وَٱتَّقُواْ فِتۡنَةٗ لَّا تُصِيبَنَّ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ مِنكُمۡ خَآصَّةٗۖ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ
Ku kiyayi fitinar da ba kawai waxanda suka yi zalunci za ta shafa ba, kuma ku sani cewa lalle Allah Mai tsananin uquba ne
وَٱذۡكُرُوٓاْ إِذۡ أَنتُمۡ قَلِيلٞ مُّسۡتَضۡعَفُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ تَخَافُونَ أَن يَتَخَطَّفَكُمُ ٱلنَّاسُ فَـَٔاوَىٰكُمۡ وَأَيَّدَكُم بِنَصۡرِهِۦ وَرَزَقَكُم مِّنَ ٱلطَّيِّبَٰتِ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ
Kuma ku tuna lokacin da kuke ‘yan tsirari masu rauni a bayan qasa, kuna tsoron kada wasu mutane su fauce ku, sai Ya tattara ku (a Madina) Ya kuma qarfafa ku da taimakonsa, Ya kuma arzuta ku da tsarkakan abubuwa don ku godiya
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَخُونُواْ ٱللَّهَ وَٱلرَّسُولَ وَتَخُونُوٓاْ أَمَٰنَٰتِكُمۡ وَأَنتُمۡ تَعۡلَمُونَ
Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku ha’inci Allah da Manzo, (kada) kuma ku ha’inci amanoninku alhali kuna sane
وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّمَآ أَمۡوَٰلُكُمۡ وَأَوۡلَٰدُكُمۡ فِتۡنَةٞ وَأَنَّ ٱللَّهَ عِندَهُۥٓ أَجۡرٌ عَظِيمٞ
Kuma ku sani cewa, dukiyoyinku da ‘ya’yanku fitina ne, Allah kuma lalle a wurinsa lada mai girma yake
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِن تَتَّقُواْ ٱللَّهَ يَجۡعَل لَّكُمۡ فُرۡقَانٗا وَيُكَفِّرۡ عَنكُمۡ سَيِّـَٔاتِكُمۡ وَيَغۡفِرۡ لَكُمۡۗ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ
Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka kiyaye dokokin Allah, to zai sanya muku (hanyar) tsira Ya kuma kankare muku munanan ayyukanku kuma Ya gafarta muku. Allah kuwa Ma’abocin babbar falala ne
وَإِذۡ يَمۡكُرُ بِكَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيُثۡبِتُوكَ أَوۡ يَقۡتُلُوكَ أَوۡ يُخۡرِجُوكَۚ وَيَمۡكُرُونَ وَيَمۡكُرُ ٱللَّهُۖ وَٱللَّهُ خَيۡرُ ٱلۡمَٰكِرِينَ
Kuma ka tuna lokacin da waxanda suka kafirta suke qulla maka makirci don su tsare ka ko kuma su kashe ka ko su kore ka. Suna kuma shirya makirci Allah kuma Yana mayar musu sakamakon makircinsu. Allah kuma (Shi ne) Ya fi masu makirci iya (sakayyar) makirci[1]
1- Wannan bayani ne game da makircin da shugabannin Quraishawa suka shirya wa Annabi () a Makka kafin ya yi hijira zuwa Madina.
وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا قَالُواْ قَدۡ سَمِعۡنَا لَوۡ نَشَآءُ لَقُلۡنَا مِثۡلَ هَٰذَآ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّآ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Idan kuma ana karanta musu ayoyinmu sai su ce: “Haqiqa mun ji, ai da mun ga dama ba shakka da mun faxi irin wannan, wannan ba komai ba ne sai tatsuniyoyin mutanen da.”
وَإِذۡ قَالُواْ ٱللَّهُمَّ إِن كَانَ هَٰذَا هُوَ ٱلۡحَقَّ مِنۡ عِندِكَ فَأَمۡطِرۡ عَلَيۡنَا حِجَارَةٗ مِّنَ ٱلسَّمَآءِ أَوِ ٱئۡتِنَا بِعَذَابٍ أَلِيمٖ
Ka tuna kuma lokacin da suka ce: “Ya Allah, idan wannan (Alqur’ani) ya zamanto gaskiya ne daga wurinka yake, to sai Ka yi mana ruwan duwatsu daga sama ko kuma Ka kawo mana da wata azaba mai raxaxi.”
