Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 201

إِنَّ ٱلَّذِينَ ٱتَّقَوۡاْ إِذَا مَسَّهُمۡ طَـٰٓئِفٞ مِّنَ ٱلشَّيۡطَٰنِ تَذَكَّرُواْ فَإِذَا هُم مُّبۡصِرُونَ

Lalle waxanda suka kiyaye dokokin Allah, idan wani Shaixan mai sa waswasi ya shafe su, sai su tuna (da Allah), sai ga su suna gani tar



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 202

وَإِخۡوَٰنُهُمۡ يَمُدُّونَهُمۡ فِي ٱلۡغَيِّ ثُمَّ لَا يُقۡصِرُونَ

‘Yan’uwansu kuwa[1] suna qara kawo musu xauki na vata, sannan su ba sa taqaitawa


1- Su ne shaixanu na mutane da aljanu, suna qara ingiza kafirai cikin vata ba tare da suna gajiya ko qosawa a kan haka ba.


Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 203

وَإِذَا لَمۡ تَأۡتِهِم بِـَٔايَةٖ قَالُواْ لَوۡلَا ٱجۡتَبَيۡتَهَاۚ قُلۡ إِنَّمَآ أَتَّبِعُ مَا يُوحَىٰٓ إِلَيَّ مِن رَّبِّيۚ هَٰذَا بَصَآئِرُ مِن رَّبِّكُمۡ وَهُدٗى وَرَحۡمَةٞ لِّقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ

Kuma idan ba ka kawo musu wata aya ba, sai su ce: “Don me ba ka qirqiro ta ba?” Ka ce: “Ba abin da nake bi sai kawai abin da aka yi min wahayinsa daga Ubangijina. Waxannan hujjoji ne daga Ubangijinku da kuma shiriya da kuma rahama ga mutanen da suke yin imani.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 204

وَإِذَا قُرِئَ ٱلۡقُرۡءَانُ فَٱسۡتَمِعُواْ لَهُۥ وَأَنصِتُواْ لَعَلَّكُمۡ تُرۡحَمُونَ

Kuma idan an karanta Alqur’ani, to ku saurare shi, ku kuma yi tsit, don a ji qan ku



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 205

وَٱذۡكُر رَّبَّكَ فِي نَفۡسِكَ تَضَرُّعٗا وَخِيفَةٗ وَدُونَ ٱلۡجَهۡرِ مِنَ ٱلۡقَوۡلِ بِٱلۡغُدُوِّ وَٱلۡأٓصَالِ وَلَا تَكُن مِّنَ ٱلۡغَٰفِلِينَ

Kuma ka ambaci (sunan) Ubangijinka a ranka, kana mai qasqantar da kai, kuma kana mai jin tsoro, ba kuma tare da xaga murya ba, safe da yamma, kada kuma ka zamo cikin gafalallu



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 206

إِنَّ ٱلَّذِينَ عِندَ رَبِّكَ لَا يَسۡتَكۡبِرُونَ عَنۡ عِبَادَتِهِۦ وَيُسَبِّحُونَهُۥ وَلَهُۥ يَسۡجُدُونَۤ۩

Lalle waxanda suke wajen Ubangijinka, ba sa girman kai wajen bautar Sa, kuma suna tsarkake Shi, kuma gare Shi kawai suke yin sujjada



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 1

يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلۡأَنفَالِۖ قُلِ ٱلۡأَنفَالُ لِلَّهِ وَٱلرَّسُولِۖ فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَصۡلِحُواْ ذَاتَ بَيۡنِكُمۡۖ وَأَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥٓ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Suna tambayar ka game da ganimomi[1]; ka ce (da su): “Ganimomi na Allah ne da kuma Manzo; saboda haka ku kiyaye dokokin Allah, ku kuma gyara tsakaninku, kuma ku bi Allah da Manzonsa, idan kun kasance muminai.”


1- Watau tambayar da sahabbai suka yi wa Annabi () game da hukuncin ganimar yaqin Badar.


Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 2

إِنَّمَا ٱلۡمُؤۡمِنُونَ ٱلَّذِينَ إِذَا ذُكِرَ ٱللَّهُ وَجِلَتۡ قُلُوبُهُمۡ وَإِذَا تُلِيَتۡ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُهُۥ زَادَتۡهُمۡ إِيمَٰنٗا وَعَلَىٰ رَبِّهِمۡ يَتَوَكَّلُونَ

Muminai na haqiqa (su ne) kaxai waxanda idan aka ambaci Allah, sai zukatansu su raurawa, idan kuma aka karanta musu ayoyinsa, sai su qara musu imani, kuma ga Ubangijinsu ne kawai suke dogara



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 3

ٱلَّذِينَ يُقِيمُونَ ٱلصَّلَوٰةَ وَمِمَّا رَزَقۡنَٰهُمۡ يُنفِقُونَ

Waxanda suke tsayar da salla kuma suke ciyarwa daga abin da muka arzurta su



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 4

أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ حَقّٗاۚ لَّهُمۡ دَرَجَٰتٌ عِندَ رَبِّهِمۡ وَمَغۡفِرَةٞ وَرِزۡقٞ كَرِيمٞ

Waxannan su ne muminai na haqiqa. Suna da muqamai a wurin Ubangijinsu da kuma gafara da arziki na karamci



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 5

كَمَآ أَخۡرَجَكَ رَبُّكَ مِنۢ بَيۡتِكَ بِٱلۡحَقِّ وَإِنَّ فَرِيقٗا مِّنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ لَكَٰرِهُونَ

Kamar yadda Ubangijinka Ya fitar da kai daga gidanka (na Madina) da gaskiya, alhali lalle wata jama’a daga muminai tabbas suna qin (haka)



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 6

يُجَٰدِلُونَكَ فِي ٱلۡحَقِّ بَعۡدَ مَا تَبَيَّنَ كَأَنَّمَا يُسَاقُونَ إِلَى ٱلۡمَوۡتِ وَهُمۡ يَنظُرُونَ

Suna jayayya da kai game da abin da yake tabbas, kai ka ce ana kora su ne wajen mutuwa, alhali kuwa suna kallo



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 7

وَإِذۡ يَعِدُكُمُ ٱللَّهُ إِحۡدَى ٱلطَّآئِفَتَيۡنِ أَنَّهَا لَكُمۡ وَتَوَدُّونَ أَنَّ غَيۡرَ ذَاتِ ٱلشَّوۡكَةِ تَكُونُ لَكُمۡ وَيُرِيدُ ٱللَّهُ أَن يُحِقَّ ٱلۡحَقَّ بِكَلِمَٰتِهِۦ وَيَقۡطَعَ دَابِرَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

(Ka tuna) kuma lokacin da Allah Ya yi muku alqawarin xayar jama’an nan guda biyu (na abokan gaba)[1] cewa, lalle taku ce, sai kuka riqa fatan marar wahalar ce za ta zama taku, alhali kuwa Allah Yana nufin Ya tabbatar da gaskiya da kalmominsa, Ya kuma tumvuke tushen kafirai


1- Watau ko dai su yi nasarar rutsawa da kayan ayarin fataken Quraishawa, ko kuma su haxu da rundunar mayaqan Makka.


Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 8

لِيُحِقَّ ٱلۡحَقَّ وَيُبۡطِلَ ٱلۡبَٰطِلَ وَلَوۡ كَرِهَ ٱلۡمُجۡرِمُونَ

Don (kuma) Ya tabbatar da gaskiya, Ya kuma lalata varna ko da kuwa kafirai sun qi (hakan)



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 9

إِذۡ تَسۡتَغِيثُونَ رَبَّكُمۡ فَٱسۡتَجَابَ لَكُمۡ أَنِّي مُمِدُّكُم بِأَلۡفٖ مِّنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ مُرۡدِفِينَ

Ku tuna lokacin da kuke neman taimakon Ubangijinku, sai Ya amsa muku cewa: “Ni zan kawo muku xauki na mala’iku dubu masu bibiyar juna.”



