Capítulo: Suratun Nur

Verso : 51

إِنَّمَا كَانَ قَوۡلَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ إِذَا دُعُوٓاْ إِلَى ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ لِيَحۡكُمَ بَيۡنَهُمۡ أَن يَقُولُواْ سَمِعۡنَا وَأَطَعۡنَاۚ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

Muminai ba su da wata magana idan aka kira su zuwa ga Allah da Manzonsa don ya yi hukunci a tsakaninsu sai faxar: “Mun ji kuma mun bi.” Waxannan kuwa su ne masu babban rabo



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 52

وَمَن يُطِعِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ وَيَخۡشَ ٱللَّهَ وَيَتَّقۡهِ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡفَآئِزُونَ

Duk kuwa wanda ya bi Allah da Manzonsa kuma yake tsoron Allah kuma yake kiyaye dokokinsa, to waxannan su ne masu rabauta



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 53

۞وَأَقۡسَمُواْ بِٱللَّهِ جَهۡدَ أَيۡمَٰنِهِمۡ لَئِنۡ أَمَرۡتَهُمۡ لَيَخۡرُجُنَّۖ قُل لَّا تُقۡسِمُواْۖ طَاعَةٞ مَّعۡرُوفَةٌۚ إِنَّ ٱللَّهَ خَبِيرُۢ بِمَا تَعۡمَلُونَ

Suka kuma rantse da Allah iya iyawarsu cewa lalle idan ka umarce su (da fita) tabbas za su fita. Ka ce (da su): “Ku daina rantse-rantse; biyayya (taku ta qarya) sananniya ce. Lalle Allah Masanin abin da kuke aikatawa ne.”



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 54

قُلۡ أَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُواْ ٱلرَّسُولَۖ فَإِن تَوَلَّوۡاْ فَإِنَّمَا عَلَيۡهِ مَا حُمِّلَ وَعَلَيۡكُم مَّا حُمِّلۡتُمۡۖ وَإِن تُطِيعُوهُ تَهۡتَدُواْۚ وَمَا عَلَى ٱلرَّسُولِ إِلَّا ٱلۡبَلَٰغُ ٱلۡمُبِينُ

Ka ce (da su): “Ku bi Allah kuma ku bi Manzo; sannan idan kuka ba da baya, to lalle nauyin abin da aka xora masa ne kawai a kansa; kuma nauyin da aka xora muku yana kanku, idan kuwa kuka bi shi za ku shiriya. Ba kuwa abin da yake kan Manzo sai isar da aike mabayyani



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 55

وَعَدَ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مِنكُمۡ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَيَسۡتَخۡلِفَنَّهُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ كَمَا ٱسۡتَخۡلَفَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ وَلَيُمَكِّنَنَّ لَهُمۡ دِينَهُمُ ٱلَّذِي ٱرۡتَضَىٰ لَهُمۡ وَلَيُبَدِّلَنَّهُم مِّنۢ بَعۡدِ خَوۡفِهِمۡ أَمۡنٗاۚ يَعۡبُدُونَنِي لَا يُشۡرِكُونَ بِي شَيۡـٔٗاۚ وَمَن كَفَرَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡفَٰسِقُونَ

Allah kuwa Ya yi wa waxanda suka yi imani daga cikinku suka kuma yi aiki na gari alqawarin lalle zai sanya su halifofi a bayan qasa kamar yadda Ya sanya waxanda suke gabaninsu halifofi, kuma lalle zai tabbatar musu da addininsu wanda Ya yardar musu, tabbas kuma zai dawo musu da zaman lafiya bayan zamantowarsu cikin tsoro. Su bauta mini, ba sa yin shirkar komai da Ni. Wanda kuwa ya kafirta bayan wannan, to waxannan su ne fasiqai



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 56

وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَأَطِيعُواْ ٱلرَّسُولَ لَعَلَّكُمۡ تُرۡحَمُونَ

Kuma ku tsai da salla ku kuma ba da zakka kuma ku bi Manzo don a ji qan ku



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 57

لَا تَحۡسَبَنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مُعۡجِزِينَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ وَمَأۡوَىٰهُمُ ٱلنَّارُۖ وَلَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Kada kuma ka tsammaci waxanda suka kafirta za su gagara a bayan qasa, kuma makomarsu wuta ce; makoma kuwa ta munana



