Capítulo: Suratul An’am

Verso : 22

وَيَوۡمَ نَحۡشُرُهُمۡ جَمِيعٗا ثُمَّ نَقُولُ لِلَّذِينَ أَشۡرَكُوٓاْ أَيۡنَ شُرَكَآؤُكُمُ ٱلَّذِينَ كُنتُمۡ تَزۡعُمُونَ

Kuma (ka tuna) ranar da za Mu tattara su gaba xaya, sannan Mu ce da waxanda suka yi shirka: “Ina abokan tarayyarku waxanda kuka kasance kuna riyawa?”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 23

ثُمَّ لَمۡ تَكُن فِتۡنَتُهُمۡ إِلَّآ أَن قَالُواْ وَٱللَّهِ رَبِّنَا مَا كُنَّا مُشۡرِكِينَ

Sannan fitinarsu ba ta zamo komai ba, face cewar da suka yi: “Wallahi, ya Ubangijinmu, ba mu kasance masu yin shirka ba!”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 24

ٱنظُرۡ كَيۡفَ كَذَبُواْ عَلَىٰٓ أَنفُسِهِمۡۚ وَضَلَّ عَنۡهُم مَّا كَانُواْ يَفۡتَرُونَ

Duba ka ga yadda suka yi wa kansu qarya. Kuma abin da suka kasance suna qirqira ya vace musu



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 25

وَمِنۡهُم مَّن يَسۡتَمِعُ إِلَيۡكَۖ وَجَعَلۡنَا عَلَىٰ قُلُوبِهِمۡ أَكِنَّةً أَن يَفۡقَهُوهُ وَفِيٓ ءَاذَانِهِمۡ وَقۡرٗاۚ وَإِن يَرَوۡاْ كُلَّ ءَايَةٖ لَّا يُؤۡمِنُواْ بِهَاۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءُوكَ يُجَٰدِلُونَكَ يَقُولُ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّآ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Kuma daga cikinsu akwai wanda yake sauraren ka; kuma Mun sanya murafai a zukatansu, ta yadda ba za su iya fahimtar sa ba, haka kuma a kunnuwansu akwai wata toshiya. Kuma in da za su ga kowace irin aya ce, ba za su yi imani da ita ba. Har ma idan sun zo maka suna jayayya da kai, (sai) waxanda suka kafirta su riqa cewa: “Ai wannan ba komai ba ne face tatsuniyoyin mutanen farko.”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 26

وَهُمۡ يَنۡهَوۡنَ عَنۡهُ وَيَنۡـَٔوۡنَ عَنۡهُۖ وَإِن يُهۡلِكُونَ إِلَّآ أَنفُسَهُمۡ وَمَا يَشۡعُرُونَ

Kuma suna hana (mutane) sauraren sa (Alqur’ani), kuma su kansu suna qara nesanta da shi; kuma ba kowa suke hallakarwa ba face kawunansu, sai dai su ba sa jin hakan



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 27

وَلَوۡ تَرَىٰٓ إِذۡ وُقِفُواْ عَلَى ٱلنَّارِ فَقَالُواْ يَٰلَيۡتَنَا نُرَدُّ وَلَا نُكَذِّبَ بِـَٔايَٰتِ رَبِّنَا وَنَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Da kuma za ka ga lokacin da ake tsayar da su a gaban wuta, sai su ce: “Kaiconmu, ina ma da za a mayar da mu (duniya), to da ba za mu sake qaryata ayoyin Ubangijinmu ba, kuma za mu zamanto cikin muminai.”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 28

بَلۡ بَدَا لَهُم مَّا كَانُواْ يُخۡفُونَ مِن قَبۡلُۖ وَلَوۡ رُدُّواْ لَعَادُواْ لِمَا نُهُواْ عَنۡهُ وَإِنَّهُمۡ لَكَٰذِبُونَ

A’a, ba haka ba ne, abin da suke voyewa a da shi ne ya bayyana a gare su[1]; kuma in da za a mayar da su, to da sun koma kan abin da aka hana su. Kuma lalle su tabbas maqaryata ne


1- A duniya suna voye gaskiyar manzancin Annabi () duk da cewa sun san gaskiyarsa.


