Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 3

ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ

Wanda ya nauyayi bayanka?



Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 4

وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ

Muka kuma xaukaka maka ambatonka[1]?


1- Watau kamar ambatonsa a cikin kiran salla da iqama da tahiya da sauransu.


Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 5

فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا

To lalle tsanani yana tare da sauqi



Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 6

إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا

Lalle tsananin yana tare da sauqi



Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 7

فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ

Saboda haka idan ka gama (harkokinka) sai ka kafu (wajen bautar Allah)



Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 8

وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب

Sannan kuma ka yi kwaxayi wajen Ubangijinka kawai



Capítulo: Suratut Tin

Verso : 1

وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيۡتُونِ

Na rantse da vaure da zaitun[1]


1- Watau wuraren tsirowarsu, watau Sham, ko kuma su kansu waxanan bishiyoyin.


Capítulo: Suratut Tin

Verso : 2

وَطُورِ سِينِينَ

Da (dutsen) Xuri Sinina



Capítulo: Suratut Tin

Verso : 3

وَهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ٱلۡأَمِينِ

Da wannan garin amintacce (watau Makka)



Capítulo: Suratut Tin

Verso : 4

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِيٓ أَحۡسَنِ تَقۡوِيمٖ

Haqiqa Mun halicci mutum a kan mafi kyan diri



Capítulo: Suratut Tin

Verso : 5

ثُمَّ رَدَدۡنَٰهُ أَسۡفَلَ سَٰفِلِينَ

Sannan Muka mayar da shi mafi qasqancin qasqantattu[1]


1- Watau ya mayar da shi tsoho tukuf a duniya, ko kuma a lahira ya zamanto xan wuta.


Capítulo: Suratut Tin

Verso : 6

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ

Sai fa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, to su kam suna da lada ba mai yankewa ba



Capítulo: Suratut Tin

Verso : 7

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعۡدُ بِٱلدِّينِ

To (kai kafiri) me ya sa kake qaryata ranar sakamako bayan haka?



Capítulo: Suratut Tin

Verso : 8

أَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَحۡكَمِ ٱلۡحَٰكِمِينَ

Ashe Allah ba Shi ne Mafi iya hukuncin masu hukunci ba?



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 1

ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 2

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِنۡ عَلَقٍ

Ya halicci mutum daga gudan jini[1]


1- Watau bayan yana xigon maniyyi.


Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 3

ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ

Ka yi karatu alhali Ubangijinka Shi ne mafi karamci



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 4

ٱلَّذِي عَلَّمَ بِٱلۡقَلَمِ

Wanda Ya koyar ta (hanyar) alqalami



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 5

عَلَّمَ ٱلۡإِنسَٰنَ مَا لَمۡ يَعۡلَمۡ

Ya koyar da mutum abin da bai sani ba



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 6

كَلَّآ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَيَطۡغَىٰٓ

Tabbas! Lalle (jinsin) mutum haqiqa yana yin xagawa



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 7

أَن رَّءَاهُ ٱسۡتَغۡنَىٰٓ

Don ya ga kansa yana cikin wadata



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 8

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجۡعَىٰٓ

Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makomar (taka) take



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 9

أَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي يَنۡهَىٰ

Ka ba ni labarin wanda yake hana



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 10

عَبۡدًا إِذَا صَلَّىٰٓ

Bawa yayin da ya yi salla



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 11

أَرَءَيۡتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلۡهُدَىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi Bawan) ya kasance a kan shiriya



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 12

أَوۡ أَمَرَ بِٱلتَّقۡوَىٰٓ

Ko kuma ya yi umarni da taqawa



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 13

أَرَءَيۡتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi mai hanawar) ya qaryata ya kuma ba da baya



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 14

أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ

Shin bai sani ba cewa lalle Allah Yana ganin (sa)?



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 15

كَلَّا لَئِن لَّمۡ يَنتَهِ لَنَسۡفَعَۢا بِٱلنَّاصِيَةِ

A’aha! Tabbas idan bai hanu ba to za Mu ja shi ta makwarkwaxar kai



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 16

نَاصِيَةٖ كَٰذِبَةٍ خَاطِئَةٖ

Makwarkwaxar kai mai qaryatawa, mai aikata laifi