Capítulo: Suratul Lail

Verso : 11

وَمَا يُغۡنِي عَنۡهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ

Dukiyarsa kuma ba za ta amfane shi ba idan ya gangara (cikin wuta)



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 12

إِنَّ عَلَيۡنَا لَلۡهُدَىٰ

Lalle bayyana hanyar shiriya a kanmu yake



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 13

وَإِنَّ لَنَا لَلۡأٓخِرَةَ وَٱلۡأُولَىٰ

Kuma lalle lahira da duniya namu ne



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 14

فَأَنذَرۡتُكُمۡ نَارٗا تَلَظَّىٰ

Don haka ina yi muku gargaxin wata wuta mai ruruwa



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 15

لَا يَصۡلَىٰهَآ إِلَّا ٱلۡأَشۡقَى

Ba mai shigar ta sai mafi tsiyacewa



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 16

ٱلَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ

Wanda ya qaryata ya kuma ba da baya



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 17

وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلۡأَتۡقَى

Kuma lalle za a nesantar da mafi taqawa[1] daga gare ta


1- Da dama daga cikin malaman tafsiri sun bayyana cewa a nan ana nufin Abubakar As-Siddiq ().


Capítulo: Suratul Lail

Verso : 18

ٱلَّذِي يُؤۡتِي مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ

Wanda yake ba da dukiyarsa yana neman tsarkaka



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 19

وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعۡمَةٖ تُجۡزَىٰٓ

Ba kuwa wani da ya yi masa wata ni’ima da za a saka masa (a kanta)[1]


1- Watau ba yana ciyar da dukiyarsa ne don ya saka wa wani a kan wata ni’ima da ya yi masa ba.


Capítulo: Suratul Lail

Verso : 20

إِلَّا ٱبۡتِغَآءَ وَجۡهِ رَبِّهِ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Sai dai don neman Fuskar Ubangijinsa Maxaukaki



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 21

وَلَسَوۡفَ يَرۡضَىٰ

Kuma lalle zai yarda (da sakamakon da za a ba shi)[1]


1- Watau gidan Aljanna a lahira.


Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 1

وَٱلضُّحَىٰ

Na rantse da lokacin hantsi



Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 2

وَٱلَّيۡلِ إِذَا سَجَىٰ

Da kuma dare idan ya yi tsit[1]


1- Watau ya lulluve komai da duhunsa, mutane su shiga mazaunansu don su yi barci.


Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 3

مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ

Ubangijinka bai bar ka ba, kuma bai qi ka ba



Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 4

وَلَلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لَّكَ مِنَ ٱلۡأُولَىٰ

Kuma lalle lahira ta fi maka alheri a kan duniya



Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 5

وَلَسَوۡفَ يُعۡطِيكَ رَبُّكَ فَتَرۡضَىٰٓ

Kuma lalle Ubangijinka zai ba ka har sai ka yarda (da abin da Ya ba ka)



Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 6

أَلَمۡ يَجِدۡكَ يَتِيمٗا فَـَٔاوَىٰ

Shin bai same ka maraya ba sai Ya haxa ka (da mai kula da kai)?



Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 7

وَوَجَدَكَ ضَآلّٗا فَهَدَىٰ

Ya kuma same ka marashin shiriya Ya shiryar (da kai)?



Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 8

وَوَجَدَكَ عَآئِلٗا فَأَغۡنَىٰ

Ya kuma same ka matalauci Ya wadata (ka)?



Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 9

فَأَمَّا ٱلۡيَتِيمَ فَلَا تَقۡهَرۡ

Don haka maraya fa kada ka yi masa fin qarfi



Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 10

وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنۡهَرۡ

Mai tambaya[1] kuma kada ka daka masa tsawa


1- Watau mai neman taimako saboda buqata, ko mai tambaya don neman sani.


Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 11

وَأَمَّا بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثۡ

Amma kuma game da ni’imar Ubangijinka sai ka ba da labari



Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 1

أَلَمۡ نَشۡرَحۡ لَكَ صَدۡرَكَ

Shin ba Mu yalwata maka qirjinka ba[1]?


1- Watau ya hore masa son sauraren wahayin da yake yiwo masa da kuma juriya a kan gallazawar mutanensa.


Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 2

وَوَضَعۡنَا عَنكَ وِزۡرَكَ

Muka kuma sauke maka nauye-nauyenka[1]?


1- Watau Allah () ya gafarta masa duk wasu laifuka na baya da na nan gaba idan za su samu.


Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 3

ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ

Wanda ya nauyayi bayanka?



Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 4

وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ

Muka kuma xaukaka maka ambatonka[1]?


1- Watau kamar ambatonsa a cikin kiran salla da iqama da tahiya da sauransu.


Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 5

فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا

To lalle tsanani yana tare da sauqi



Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 6

إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا

Lalle tsananin yana tare da sauqi



Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 7

فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ

Saboda haka idan ka gama (harkokinka) sai ka kafu (wajen bautar Allah)



Capítulo: Suratus Sharh

Verso : 8

وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب

Sannan kuma ka yi kwaxayi wajen Ubangijinka kawai