Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 1

سَبَّحَ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Abin da yake cikin sammai da qasa ya yi tasbihi ga Allah; Shi ne kuma Mabuwayi, Mai hikima



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 2

لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ يُحۡيِۦ وَيُمِيتُۖ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ

Mulkin sammai da qasa nasa ne; Yana rayawa, Yana kuma kashewa; kuma Shi Mai iko ne a kan komai



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 3

هُوَ ٱلۡأَوَّلُ وَٱلۡأٓخِرُ وَٱلظَّـٰهِرُ وَٱلۡبَاطِنُۖ وَهُوَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٌ

Shi ne Na farko kuma Na qarshe, kuma Bayyananne kuma Voyayye[1]; Shi kuma Masanin komai ne


1- Na farko, watau babu wani abu gabaninsa. Na qarshe, watau babu wani abu bayansa. Bayyananne, watau babu wani abu sama da shi. Voyayye, watau babu wani abu da ya fi shi vuya.


Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 4

هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰ عَلَى ٱلۡعَرۡشِۖ يَعۡلَمُ مَا يَلِجُ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا يَخۡرُجُ مِنۡهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ وَمَا يَعۡرُجُ فِيهَاۖ وَهُوَ مَعَكُمۡ أَيۡنَ مَا كُنتُمۡۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

Shi ne wanda Ya halicci sammai da qasa cikin kwana shida, sannan Ya daidaitu a kan Al’arshi. Yana sane da abin da yake shiga cikin qasa da abin da yake fitowa daga cikinta, da kuma abin da yake saukowa daga sama da abin da yake hawa cikinta; kuma Shi Yana tare da ku a duk inda kuka kasance[1]. Allah kuwa Mai ganin duk abin da kuke aikatawa ne


1- Watau da iliminsa. Babu wani abu da yake vuya a gare shi, yana kuma ganin duk abin da suke aikatawa.


Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 5

لَّهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَإِلَى ٱللَّهِ تُرۡجَعُ ٱلۡأُمُورُ

Mulkin sammai da qasa nasa ne. Kuma ga Allah ake mayar da al’amura



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 6

يُولِجُ ٱلَّيۡلَ فِي ٱلنَّهَارِ وَيُولِجُ ٱلنَّهَارَ فِي ٱلَّيۡلِۚ وَهُوَ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

Yana shigar da dare cikin rana, Yana kuma shigar da rana cikin dare. Kuma Shi Masanin abubuwan da suke cikin qiraza ne



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 7

ءَامِنُواْ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَأَنفِقُواْ مِمَّا جَعَلَكُم مُّسۡتَخۡلَفِينَ فِيهِۖ فَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مِنكُمۡ وَأَنفَقُواْ لَهُمۡ أَجۡرٞ كَبِيرٞ

Ku yi imani da Allah da kuma Manzonsa, ku kuma ciyar daga abin da ya sanya ku wakilai a kansa, to waxanda suka yi imani daga cikinku, suka kuma ciyar suna da lada mai girma



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 8

وَمَا لَكُمۡ لَا تُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلرَّسُولُ يَدۡعُوكُمۡ لِتُؤۡمِنُواْ بِرَبِّكُمۡ وَقَدۡ أَخَذَ مِيثَٰقَكُمۡ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Kuma me ya same ku ne ba kwa yin imani da Allah, alhali kuwa Manzo yana kiran ku don ku yi imani da Ubangijinku, haqiqa kuma kun yi masa alqawari, in dai kun kasance muminai



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 9

هُوَ ٱلَّذِي يُنَزِّلُ عَلَىٰ عَبۡدِهِۦٓ ءَايَٰتِۭ بَيِّنَٰتٖ لِّيُخۡرِجَكُم مِّنَ ٱلظُّلُمَٰتِ إِلَى ٱلنُّورِۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ بِكُمۡ لَرَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Shi ne Wanda Yake saukar da ayoyi bayyanannu ga Bawansa don Ya fitar da ku daga duffai zuwa haske. Kuma lalle Allah Mai tausayi ne, Mai rahama a gare ku