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 58

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لِيَسۡتَـٔۡذِنكُمُ ٱلَّذِينَ مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُكُمۡ وَٱلَّذِينَ لَمۡ يَبۡلُغُواْ ٱلۡحُلُمَ مِنكُمۡ ثَلَٰثَ مَرَّـٰتٖۚ مِّن قَبۡلِ صَلَوٰةِ ٱلۡفَجۡرِ وَحِينَ تَضَعُونَ ثِيَابَكُم مِّنَ ٱلظَّهِيرَةِ وَمِنۢ بَعۡدِ صَلَوٰةِ ٱلۡعِشَآءِۚ ثَلَٰثُ عَوۡرَٰتٖ لَّكُمۡۚ لَيۡسَ عَلَيۡكُمۡ وَلَا عَلَيۡهِمۡ جُنَاحُۢ بَعۡدَهُنَّۚ طَوَّـٰفُونَ عَلَيۡكُم بَعۡضُكُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖۚ كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمُ ٱلۡأٓيَٰتِۗ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٞ

Ya ku waxanda suka yi imani, bayinku da kuma waxanda ba su isa mafarki ba a cikinku (watau waxanda ba su balaga ba) su nemi izininku sau uku. Kafin sallar Asuba da sanda kuke tuve tufafinku a lokacin garjin rana da kuma bayan sallar Lisha. Lokatai ne guda uku na tsiraicinku[1]. Babu laifi a kanku ko a kansu bayansu (waxannan lokatai). Masu shige da fice ne a gare ku sashinku bisa sashi. Kamar haka ne Allah Yake bayyana muku ayoyi. Allah kuma Masani ne, Mai hikima


1- Watau lokacin da suke sanya tufafin barci ko na shan iska a gida.


Capítulo: Suratun Nur

Verso : 59

وَإِذَا بَلَغَ ٱلۡأَطۡفَٰلُ مِنكُمُ ٱلۡحُلُمَ فَلۡيَسۡتَـٔۡذِنُواْ كَمَا ٱسۡتَـٔۡذَنَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۚ كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمۡ ءَايَٰتِهِۦۗ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٞ

Idan kuma yara daga cikinku suka isa mafarki (watau suka balaga) sai su nemi izini kamar yadda waxanda suke gabaninsu suka riqa neman izini. Kamar haka Allah Yake bayyana muku ayoyinsa. Allah kuwa Masani ne, Mai hikima



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 60

وَٱلۡقَوَٰعِدُ مِنَ ٱلنِّسَآءِ ٱلَّـٰتِي لَا يَرۡجُونَ نِكَاحٗا فَلَيۡسَ عَلَيۡهِنَّ جُنَاحٌ أَن يَضَعۡنَ ثِيَابَهُنَّ غَيۡرَ مُتَبَرِّجَٰتِۭ بِزِينَةٖۖ وَأَن يَسۡتَعۡفِفۡنَ خَيۡرٞ لَّهُنَّۗ وَٱللَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٞ

Tsofaffin mata kuwa waxanda ba sa tsammanin yin aure to babu laifi a kansu su sauke lulluvinsu, amma ba masu fitar da adonsu ba; amma kuma su yi lulluvi shi ya fi zama alheri a gare su. Allah kuwa Mai ji ne, Masani



