Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 1

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡبُرُوجِ

Na rantse da sama ma’abociyar manziloli[1]


1- Watau manziloli na rana da wata da taurari.


Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 2

وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡمَوۡعُودِ

Da ranar da aka yi alqawarin zuwanta[1]


1- Watau ranar alqiyama.


Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 3

وَشَاهِدٖ وَمَشۡهُودٖ

Da mai shaida[1] da kuma abin yi wa shaida


1- Watau kamar Annabi da zai ba da shaida game da al’ummarsa.


Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 4

قُتِلَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡأُخۡدُودِ

An la’anci ma’abota rami (na azabtar da muminai)[1]


1- Wani azzalumin sarki ne da aka yi a Najrana ta qasar Yaman kafin aiko Annabi () wanda aka haqa masa rami aka hura wuta, ya riqa jefa muminai a cikinsa yana qona su da ransu.


Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 5

ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلۡوَقُودِ

Na wuta mai ruruwa



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 6

إِذۡ هُمۡ عَلَيۡهَا قُعُودٞ

Yayin da suke zaune a gefenta



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 7

وَهُمۡ عَلَىٰ مَا يَفۡعَلُونَ بِٱلۡمُؤۡمِنِينَ شُهُودٞ

Alhali su suna kallon abin da suke aikata wa muminai



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 8

وَمَا نَقَمُواْ مِنۡهُمۡ إِلَّآ أَن يُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

Babu kuwa abin da suke tuhumar su da shi sai don kawai sun yi imani da Allah Mabuwayi, Sha-yabo



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 9

ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Wanda Yake da mulkin sammai da qasa. Allah kuma Mai ganin komai ne



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُواْ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ ثُمَّ لَمۡ يَتُوبُواْ فَلَهُمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمۡ عَذَابُ ٱلۡحَرِيقِ

Lalle waxanda suka azabtar da muminai maza da muminai mata sannan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, suna kuma da azabar quna



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 11

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡكَبِيرُ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Wannan kuwa shi ne babban rabo



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 12

إِنَّ بَطۡشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ

Lalle damqar Ubangijinka tabbas mai tsanani ce



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 13

إِنَّهُۥ هُوَ يُبۡدِئُ وَيُعِيدُ

Lalle Shi ne Yake farar (da komai) Yake kuma dawo (da shi)



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 14

وَهُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلۡوَدُودُ

Shi ne kuma Mai gafara, Mai qaunar (bayinsa na qwarai)



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 15

ذُو ٱلۡعَرۡشِ ٱلۡمَجِيدُ

Ma’abocin Al’arshi Mai girma



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 16

فَعَّالٞ لِّمَا يُرِيدُ

Mai aikata abin da Yake nufi



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 17

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلۡجُنُودِ

Shin labarin rundunoni ya zo maka?



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 18

فِرۡعَوۡنَ وَثَمُودَ

(Su ne) Fir’auna da Samudawa



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 19

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي تَكۡذِيبٖ

A’a, su dai waxanda suka kafirta suna cikin qaryatawa ne



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 20

وَٱللَّهُ مِن وَرَآئِهِم مُّحِيطُۢ

Allah kuwa Yana kewaye da su (da iliminsa)



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 21

بَلۡ هُوَ قُرۡءَانٞ مَّجِيدٞ

A’a, shi dai Alqur’ani ne mai girma



Capítulo: Suratul Buruj

Verso : 22

فِي لَوۡحٖ مَّحۡفُوظِۭ

A cikin Lauhul-Mahafuzu