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 10

وَمَا لَكُمۡ أَلَّا تُنفِقُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَلِلَّهِ مِيرَٰثُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ لَا يَسۡتَوِي مِنكُم مَّنۡ أَنفَقَ مِن قَبۡلِ ٱلۡفَتۡحِ وَقَٰتَلَۚ أُوْلَـٰٓئِكَ أَعۡظَمُ دَرَجَةٗ مِّنَ ٱلَّذِينَ أَنفَقُواْ مِنۢ بَعۡدُ وَقَٰتَلُواْۚ وَكُلّٗا وَعَدَ ٱللَّهُ ٱلۡحُسۡنَىٰۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٞ

Kuma me ya same ku ne da ba za ku ciyar saboda Allah ba, alhali kuwa gadon sammai da qasa na Allah ne? Wanda ya ciyar daga cikinku tun kafin buxe (Makka)[1] ya kuma yi yaqi, ba zai zama daidai (da wanda bai yi) ba. Waxannan su suka fi girman daraja a kan waxanda suka ciyar daga bisani, suka kuma yi yaqi. Amma kuma kowannensu Allah Ya yi masa alqawarin Aljanna. Allah kuma Masanin abin da kuke aikatawa ne


1- Wasu daga cikin malamai sun fassara Fat’hu a wannan ayar da cewa ana nufin Sulhul Hudaibiyya.


Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 11

مَّن ذَا ٱلَّذِي يُقۡرِضُ ٱللَّهَ قَرۡضًا حَسَنٗا فَيُضَٰعِفَهُۥ لَهُۥ وَلَهُۥٓ أَجۡرٞ كَرِيمٞ

Wane ne wanda zai bai wa Allah rance kyakkyawan rance, sai Ya ninka masa shi, alhali yana kuma da lada mai girma?



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 12

يَوۡمَ تَرَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ يَسۡعَىٰ نُورُهُم بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَبِأَيۡمَٰنِهِمۖ بُشۡرَىٰكُمُ ٱلۡيَوۡمَ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

(Ka tuna) ranar da za ka ga muminai maza da muminai mata haskensu yana tafiya ta gabansu da ta damansu, (ana cewa da su): “Albishirinku a wannan rana (su ne) gidajen Aljanna da qoramu suke gudana ta qarqashinsu, kuna masu dawwama a cikinsu. Wannan shi ne rabo mai girma.”



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 13

يَوۡمَ يَقُولُ ٱلۡمُنَٰفِقُونَ وَٱلۡمُنَٰفِقَٰتُ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱنظُرُونَا نَقۡتَبِسۡ مِن نُّورِكُمۡ قِيلَ ٱرۡجِعُواْ وَرَآءَكُمۡ فَٱلۡتَمِسُواْ نُورٗاۖ فَضُرِبَ بَيۡنَهُم بِسُورٖ لَّهُۥ بَابُۢ بَاطِنُهُۥ فِيهِ ٱلرَّحۡمَةُ وَظَٰهِرُهُۥ مِن قِبَلِهِ ٱلۡعَذَابُ

A ranar da munafukai maza da munafukai mata za su riqa cewa da waxanda suka yi imani: “Ku saurara mana mu xan xosani haskenku.” Aka ce (da su): “Ku koma bayanku (watau duniya) sai ku nemi haske.” sai aka raba tsakaninsu da katanga wadda take da wata qofa, daga cikinta akwai rahama, bayanta kuma azaba ce (take bugowa) daga gare ta



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 14

يُنَادُونَهُمۡ أَلَمۡ نَكُن مَّعَكُمۡۖ قَالُواْ بَلَىٰ وَلَٰكِنَّكُمۡ فَتَنتُمۡ أَنفُسَكُمۡ وَتَرَبَّصۡتُمۡ وَٱرۡتَبۡتُمۡ وَغَرَّتۡكُمُ ٱلۡأَمَانِيُّ حَتَّىٰ جَآءَ أَمۡرُ ٱللَّهِ وَغَرَّكُم بِٱللَّهِ ٱلۡغَرُورُ

(Munafukan) suna kiran su cewa: “Yanzu ba mu kasance a tare da ku ba ne?” Suka ce: “Haka ne, sai dai ku kuma kun fitini kanku (da munafunci) kuka kuma saurari (aukuwar mummunan abu ga muminai), kuka kuma yi shakka (game da addini), burace-burace kuma suka ruxe ku har mutuwa ta zo, Shaixan kuma ya ruxe ku game da Allah



