Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 7

وَإِنَّهُۥ عَلَىٰ ذَٰلِكَ لَشَهِيدٞ

Lalle kuma shi shaida ne a kan haka



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 8

وَإِنَّهُۥ لِحُبِّ ٱلۡخَيۡرِ لَشَدِيدٌ

Lalle shi kuma mai tsananin son alheri ne[1]


1- Watau yana da tsananin son dukiya, wannan ne kuma yake sanya shi rowa.


Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 9

۞أَفَلَا يَعۡلَمُ إِذَا بُعۡثِرَ مَا فِي ٱلۡقُبُورِ

Shin bai sani ba ne idan aka bankaxo abubuwan da suke cikin qaburbura?



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 10

وَحُصِّلَ مَا فِي ٱلصُّدُورِ

Aka kuma tattaro abubuwan da suke cikin qiraza?



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 11

إِنَّ رَبَّهُم بِهِمۡ يَوۡمَئِذٖ لَّخَبِيرُۢ

Lalle a wannan ranar tabbas Ubangijinsu Masani ne game da su



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 1

ٱلۡقَارِعَةُ

Mai qwanqwasa (zukata da tsoro)



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 2

مَا ٱلۡقَارِعَةُ

Mece ce mai qwanqwsa (zukata da tsoro)?



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 3

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡقَارِعَةُ

Kuma me ya sanar da kai mece ce mai qwanqwasa (zukata da tsoro)?



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 4

يَوۡمَ يَكُونُ ٱلنَّاسُ كَٱلۡفَرَاشِ ٱلۡمَبۡثُوثِ

(Ita ce) ranar da mutane za su zama kamar xangon fari masu bazuwa



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 5

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ ٱلۡمَنفُوشِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga[1]


1- Watau saboda rashin nauyinsu da warwatsuwarsu a cikin sararin sama.


Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 6

فَأَمَّا مَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ

To amma wanda ma’aunan ayyukansa suka yi nauyi



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 7

فَهُوَ فِي عِيشَةٖ رَّاضِيَةٖ

To shi kam yana cikin rayuwa mai gamsarwa



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 8

وَأَمَّا مَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ

Amma kuma duk wanda ma’aunan ayyukansa suka yi shafal



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 9

فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٞ

To shi makomarsa (wutar) Hawiya ce



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 10

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا هِيَهۡ

Kuma me ya sanar da kai mece ce ita?



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 11

نَارٌ حَامِيَةُۢ

Wuta ce mai tsananin zafi



Capítulo: Suratut Takasur

Verso : 1

أَلۡهَىٰكُمُ ٱلتَّكَاثُرُ

Alfahari da yawan (‘ya’ya da dukiya) ya shagaltar da ku[1]


1- Watau su xauke musu hankali har su kai ga barin xa’ar Allah.


Capítulo: Suratut Takasur

Verso : 2

حَتَّىٰ زُرۡتُمُ ٱلۡمَقَابِرَ

Har kuka (mutu kuka) ziyarci qaburbura



Capítulo: Suratut Takasur

Verso : 3

كَلَّا سَوۡفَ تَعۡلَمُونَ

A’aha! (haka bai kamace ku ba) da sannu za ku sani



Capítulo: Suratut Takasur

Verso : 4

ثُمَّ كَلَّا سَوۡفَ تَعۡلَمُونَ

Sannan a’aha, da sannu za ku sani



Capítulo: Suratut Takasur

Verso : 5

كَلَّا لَوۡ تَعۡلَمُونَ عِلۡمَ ٱلۡيَقِينِ

Tabbas da za ku yi sani, sani na sakankancewa[1]


1- Watau wanda babu kokwanto ko kaxan a cikinsa.


Capítulo: Suratut Takasur

Verso : 6

لَتَرَوُنَّ ٱلۡجَحِيمَ

Tabbas haqiqa za ku ga wutar Jahimu



Capítulo: Suratut Takasur

Verso : 7

ثُمَّ لَتَرَوُنَّهَا عَيۡنَ ٱلۡيَقِينِ

Sannan tabbas haqiqa za ku gan ta gani da ido na sakankancewa



Capítulo: Suratut Takasur

Verso : 8

ثُمَّ لَتُسۡـَٔلُنَّ يَوۡمَئِذٍ عَنِ ٱلنَّعِيمِ

Sannan kuma tabbas lalle za a tambaye ku a wannan ranar game da ni’imomin (da kuka mora a duniya)



Capítulo: Suratul Asr

Verso : 1

وَٱلۡعَصۡرِ

Na rantse da zamani[1]


1- Wannan ya qunshi dare da rana waxanda su ne mahallin dukkan ayyukan bayi.


Capítulo: Suratul Asr

Verso : 2

إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَفِي خُسۡرٍ

Lalle mutum yana cikin asara



Capítulo: Suratul Asr

Verso : 3

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡحَقِّ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ

Sai dai waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, suka kuma yi wa juna wasiyya da gaskiya, suka kuma yi wa juna wasiyya da haquri



Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 1

وَيۡلٞ لِّكُلِّ هُمَزَةٖ لُّمَزَةٍ

Tsananin azaba ya tabbata ga duk wani mai yawan qyafice mai yawan suka[1]


1- Watau yawan qyafice ga mutane, yana kuma yawan sukan su da aibata su a bayan idanuwansu..


Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 2

ٱلَّذِي جَمَعَ مَالٗا وَعَدَّدَهُۥ

Wanda ya tara dukiya ya qididdige ta



Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 3

يَحۡسَبُ أَنَّ مَالَهُۥٓ أَخۡلَدَهُۥ

Yana zaton cewa dukiyarsa za ta dawwamar da shi