Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 1

سَأَلَ سَآئِلُۢ بِعَذَابٖ وَاقِعٖ

Mai tambaya ya yi tambaya game da wata azaba mai aukuwa[1]


1- Watau wadda Annabi () yake musu kashedi da ita idan sun qi imani. Duba Suratul Anfal, aya ta 32. Mai tambayar kuwa shi ne Nadhru xan Haris.


Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 2

لِّلۡكَٰفِرِينَ لَيۡسَ لَهُۥ دَافِعٞ

Ga kafirai (wadda) ba ta da wani mai kaxe ta



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 3

مِّنَ ٱللَّهِ ذِي ٱلۡمَعَارِجِ

Daga Allah Mai matattakalai



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 4

تَعۡرُجُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيۡهِ فِي يَوۡمٖ كَانَ مِقۡدَارُهُۥ خَمۡسِينَ أَلۡفَ سَنَةٖ

Mala’iku tare da Jibrilu suna hawa zuwa gare Shi a cikin wata rana (wadda) gwargwadonta yake daidai da shekara dubu hamsin



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 5

فَٱصۡبِرۡ صَبۡرٗا جَمِيلًا

Sai ka yi haquri kyakkyawan haquri



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 6

إِنَّهُمۡ يَرَوۡنَهُۥ بَعِيدٗا

Lalle su suna ganin ta mai nisa ce



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 7

وَنَرَىٰهُ قَرِيبٗا

Mu kuma Muna ganin ta kusa-kusa



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 8

يَوۡمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلۡمُهۡلِ

A ranar da sama za ta kasance kamar narkakkiyar dalma



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 9

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga (ta gashin tumaki)



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 10

وَلَا يَسۡـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمٗا

Kuma aboki ba ya tambayar aboki



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 11

يُبَصَّرُونَهُمۡۚ يَوَدُّ ٱلۡمُجۡرِمُ لَوۡ يَفۡتَدِي مِنۡ عَذَابِ يَوۡمِئِذِۭ بِبَنِيهِ

(Alhali kuma) ana nuna musu junansu. Mai laifi ya riqa burin ina ma zai fanshi kansa daga azabar wannan rana da ‘ya’yansa



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 12

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

Da matarsa da xan’uwansa



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 13

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِي تُـٔۡوِيهِ

Da danginsa waxanda suke kare shi



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 14

وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ يُنجِيهِ

Da ma duk wanda yake a bayan qasa baki xaya, sannan (fansar) ta tserar da shi



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 17

تَدۡعُواْ مَنۡ أَدۡبَرَ وَتَوَلَّىٰ

Tana kiran wanda ya juya ya ba da baya



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 18

وَجَمَعَ فَأَوۡعَىٰٓ

Ya kuma tara (dukiya) sai ya voye (ta)



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 19

۞إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا

Lalle mutum an halicce shi mai rashin nutsuwa ne



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 20

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعٗا

(Watau) idan sharri ya same shi ya zama mai raki



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 21

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلۡخَيۡرُ مَنُوعًا

Idan kuma alheri ya same shi ya zama mai maqo



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 22

إِلَّا ٱلۡمُصَلِّينَ

Sai dai masallata



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 23

ٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ دَآئِمُونَ

Waxanda suke masu dawwama a kan sallarsu



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 24

وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ

Waxanda kuma suke akwai haqqi sananne a cikin dukiyoyinsu



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 25

لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

Ga mai roqo da wanda ake hana wa (saboda ba ya roqo)



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 26

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

Waxanda kuma suke gaskata ranar sakamako



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 27

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ

Waxanda kuma suke tsoron azabar Ubangijinsu



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 28

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمۡ غَيۡرُ مَأۡمُونٖ

Lalle azabar Ubangijinsu ba abar amincewa ba ce



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 29

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye al’aurarsu (daga yin zina)



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ

Sai a wajan matayensu ko kuma qwarqarorinsu; to su a nan ba ababen zargi ba ne