡكِتَٰبِ وَأُخَرُ مُتَشَٰبِهَٰتٞۖ فَأَمَّا ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِمۡ زَيۡغٞ فَيَتَّبِعُونَ مَا تَشَٰبَهَ مِنۡهُ ٱبۡتِغَآءَ ٱلۡفِتۡنَةِ وَٱبۡتِغَآءَ تَأۡوِيلِهِۦۖ وَمَا يَعۡلَمُ تَأۡوِيلَهُۥٓ إِلَّا ٱللَّهُۗ وَٱلرَّـٰسِخُونَ فِي ٱلۡعِلۡمِ يَقُولُونَ ءَامَنَّا بِهِۦ كُلّٞ مِّنۡ عِندِ رَبِّنَاۗ وَمَا يَذَّكَّرُ إِلَّآ أُوْلُواْ ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Shi ne Wanda ya saukar maka da Littafi, a cikinsa akwai ayoyi masu bayyanannun hukunce-hukunce, su ne asalin Littafin, akwai kuma waxansu masu rikitarwa[1]; to amma waxanda suke da karkata a zukatansu sai su riqa bin abin da yake rikitarwar a cikinsu don neman fitina da kuma neman sanin haqiqanin fassararsa. Kuma babu wanda ya san haqiqanin fassararsa sai Allah. Kuma masu zurfi cikin ilimi suna cewa: “Mun yi imani da shi, dukkaninsa daga wurin Ubangijinmu yake.” Kuma ba mai wa’azantuwa sai masu hankali


1- Ayoyi masu rikitarwa, su ne waxanda ma’anoninsu ba su fito fili ba.


Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 8

رَبَّنَا لَا تُزِغۡ قُلُوبَنَا بَعۡدَ إِذۡ هَدَيۡتَنَا وَهَبۡ لَنَا مِن لَّدُنكَ رَحۡمَةًۚ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡوَهَّابُ

“Ya Ubangijinmu, kada Ka karkatar da zukatanmu bayan Ka shiryar da mu, kuma Ka yi mana rahama daga gare Ka. Lalle kai Mai yawan baiwa ne.”



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 9

رَبَّنَآ إِنَّكَ جَامِعُ ٱلنَّاسِ لِيَوۡمٖ لَّا رَيۡبَ فِيهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُخۡلِفُ ٱلۡمِيعَادَ

“Ya Ubangijinmu, lalle Kai ne Mai tattara mutane a yinin da babu kokwanto a cikinsa. Lalle Allah ba Ya sava alqawari.”



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَن تُغۡنِيَ عَنۡهُمۡ أَمۡوَٰلُهُمۡ وَلَآ أَوۡلَٰدُهُم مِّنَ ٱللَّهِ شَيۡـٔٗاۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ وَقُودُ ٱلنَّارِ

Lalle waxanda suka kafirta, dukiyoyinsu da ‘ya’yansu ba za su wadatar da su da komai ba a wajen Allah; kuma waxannan su makamashi ne na wuta



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 11

كَدَأۡبِ ءَالِ فِرۡعَوۡنَ وَٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۚ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا فَأَخَذَهُمُ ٱللَّهُ بِذُنُوبِهِمۡۗ وَٱللَّهُ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Kamar dai halin abin da ya gudana ga mutanen Fir’auna da waxanda suka gabace su. Sun qaryata ayoyinmu, sai Allah Ya kama su da zunubansu, kuma Allah Mai tsananin uquba ne



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 12

قُل لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ سَتُغۡلَبُونَ وَتُحۡشَرُونَ إِلَىٰ جَهَنَّمَۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمِهَادُ

Ka ce wa waxanda suka kafirta: “Da sannu za a rinjaye ku, kuma za a tara ku zuwa Jahannama. Kuma tir da wannan mashimfixi



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 13

قَدۡ كَانَ لَكُمۡ ءَايَةٞ فِي فِئَتَيۡنِ ٱلۡتَقَتَاۖ فِئَةٞ تُقَٰتِلُ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَأُخۡرَىٰ كَافِرَةٞ يَرَوۡنَهُم مِّثۡلَيۡهِمۡ رَأۡيَ ٱلۡعَيۡنِۚ وَٱللَّهُ يُؤَيِّدُ بِنَصۡرِهِۦ مَن يَشَآءُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةٗ لِّأُوْلِي ٱلۡأَبۡصَٰرِ

Haqiqa wata izina ta bayyana a gare ku game da wasu rundunoni biyu da suka gwabza, xaya rundunar tana yaqi saboda Allah, xayar kuma kafira ce, suna kallon su (kafiran) kamar ninki biyu a ganin ido[1]; kuma Allah Yana qarfafar wanda Ya ga dama da nasararsa. Lalle a cikin hakan akwai izina ga ma’abota basira


1- Qungiyar farko su ne Annabi () da sahabbai a lokacin yaqin Badar, suna ganin qungiya ta biyu wato kafirai, sun ninka su gida biyu. Wannan kuwa ya qara musu dogaro ga Allah.


Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 14

زُيِّنَ لِلنَّاسِ حُبُّ ٱلشَّهَوَٰتِ مِنَ ٱلنِّسَآءِ وَٱلۡبَنِينَ وَٱلۡقَنَٰطِيرِ ٱلۡمُقَنطَرَةِ مِنَ ٱلذَّهَبِ وَٱلۡفِضَّةِ وَٱلۡخَيۡلِ ٱلۡمُسَوَّمَةِ وَٱلۡأَنۡعَٰمِ وَٱلۡحَرۡثِۗ ذَٰلِكَ مَتَٰعُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ وَٱللَّهُ عِندَهُۥ حُسۡنُ ٱلۡمَـَٔابِ

An qawata wa mutane son sha’awace-sha’awace na mata da ‘ya’ya da dukiya mai yawa abar tarawa ta zinariya da azurfa da kuma kiwatattun dawaki da dabbobi na gida da amfanin gona. Waxannan duk morewa ce ta rayuwar duniya; Allah kuwa a wurinsa ne kyakkyawar makoma take



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 15

۞قُلۡ أَؤُنَبِّئُكُم بِخَيۡرٖ مِّن ذَٰلِكُمۡۖ لِلَّذِينَ ٱتَّقَوۡاْ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَا وَأَزۡوَٰجٞ مُّطَهَّرَةٞ وَرِضۡوَٰنٞ مِّنَ ٱللَّهِۗ وَٱللَّهُ بَصِيرُۢ بِٱلۡعِبَادِ

Ka ce: “Shin in ba ku labarin da abin da ya fi waxancan alheri? Waxanda suka yi taqawa, suna da wasu gidajen aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, a wurin Ubangijinsu, suna masu zama a cikinsu dindindin da mata na aure tsarkaka da kuma yarda daga Allah. Kuma Allah Mai ganin bayinsa ne.”



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 16

ٱلَّذِينَ يَقُولُونَ رَبَّنَآ إِنَّنَآ ءَامَنَّا فَٱغۡفِرۡ لَنَا ذُنُوبَنَا وَقِنَا عَذَابَ ٱلنَّارِ

(Su ne) waxanda suke cewa: “Ya Ubangijinmu, lalle mu mun yi imani, don haka Ka gafarta mana zunubanmu, kuma Ka tserar da mu daga azabar wuta.”



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 17

ٱلصَّـٰبِرِينَ وَٱلصَّـٰدِقِينَ وَٱلۡقَٰنِتِينَ وَٱلۡمُنفِقِينَ وَٱلۡمُسۡتَغۡفِرِينَ بِٱلۡأَسۡحَارِ

(Su ne) masu haquri, masu gaskiya, kuma masu xa’a, kuma masu ciyarwa, kuma masu neman gafara a qarshen dare



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 18

شَهِدَ ٱللَّهُ أَنَّهُۥ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَأُوْلُواْ ٱلۡعِلۡمِ قَآئِمَۢا بِٱلۡقِسۡطِۚ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Allah Ya shaida cewa, babu abin bauta wa da gaskiya sai Shi, haka mala’iku ma da ma’abota ilimi, Tsayayye ne da adalci. Babu abin bauta wa da gaskiya sai Shi, Mabuwayi, Mai hikima



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 19

إِنَّ ٱلدِّينَ عِندَ ٱللَّهِ ٱلۡإِسۡلَٰمُۗ وَمَا ٱخۡتَلَفَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَهُمُ ٱلۡعِلۡمُ بَغۡيَۢا بَيۡنَهُمۡۗ وَمَن يَكۡفُرۡ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ فَإِنَّ ٱللَّهَ سَرِيعُ ٱلۡحِسَابِ

Lalle addini a wurin Allah shi ne Musulunci. Kuma waxanda aka ba wa Littafi ba su yi savani ba sai bayan da ilimi ya zo musu saboda zalunci a tsakaninsu. Wanda kuwa duk ya kafirce wa ayoyin Allah, to lalle Allah Mai gaggawar hisabi ne