Capítulo: Suratul An’am

Verso : 29

وَقَالُوٓاْ إِنۡ هِيَ إِلَّا حَيَاتُنَا ٱلدُّنۡيَا وَمَا نَحۡنُ بِمَبۡعُوثِينَ

Kuma suka ce: “Ba wata (rayuwa) sai rayuwarmu ta duniya, kuma mu ba waxanda za a sake tashin mu ba ne.”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 30

وَلَوۡ تَرَىٰٓ إِذۡ وُقِفُواْ عَلَىٰ رَبِّهِمۡۚ قَالَ أَلَيۡسَ هَٰذَا بِٱلۡحَقِّۚ قَالُواْ بَلَىٰ وَرَبِّنَاۚ قَالَ فَذُوقُواْ ٱلۡعَذَابَ بِمَا كُنتُمۡ تَكۡفُرُونَ

Kuma in da za ka ga lokacin da aka tsayar da su a gaban Ubangjinsu; ya ce: “Shin ashe wannan ba gaskiya ne ba?” Sai su ce: “Gaskiya ne, muna rantsuwa da Ubangijinmu.” Sai Ya ce: “To ku xanxani azaba saboda abin da kuka kasance kuna yi na kafirci.”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 31

قَدۡ خَسِرَ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِلِقَآءِ ٱللَّهِۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءَتۡهُمُ ٱلسَّاعَةُ بَغۡتَةٗ قَالُواْ يَٰحَسۡرَتَنَا عَلَىٰ مَا فَرَّطۡنَا فِيهَا وَهُمۡ يَحۡمِلُونَ أَوۡزَارَهُمۡ عَلَىٰ ظُهُورِهِمۡۚ أَلَا سَآءَ مَا يَزِرُونَ

Haqiqa waxanda suka qaryata haxuwa da Allah sun yi hasara; har sai lokacin da alqiyama ta zo musu ba zato ba tsammani, sai su ce: “Kaiconmu kan irin sakacin da muka yi a cikinta (duniya),” alhalin kuwa suna xauke da kayan laifukansu a bayansu. Ku saurara, abin da suka xauka na laifi ya munana matuqa



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 32

وَمَا ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَآ إِلَّا لَعِبٞ وَلَهۡوٞۖ وَلَلدَّارُ ٱلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لِّلَّذِينَ يَتَّقُونَۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Kuma rayuwar duniya ba komai ba ce face wasa da sharholiya; kuma lalle gidan lahira shi ne mafi alheri ga waxanda suke kiyaye dokokin (Allah). Shin ba za ku hankalta ba?



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 33

قَدۡ نَعۡلَمُ إِنَّهُۥ لَيَحۡزُنُكَ ٱلَّذِي يَقُولُونَۖ فَإِنَّهُمۡ لَا يُكَذِّبُونَكَ وَلَٰكِنَّ ٱلظَّـٰلِمِينَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ يَجۡحَدُونَ

Haqiqa Muna da cikakkiyar masaniyar cewa, lalle irin abin da suke faxa yakan baqanta maka rai; to a gaskiya su ba kai suke qaryatawa ba, sai dai azzalumai suna jayayya ne da ayoyin Allah



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 34

وَلَقَدۡ كُذِّبَتۡ رُسُلٞ مِّن قَبۡلِكَ فَصَبَرُواْ عَلَىٰ مَا كُذِّبُواْ وَأُوذُواْ حَتَّىٰٓ أَتَىٰهُمۡ نَصۡرُنَاۚ وَلَا مُبَدِّلَ لِكَلِمَٰتِ ٱللَّهِۚ وَلَقَدۡ جَآءَكَ مِن نَّبَإِيْ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Kuma lalle haqiqa an qaryata waxansu manzanni a gabaninka, sai suka yi haquri a kan qaryata su da aka yi, kuma an cutar da su, har sai da taimakonmu ya zo musu. Kuma babu wanda ya isa ya musanya kalmomin Allah. Kuma lalle haqiqa wani sashi na labarin manzanni ya zo maka



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 35

وَإِن كَانَ كَبُرَ عَلَيۡكَ إِعۡرَاضُهُمۡ فَإِنِ ٱسۡتَطَعۡتَ أَن تَبۡتَغِيَ نَفَقٗا فِي ٱلۡأَرۡضِ أَوۡ سُلَّمٗا فِي ٱلسَّمَآءِ فَتَأۡتِيَهُم بِـَٔايَةٖۚ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَجَمَعَهُمۡ عَلَى ٱلۡهُدَىٰۚ فَلَا تَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡجَٰهِلِينَ

Kuma idan bijirewarsu ta dame ka, to idan har kana iya haqa rami a cikin qasa, ko kuma (ka samu) wani tsani ka hau sama, don ka zo musu da wata aya, (to ka yi hakan). Kuma in da Allah Ya ga dama, tabbas da Ya tara su gaba xaya a kan shiriya. Don haka kada ka kasance cikin jahilai