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 10

وَمَا جَعَلَهُ ٱللَّهُ إِلَّا بُشۡرَىٰ وَلِتَطۡمَئِنَّ بِهِۦ قُلُوبُكُمۡۚ وَمَا ٱلنَّصۡرُ إِلَّا مِنۡ عِندِ ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَزِيزٌ حَكِيمٌ

Kuma (wannan taimakon) Allah bai sanya shi ba, sai don albishir a gare ku, don kuma zukatanku su nutsu da shi. Babu kuma wata nasara sai daga wurin Allah. Lalle Allah Mabuwayi ne Mai hikima



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 11

إِذۡ يُغَشِّيكُمُ ٱلنُّعَاسَ أَمَنَةٗ مِّنۡهُ وَيُنَزِّلُ عَلَيۡكُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ لِّيُطَهِّرَكُم بِهِۦ وَيُذۡهِبَ عَنكُمۡ رِجۡزَ ٱلشَّيۡطَٰنِ وَلِيَرۡبِطَ عَلَىٰ قُلُوبِكُمۡ وَيُثَبِّتَ بِهِ ٱلۡأَقۡدَامَ

(Ku kuma tuna) lokacin da gyangyaxi yake kwashe ku (Allah) Yana Mai amintar da ku (daga tunanin abokan gaba), Ya kuma riqa saukar da ruwa daga sama don Ya tsarkake ku da shi, Ya kuma tafiyar muku da waswasin shaixan, don kuma Ya qarfafa zukatanku Ya kuma tabbatar da dugaduganku da shi



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 12

إِذۡ يُوحِي رَبُّكَ إِلَى ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ أَنِّي مَعَكُمۡ فَثَبِّتُواْ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْۚ سَأُلۡقِي فِي قُلُوبِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلرُّعۡبَ فَٱضۡرِبُواْ فَوۡقَ ٱلۡأَعۡنَاقِ وَٱضۡرِبُواْ مِنۡهُمۡ كُلَّ بَنَانٖ

(Ka kuma tuna) lokacin da Ubangijinka Yake wahayi zuwa ga mala’iku cewa: “Lalle Ni ina tare da ku, saboda haka ku qarfafa wa waxanda suka yi imani gwiwa. Da sannu zan jefa tsoro cikin zukatan waxanda suka kafirce, saboda haka ku doki wuyansu, kuma ku doki dukkanin gavovin hannaye da qafafu.”



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 13

ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ شَآقُّواْ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥۚ وَمَن يُشَاقِقِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ فَإِنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Wannan kuwa saboda sun sava wa Allah da Manzonsa. Duk wanda kuwa ya sava wa Allah da Manzonsa to lalle Allah Mai tsananin uquba ne



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 14

ذَٰلِكُمۡ فَذُوقُوهُ وَأَنَّ لِلۡكَٰفِرِينَ عَذَابَ ٱلنَّارِ

Wannan (uqubar) sai ku xanxane ta (a duniya), kuma ba shakka kafirai suna da azabar wuta



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 15

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِذَا لَقِيتُمُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ زَحۡفٗا فَلَا تُوَلُّوهُمُ ٱلۡأَدۡبَارَ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka haxu da cincirindon waxanda suka kafirta, to kada ku ba su baya



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 16

وَمَن يُوَلِّهِمۡ يَوۡمَئِذٖ دُبُرَهُۥٓ إِلَّا مُتَحَرِّفٗا لِّقِتَالٍ أَوۡ مُتَحَيِّزًا إِلَىٰ فِئَةٖ فَقَدۡ بَآءَ بِغَضَبٖ مِّنَ ٱللَّهِ وَمَأۡوَىٰهُ جَهَنَّمُۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Duk kuwa wanda ya ba su baya a wannan ranar idan dai ba wanda ya gudu da niyyar juyowa ya kai xauki ko kuma mai niyyar haxuwa da wata jama’a (ta mayaqa) ba, to haqiqa ya komo da fushin Allah, kuma makomarsa Jahannama ce; wannan makoma kuwa ta munana



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 17

فَلَمۡ تَقۡتُلُوهُمۡ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ قَتَلَهُمۡۚ وَمَا رَمَيۡتَ إِذۡ رَمَيۡتَ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ رَمَىٰ وَلِيُبۡلِيَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ مِنۡهُ بَلَآءً حَسَنًاۚ إِنَّ ٱللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٞ

Saboda haka ba ku kuka kashe su ba, Allah ne Ya kashe su[1]. Kuma ba ka jefa ba lokacin da ka jefa, sai dai Allah ne Ya jefa[2]. Don kuma Ya jarrabi muminai da kyakkyawar jarrabawa[3]. Lalle Allah Mai ji ne Masani


1- Domin komai ya faru ne da taimakonsa da agajinsa.