وَمَا كَانَ ٱللَّهُ لِيُعَذِّبَهُمۡ وَأَنتَ فِيهِمۡۚ وَمَا كَانَ ٱللَّهُ مُعَذِّبَهُمۡ وَهُمۡ يَسۡتَغۡفِرُونَ
Allah kuwa bai zamanto Mai yi musu azaba ba alhali kai kana cikinsu, kuma Allah ba zai yi musu azaba ba alhali suna neman gafara
وَمَا لَهُمۡ أَلَّا يُعَذِّبَهُمُ ٱللَّهُ وَهُمۡ يَصُدُّونَ عَنِ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ وَمَا كَانُوٓاْ أَوۡلِيَآءَهُۥٓۚ إِنۡ أَوۡلِيَآؤُهُۥٓ إِلَّا ٱلۡمُتَّقُونَ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ
Me zai hana Allah Ya yi musu azaba alhali su suna hana mutane zuwa Masallaci mai alfarma, alhali kuwa ba su zamanto masu qaunar Sa na haqiqa ba. Masu qaunar Sa na haqiqa su ne masu taqawa, sai dai yawancinsu ba sa sanin (haka)
وَمَا كَانَ صَلَاتُهُمۡ عِندَ ٱلۡبَيۡتِ إِلَّا مُكَآءٗ وَتَصۡدِيَةٗۚ فَذُوقُواْ ٱلۡعَذَابَ بِمَا كُنتُمۡ تَكۡفُرُونَ
Kuma sallarsu a Xakin (Ka’aba) ba ta zamanto ba sai fito da tafi. Sai ku xanxani azaba saboda abin da kuka zamanto kuna yi na kafirci
إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمۡ لِيَصُدُّواْ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِۚ فَسَيُنفِقُونَهَا ثُمَّ تَكُونُ عَلَيۡهِمۡ حَسۡرَةٗ ثُمَّ يُغۡلَبُونَۗ وَٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِلَىٰ جَهَنَّمَ يُحۡشَرُونَ
Lalle waxanda suka kafirta suna kashe dukiyoyinsu don su toshe hanyar Allah. To da sannu za su kashe ta (dukiyar) sannan ta zama nadama a gare su, sannan kuma a rinjaye su. Waxanda kuwa suka kafirta a Jahannama za a tattara su
لِيَمِيزَ ٱللَّهُ ٱلۡخَبِيثَ مِنَ ٱلطَّيِّبِ وَيَجۡعَلَ ٱلۡخَبِيثَ بَعۡضَهُۥ عَلَىٰ بَعۡضٖ فَيَرۡكُمَهُۥ جَمِيعٗا فَيَجۡعَلَهُۥ فِي جَهَنَّمَۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ
Don Allah Ya ware mummuna daga kyakkyawa, Ya kuma haxa mummuna wani a kan wani, sannan Ya tattara shi gaba xaya cikin Jahannama. Waxannan su ne asararru
قُل لِّلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِن يَنتَهُواْ يُغۡفَرۡ لَهُم مَّا قَدۡ سَلَفَ وَإِن يَعُودُواْ فَقَدۡ مَضَتۡ سُنَّتُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Ka ce da waxanda suka kafirta idan suka daina, to za a gafarta musu abin da ya riga ya wuce, idan kuma suka koma to fa ba shakka al’adar mutanen farko ta gabata[1]
1- Watau yadda Allah () ya hallaka al’ummun da suka gabata waxanda suka qaryata annabawansu.
وَقَٰتِلُوهُمۡ حَتَّىٰ لَا تَكُونَ فِتۡنَةٞ وَيَكُونَ ٱلدِّينُ كُلُّهُۥ لِلَّهِۚ فَإِنِ ٱنتَهَوۡاْ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِمَا يَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ
Kuma ku yaqe su har sai ya zamanto ba wata fitina[1], addini kuma ya zamanto dukkaninsa na Allah. Sannan idan suka daina, to lalle Allah Mai ganin abin da suke aikatawa ne
1- Watau watsuwar shirka a cikin al’umma da yunqurin hana mutane karvar gaskiya.
وَإِن تَوَلَّوۡاْ فَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ مَوۡلَىٰكُمۡۚ نِعۡمَ ٱلۡمَوۡلَىٰ وَنِعۡمَ ٱلنَّصِيرُ
Idan kuma suka ba da baya, to ku sani cewa, Allah (Shi ne) Majivincin al’amarinku. Madalla da wannan Majivinci, kuma madalla da wannan Mai taimako