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 20

فَإِنۡ حَآجُّوكَ فَقُلۡ أَسۡلَمۡتُ وَجۡهِيَ لِلَّهِ وَمَنِ ٱتَّبَعَنِۗ وَقُل لِّلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡأُمِّيِّـۧنَ ءَأَسۡلَمۡتُمۡۚ فَإِنۡ أَسۡلَمُواْ فَقَدِ ٱهۡتَدَواْۖ وَّإِن تَوَلَّوۡاْ فَإِنَّمَا عَلَيۡكَ ٱلۡبَلَٰغُۗ وَٱللَّهُ بَصِيرُۢ بِٱلۡعِبَادِ

To idan sun yi jayayya da kai, sai ka ce: “Ni na miqa wuyana ne ga Allah, haka ma wanda ya bi ni.” Kuma ka faxa wa waxanda aka bai wa Littafi da Ummiyyai (Larabawa): “Shin kun miqa wuya?” To idan sun miqa wuya, haqiqa sun shiryu; idan kuwa suka juya baya, to babu abin da yake a kanka sai isar da saqo. Kuma Allah Mai ganin bayinsa ne



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 21

إِنَّ ٱلَّذِينَ يَكۡفُرُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَيَقۡتُلُونَ ٱلنَّبِيِّـۧنَ بِغَيۡرِ حَقّٖ وَيَقۡتُلُونَ ٱلَّذِينَ يَأۡمُرُونَ بِٱلۡقِسۡطِ مِنَ ٱلنَّاسِ فَبَشِّرۡهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ

Lalle waxanda suke kafirce wa ayoyin Allah, kuma suke kashe annabawa ba tare da wani haqqi ba, kuma suke kashe waxanda suke yin umarni da adalci cikin mutane, to ka yi musu albishir da wata azaba mai raxaxi



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 22

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ حَبِطَتۡ أَعۡمَٰلُهُمۡ فِي ٱلدُّنۡيَا وَٱلۡأٓخِرَةِ وَمَا لَهُم مِّن نَّـٰصِرِينَ

Waxannan su ne waxanda ayyukansu suka lalace a duniya da lahira, kuma ba su da wasu mataimaka



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 23

أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلَّذِينَ أُوتُواْ نَصِيبٗا مِّنَ ٱلۡكِتَٰبِ يُدۡعَوۡنَ إِلَىٰ كِتَٰبِ ٱللَّهِ لِيَحۡكُمَ بَيۡنَهُمۡ ثُمَّ يَتَوَلَّىٰ فَرِيقٞ مِّنۡهُمۡ وَهُم مُّعۡرِضُونَ

Shin ba ka ga waxannan da aka ba su wani kaso na ilimin Littafi ba, ana kiran su zuwa ga Littafin Allah don Ya yi hukunci a tsakaninsu, sannan sai wani vangare daga cikinsu suna juya baya, suna masu bijirewa



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 24

ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ قَالُواْ لَن تَمَسَّنَا ٱلنَّارُ إِلَّآ أَيَّامٗا مَّعۡدُودَٰتٖۖ وَغَرَّهُمۡ فِي دِينِهِم مَّا كَانُواْ يَفۡتَرُونَ

Wannan kuwa saboda su sun ce: “Wuta ba za ta shafe mu ba sai a waxansu ‘yan kwanaki qididdigaggu.” kuma abin da suka kasance suna qirqira a addininsu shi ne ya ruxe su



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 25

فَكَيۡفَ إِذَا جَمَعۡنَٰهُمۡ لِيَوۡمٖ لَّا رَيۡبَ فِيهِ وَوُفِّيَتۡ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا كَسَبَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

To yaya halinsu zai kasance idan Muka tara su a wani yini da babu shakka game da shi, kuma kowane rai za a saka masa da abin da ya aikata, kuma su ba za a zalunce su ba?



Capítulo: Suratu Ali-Imran

Verso : 26

قُلِ ٱللَّهُمَّ مَٰلِكَ ٱلۡمُلۡكِ تُؤۡتِي ٱلۡمُلۡكَ مَن تَشَآءُ وَتَنزِعُ ٱلۡمُلۡكَ مِمَّن تَشَآءُ وَتُعِزُّ مَن تَشَآءُ وَتُذِلُّ مَن تَشَآءُۖ بِيَدِكَ ٱلۡخَيۡرُۖ إِنَّكَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Ka ce: “Ya Allah, Kai ne Mamallakin mulki, Kana bayar da mulki ga wanda Ka ga dama, kuma Kana qwace mulki daga wanda Ka ga dama, kuma Kana xaukaka wanda Ka ga dama, kuma Kana qasqantar da wanda Ka ga dama; duk alheri yana hannuka, lalle Kai Mai iko ne a kan komai