2- Watau shi ma Annabi () da ya xauki qasa da tafin hannunsa ya watsa ta a fuskokin kafirai ta kuma cika musu ido, to a haqiqa ba shi ne ya yi wannan jifan ba, Allah ne ya yi.


3- Domin su yi masa godiya a kan ni’imominsa.


Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 18

ذَٰلِكُمۡ وَأَنَّ ٱللَّهَ مُوهِنُ كَيۡدِ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Waccan (jarraba ku da aka yi gaskiya ne), kuma lalle Allah Mai raunana makircin kafirai ne



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 19

إِن تَسۡتَفۡتِحُواْ فَقَدۡ جَآءَكُمُ ٱلۡفَتۡحُۖ وَإِن تَنتَهُواْ فَهُوَ خَيۡرٞ لَّكُمۡۖ وَإِن تَعُودُواْ نَعُدۡ وَلَن تُغۡنِيَ عَنكُمۡ فِئَتُكُمۡ شَيۡـٔٗا وَلَوۡ كَثُرَتۡ وَأَنَّ ٱللَّهَ مَعَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Idan kuna neman zuwan hukunci ne (watau azaba), to haqiqa hukuncin ya zo muku. Idan kuka daina to shi ya fi muku alheri, idan kuma kuka koma, to za Mu koma, jama’arku kuma ba za ta amfana muku komai ba, komai yawanta kuwa, lalle kuma Allah Yana tare da muminai



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 20

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ وَلَا تَوَلَّوۡاْ عَنۡهُ وَأَنتُمۡ تَسۡمَعُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku bi Allah da Manzonsa kada kuma ku ba shi baya alhali kuwa kuna ji



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 21

وَلَا تَكُونُواْ كَٱلَّذِينَ قَالُواْ سَمِعۡنَا وَهُمۡ لَا يَسۡمَعُونَ

Kada kuma ku zama kamar waxanda suka ce: “Mun ji,” alhalin kuwa su ba sa ji



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 22

۞إِنَّ شَرَّ ٱلدَّوَآبِّ عِندَ ٱللَّهِ ٱلصُّمُّ ٱلۡبُكۡمُ ٱلَّذِينَ لَا يَعۡقِلُونَ

Lalle mafi sharrin masu tafiya a bayan qasa a wurin Allah (su ne) kurame (ga jin gaskiya) bebaye (ga faxar gaskiya) waxanda ba sa hankalta



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 23

وَلَوۡ عَلِمَ ٱللَّهُ فِيهِمۡ خَيۡرٗا لَّأَسۡمَعَهُمۡۖ وَلَوۡ أَسۡمَعَهُمۡ لَتَوَلَّواْ وَّهُم مُّعۡرِضُونَ

Da Allah Ya san da akwai wani alheri a tare da su, to da Ya jiyar da su (gaskiya); da kuma Ya jiyar da su xin ma, to da kuwa sun ba da baya suna masu bijirewa



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 24

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱسۡتَجِيبُواْ لِلَّهِ وَلِلرَّسُولِ إِذَا دَعَاكُمۡ لِمَا يُحۡيِيكُمۡۖ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ يَحُولُ بَيۡنَ ٱلۡمَرۡءِ وَقَلۡبِهِۦ وَأَنَّهُۥٓ إِلَيۡهِ تُحۡشَرُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku amsa kiran Allah da na Manzo idan ya yi kiran ku ga abin da zai raya ku; kuma ku sani cewa, lalle Allah Yana kange tsakanin mutum da zuciyarsa, kuma lalle wurinsa ne za a tattara ku