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 61

لَّيۡسَ عَلَى ٱلۡأَعۡمَىٰ حَرَجٞ وَلَا عَلَى ٱلۡأَعۡرَجِ حَرَجٞ وَلَا عَلَى ٱلۡمَرِيضِ حَرَجٞ وَلَا عَلَىٰٓ أَنفُسِكُمۡ أَن تَأۡكُلُواْ مِنۢ بُيُوتِكُمۡ أَوۡ بُيُوتِ ءَابَآئِكُمۡ أَوۡ بُيُوتِ أُمَّهَٰتِكُمۡ أَوۡ بُيُوتِ إِخۡوَٰنِكُمۡ أَوۡ بُيُوتِ أَخَوَٰتِكُمۡ أَوۡ بُيُوتِ أَعۡمَٰمِكُمۡ أَوۡ بُيُوتِ عَمَّـٰتِكُمۡ أَوۡ بُيُوتِ أَخۡوَٰلِكُمۡ أَوۡ بُيُوتِ خَٰلَٰتِكُمۡ أَوۡ مَا مَلَكۡتُم مَّفَاتِحَهُۥٓ أَوۡ صَدِيقِكُمۡۚ لَيۡسَ عَلَيۡكُمۡ جُنَاحٌ أَن تَأۡكُلُواْ جَمِيعًا أَوۡ أَشۡتَاتٗاۚ فَإِذَا دَخَلۡتُم بُيُوتٗا فَسَلِّمُواْ عَلَىٰٓ أَنفُسِكُمۡ تَحِيَّةٗ مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِ مُبَٰرَكَةٗ طَيِّبَةٗۚ كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمُ ٱلۡأٓيَٰتِ لَعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Babu wani laifi a kan makaho, babu kuma wani laifi a kan gurgu, kuma babu wani laifi a kan marar lafiya ko kuma a kanku, kan ku ci a gidajenku ko a gidajen iyayenku maza ko a gidajen iyayenku mata ko a gidajen ‘yan’uwanku maza ko a gidajen ‘yan’uwanku mata ko a gidajen baffanninku ko a gidajen gwaggwanninku ko kuma a gidajen kawunnanku ko kuma a gidajen yagwalgwalanku, ko kuma abin da kuka mallaki mabuxansa, ko kuma na abokinku. Babu wani laifi a kanku ku ci tare ko kuma daban-daban, sannan idan za ku shiga gidaje sai ku yi wa junanku sallama, (wannan) gaisuwa ce daga wurin Allah mai albarka tsattsarka. Kamar haka Allah Yake bayyana muku ayoyi don ku hankalta



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 62

إِنَّمَا ٱلۡمُؤۡمِنُونَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَإِذَا كَانُواْ مَعَهُۥ عَلَىٰٓ أَمۡرٖ جَامِعٖ لَّمۡ يَذۡهَبُواْ حَتَّىٰ يَسۡتَـٔۡذِنُوهُۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ يَسۡتَـٔۡذِنُونَكَ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦۚ فَإِذَا ٱسۡتَـٔۡذَنُوكَ لِبَعۡضِ شَأۡنِهِمۡ فَأۡذَن لِّمَن شِئۡتَ مِنۡهُمۡ وَٱسۡتَغۡفِرۡ لَهُمُ ٱللَّهَۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Muminai na haqiqa (su ne) waxanda suka yi imani da Allah da Manzonsa, idan kuma suka kasance tare da shi bisa wani al’amari na jama’a, to ba za su tafi ba har sai sun nemi izininsa. Lalle waxanda suke neman izininka waxannan (su ne) waxanda suka yi imani da Allah da Manzonsa. To idan sun nemi izininka saboda wani sha’aninsu, sai ka yi izini ga wanda ka ga dama daga cikinsu, kuma ka nema musu gafarar Allah. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai rahama



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 63

لَّا تَجۡعَلُواْ دُعَآءَ ٱلرَّسُولِ بَيۡنَكُمۡ كَدُعَآءِ بَعۡضِكُم بَعۡضٗاۚ قَدۡ يَعۡلَمُ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ يَتَسَلَّلُونَ مِنكُمۡ لِوَاذٗاۚ فَلۡيَحۡذَرِ ٱلَّذِينَ يُخَالِفُونَ عَنۡ أَمۡرِهِۦٓ أَن تُصِيبَهُمۡ فِتۡنَةٌ أَوۡ يُصِيبَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٌ

Kada ku mayar da kiran Manzo a tsakaninku kamar kiran junanku ga juna[1]. Haqiqa Allah Yana sane da waxanda suke zare jiki daga cikinku a voye. To lalle waxanda suke sava wa umarninsa su ji tsoron kada wata fitina ta shafe su ko kuma wata azaba mai raxaxi ta same su


1- Watau xayansu ya riqa cewa: “Ya Muhammadu” ko “Ya Muhammadu xan Abdullahi” ko “Ya xan Abdullahi”. Sai dai su ce: “Ya Manzon Allah” ko “Ya Annabin Allah”.


