Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 17

سَأُرۡهِقُهُۥ صَعُودًا

Ba da daxewa ba zan xora masa (azaba) mai matsananciyar wahala



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 18

إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ

Lalle shi ya yi tunani, ya kuma auna (a ransa)



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 19

فَقُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sai aka la’ane shi, yaya ya yi irin wannan awon?



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 20

ثُمَّ قُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sannan aka kuma la’antar sa, yaya ya yi wannan awon?



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 21

ثُمَّ نَظَرَ

Sannan ya yi nazari



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 22

ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ

Sannan ya xaure fuska, ya kuma murtuke



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 23

ثُمَّ أَدۡبَرَ وَٱسۡتَكۡبَرَ

Sannan ya ba da baya (daga imani) ya kuma yi girman kai



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 24

فَقَالَ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ يُؤۡثَرُ

Sai ya ce: “Wannan (Alqur’ani) ba komai ba ne sai sihiri da aka samo (daga wasu)



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 25

إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا قَوۡلُ ٱلۡبَشَرِ

“Wannan ba komai ba ne sai magana irin ta mutane.”



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 26

سَأُصۡلِيهِ سَقَرَ

(Allah ya ce): Da sannu zan shigar da shi (wutar) Saqara



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 27

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سَقَرُ

Me ya sanar da kai abin da ake ce wa Saqara?



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 28

لَا تُبۡقِي وَلَا تَذَرُ

Ba ta ragewa kuma ba ta barin (komai)



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 29

لَوَّاحَةٞ لِّلۡبَشَرِ

Mai xaxxaye fata ce



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 30

عَلَيۡهَا تِسۡعَةَ عَشَرَ

Akwai (mala’iku) goma sha tara suna tsaron ta



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 31

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ

Ba Mu kuwa sanya masu tsaron wutar ba sai mala’iku, ba Mu kuma sanya adadinsu ba sai don fitina ga waxanda suka kafirta, don kuma waxanda aka bai wa littafi su sami yaqini, waxanda kuma suka yi imani su qara imani, waxanda aka bai wa littafi da muminai kuma kada su yi tababa, don kuma waxanda suke da raunin imani a zukatansu da kuma kafirai su ce: “Me Allah Yake nufi da yin misali da wannan (adadin)?” Kamar haka Allah Yake vatar da wanda Ya ga dama, Yake kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Ba kuma wanda ya san (yawan) rundunar Ubangijinka sai Shi. Ita (Saqara) kuma ba wata abu ba ce face wa’azi ga mutane



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 32

كَلَّا وَٱلۡقَمَرِ

A’a. Na rantse da wata



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 33

وَٱلَّيۡلِ إِذۡ أَدۡبَرَ

Da kuma dare idan ya ba da baya



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 34

وَٱلصُّبۡحِ إِذَآ أَسۡفَرَ

Da kuma asuba idan ta bayyana (da haskenta)



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 35

إِنَّهَا لَإِحۡدَى ٱلۡكُبَرِ

Lalle ita (Saqara) tana xaya daga manya-manyan (bala’o’i)



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 36

نَذِيرٗا لِّلۡبَشَرِ

Gargaxi ce ga mutane



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 37

لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَتَقَدَّمَ أَوۡ يَتَأَخَّرَ

Ga wanda ya ga dama daga cikinku, ya ci gaba ko ya ci baya



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 38

كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ رَهِينَةٌ

Kowane rai jingina ne ga abin da ya tsuwurwurta[1]


1- Watau jingina ne ga ayyukansu, ko dai su hallakar da shi ko su kuvutar da shi, su ‘yanta shi.


Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 39

إِلَّآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡيَمِينِ

Sai dai ga ma’abota dama[1]


1- Watau waxanda za su karvi littattafan ayyukansu ta hannayensu na dama.


Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 40

فِي جَنَّـٰتٖ يَتَسَآءَلُونَ

(Su kam suna) cikin gidajen Aljanna suna tambayar juna



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 41

عَنِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Game da manyan masu laifuka



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 42

مَا سَلَكَكُمۡ فِي سَقَرَ

(Suna cewa): “Me ya shigar da ku cikin Saqara?”



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 43

قَالُواْ لَمۡ نَكُ مِنَ ٱلۡمُصَلِّينَ

Suka ce: “Ba mu zama daga cikin masallata ba



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 44

وَلَمۡ نَكُ نُطۡعِمُ ٱلۡمِسۡكِينَ

“Kuma ba mu kasance muna ciyar da miskini ba



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 45

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلۡخَآئِضِينَ

“Mun kuma kasance muna kutsawa (cikin varna)[1] tare da masu kutsawa


1- Watau suna faxar qarerayi game da Annabi () da Alqur’ani.


Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 46

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

“Kuma mun kasance muna qaryata ranar sakamako