Capítulo: Suratun Nur

Verso : 64

أَلَآ إِنَّ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ قَدۡ يَعۡلَمُ مَآ أَنتُمۡ عَلَيۡهِ وَيَوۡمَ يُرۡجَعُونَ إِلَيۡهِ فَيُنَبِّئُهُم بِمَا عَمِلُواْۗ وَٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمُۢ

Ku saurara, lalle abin da yake sammai da qasa na Allah ne; haqiqa Yana sane da abin da ku kuke kansa, da kuma ranar da za a komar da su zuwa gare Shi, sannan Ya ba su labarin abin da suka aikata. Allah Masanin komai ne



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 1

تَبَارَكَ ٱلَّذِي نَزَّلَ ٱلۡفُرۡقَانَ عَلَىٰ عَبۡدِهِۦ لِيَكُونَ لِلۡعَٰلَمِينَ نَذِيرًا

(Allah) Wanda Ya saukar wa Bawansa Alqur’ani don ya zamo mai gargaxi ga talikai albarkatunsa sun yawaita



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 2

ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَلَمۡ يَتَّخِذۡ وَلَدٗا وَلَمۡ يَكُن لَّهُۥ شَرِيكٞ فِي ٱلۡمُلۡكِ وَخَلَقَ كُلَّ شَيۡءٖ فَقَدَّرَهُۥ تَقۡدِيرٗا

(Shi ne) Wanda mulkin sammai da qasa nasa ne, kuma bai riqi wani xa ba, ba kuma Shi da wani abokin tarayya a cikin mulkin, Ya kuma halicci kowanne abu, sannan Ya ajiye shi a irin gwargwadon da ya dace da shi



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 3

وَٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ ءَالِهَةٗ لَّا يَخۡلُقُونَ شَيۡـٔٗا وَهُمۡ يُخۡلَقُونَ وَلَا يَمۡلِكُونَ لِأَنفُسِهِمۡ ضَرّٗا وَلَا نَفۡعٗا وَلَا يَمۡلِكُونَ مَوۡتٗا وَلَا حَيَوٰةٗ وَلَا نُشُورٗا

Kuma suka riqi ababen bauta ba Shi ba, ba sa halittar komai, alhali kuwa su ake halittawa, kuma ba sa mallakar cuta ko amfani ga kawunansu, ba sa kuma mallakar kashewa ko rayawa ko tashi (bayan mutuwa)



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 4

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّآ إِفۡكٌ ٱفۡتَرَىٰهُ وَأَعَانَهُۥ عَلَيۡهِ قَوۡمٌ ءَاخَرُونَۖ فَقَدۡ جَآءُو ظُلۡمٗا وَزُورٗا

Waxanda kuma suka kafirta suka ce: “Wannan (Alqur’ani) ba komai ba ne sai qarya da ya qage ta kuma wasu mutane daban suka taimake shi a kansa.” To haqiqa sun zo da zalunci da kuma qarya



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 5

وَقَالُوٓاْ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ ٱكۡتَتَبَهَا فَهِيَ تُمۡلَىٰ عَلَيۡهِ بُكۡرَةٗ وَأَصِيلٗا

Suka kuma ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko ne da ya rubuta su, waxanda ake masa shiftar su safe da yamma.”



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 6

قُلۡ أَنزَلَهُ ٱلَّذِي يَعۡلَمُ ٱلسِّرَّ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ إِنَّهُۥ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Ka ce (da su): “Wanda Yake sane da asirin sammai da qasa Shi Ya saukar da shi. Lalle Shi Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai.”



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 7

وَقَالُواْ مَالِ هَٰذَا ٱلرَّسُولِ يَأۡكُلُ ٱلطَّعَامَ وَيَمۡشِي فِي ٱلۡأَسۡوَاقِ لَوۡلَآ أُنزِلَ إِلَيۡهِ مَلَكٞ فَيَكُونَ مَعَهُۥ نَذِيرًا

Suka kuma ce: “Me ya sa wannan Manzo yake cin abinci kuma yake tafiya cikin kasuwanni? Me ya hana a saukar masa da mala’ika, sai ya zama mai gargaxi tare da shi?



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 8

أَوۡ يُلۡقَىٰٓ إِلَيۡهِ كَنزٌ أَوۡ تَكُونُ لَهُۥ جَنَّةٞ يَأۡكُلُ مِنۡهَاۚ وَقَالَ ٱلظَّـٰلِمُونَ إِن تَتَّبِعُونَ إِلَّا رَجُلٗا مَّسۡحُورًا

Ko a jefo masa wata taskar dukiya ko ya zama yana da wani lambu wanda daga gare shi zai riqa ci?” Sai azzalumai suka ce “Ba wanda kuke bi sai wani mutum wanda aka yi wa sihiri!”



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 9

ٱنظُرۡ كَيۡفَ ضَرَبُواْ لَكَ ٱلۡأَمۡثَٰلَ فَضَلُّواْ فَلَا يَسۡتَطِيعُونَ سَبِيلٗا

To ka dubi yadda suka riqa buga maka misali[1], sai suka vata, don haka ba za su iya bin hanyar shiriya ba


1- Watau wani lokaci su ce masa mai sihiri, wani lokaci kuma su ce mawaqi, ko su ce boka, ko mai tavin hankali.


Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 10

تَبَارَكَ ٱلَّذِيٓ إِن شَآءَ جَعَلَ لَكَ خَيۡرٗا مِّن ذَٰلِكَ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ وَيَجۡعَل لَّكَ قُصُورَۢا

Albarkatun (Allah) sun yawaita, wanda idan Ya ga dama sai Ya sanya maka alheri fiye da waxannan: (su ne) gonakai waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, Ya kuma sanya maka maka-makan gidaje



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 11

بَلۡ كَذَّبُواْ بِٱلسَّاعَةِۖ وَأَعۡتَدۡنَا لِمَن كَذَّبَ بِٱلسَّاعَةِ سَعِيرًا

Ba haka ba ne, sun dai qaryata tashin alqiyama ne; Mun kuwa tanadi (wutar) Sa’ira ga wanda ya qaryata tashin alqiyama



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 12

إِذَا رَأَتۡهُم مِّن مَّكَانِۭ بَعِيدٖ سَمِعُواْ لَهَا تَغَيُّظٗا وَزَفِيرٗا

Idan (wutar) ta hango su daga wuri mai nisa sai su ji tafarfasa da gurnaninta



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 13

وَإِذَآ أُلۡقُواْ مِنۡهَا مَكَانٗا ضَيِّقٗا مُّقَرَّنِينَ دَعَوۡاْ هُنَالِكَ ثُبُورٗا

Idan kuwa aka jefa su cikinta a wani wuri quntatacce nata, suna ququnce, sai su riqa kiran hallaka a can



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 14

لَّا تَدۡعُواْ ٱلۡيَوۡمَ ثُبُورٗا وَٰحِدٗا وَٱدۡعُواْ ثُبُورٗا كَثِيرٗا

(Sai a ce da su): “A yau kada ku kirawo hallaka xaya kawai, ku kirawo hallaka da yawa!”



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 15

قُلۡ أَذَٰلِكَ خَيۡرٌ أَمۡ جَنَّةُ ٱلۡخُلۡدِ ٱلَّتِي وُعِدَ ٱلۡمُتَّقُونَۚ كَانَتۡ لَهُمۡ جَزَآءٗ وَمَصِيرٗا

Ka ce (da su): “Yanzu wannan ne ya fi alheri, ko kuwa Aljannar dawwama wadda aka yi wa masu taqawa alqawarinta, ta zama sakamako da makoma a gare su?”



Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 16

لَّهُمۡ فِيهَا مَا يَشَآءُونَ خَٰلِدِينَۚ كَانَ عَلَىٰ رَبِّكَ وَعۡدٗا مَّسۡـُٔولٗا

Suna da duk abin da suka ga dama a cikinta, masu dawwama ne. (Wannan kuma) ya kasance alqawari ne abin tambaya a kan Ubangijnka