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 15

فَٱلۡيَوۡمَ لَا يُؤۡخَذُ مِنكُمۡ فِدۡيَةٞ وَلَا مِنَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۚ مَأۡوَىٰكُمُ ٱلنَّارُۖ هِيَ مَوۡلَىٰكُمۡۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

“To a yau ba za a karvi wata fansa ba daga gare ku da kuma daga waxanda suka kafirta. Makomarku wuta; ita ce ta kamace ku, makoma kuwa ta munana.”



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 16

۞أَلَمۡ يَأۡنِ لِلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَن تَخۡشَعَ قُلُوبُهُمۡ لِذِكۡرِ ٱللَّهِ وَمَا نَزَلَ مِنَ ٱلۡحَقِّ وَلَا يَكُونُواْ كَٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ مِن قَبۡلُ فَطَالَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡأَمَدُ فَقَسَتۡ قُلُوبُهُمۡۖ وَكَثِيرٞ مِّنۡهُمۡ فَٰسِقُونَ

Yanzu lokaci bai yi ba ga waxanda suka yi imani zukatansu su yi taushi da zikirin Allah da kuma abin da Ya saukar na gaskiya, kuma kada su zama kamar waxanda aka bai wa Littafi tun gabaninsu, sai lokaci ya tsawaita a gare su, sai zukatansu suka qeqashe; mafiya yawa kuma daga cikinsu fasiqai ne?



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 17

ٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ يُحۡيِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَاۚ قَدۡ بَيَّنَّا لَكُمُ ٱلۡأٓيَٰتِ لَعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Ku sani cewa Allah Yana raya qasa bayan mutuwarta[1]. Haqiqa Mun bayyana muku ayoyi don ku hankalta


1- Watau hakanan Alqur’ani yake raya zukata bayan sun qeqashe.


Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 18

إِنَّ ٱلۡمُصَّدِّقِينَ وَٱلۡمُصَّدِّقَٰتِ وَأَقۡرَضُواْ ٱللَّهَ قَرۡضًا حَسَنٗا يُضَٰعَفُ لَهُمۡ وَلَهُمۡ أَجۡرٞ كَرِيمٞ

Lalle masu yin sadaka maza da masu yin sadaka mata, suka kuma bai wa Allah kyakkyawan rance, to za a ninninka musu shi, suna kuma da wani ladan mai daraja



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 19

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦٓ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلصِّدِّيقُونَۖ وَٱلشُّهَدَآءُ عِندَ رَبِّهِمۡ لَهُمۡ أَجۡرُهُمۡ وَنُورُهُمۡۖ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَكَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَآ أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡجَحِيمِ

Waxanda kuma suka yi imani da Allah da manzanninsa, waxannan su ne siddiqai; shahidai kuma suna da ladansu da haskensu a wurin Ubangijinsu; waxanda kuwa suka kafirta suke kuma qaryata ayoyinmu, to waxannan su ne ‘yan (wutar) Jahimu



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 20

ٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّمَا ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا لَعِبٞ وَلَهۡوٞ وَزِينَةٞ وَتَفَاخُرُۢ بَيۡنَكُمۡ وَتَكَاثُرٞ فِي ٱلۡأَمۡوَٰلِ وَٱلۡأَوۡلَٰدِۖ كَمَثَلِ غَيۡثٍ أَعۡجَبَ ٱلۡكُفَّارَ نَبَاتُهُۥ ثُمَّ يَهِيجُ فَتَرَىٰهُ مُصۡفَرّٗا ثُمَّ يَكُونُ حُطَٰمٗاۖ وَفِي ٱلۡأٓخِرَةِ عَذَابٞ شَدِيدٞ وَمَغۡفِرَةٞ مِّنَ ٱللَّهِ وَرِضۡوَٰنٞۚ وَمَا ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَآ إِلَّا مَتَٰعُ ٱلۡغُرُورِ

Ku sani cewa, ita dai rayuwar duniya ba wata aba ba ce sai wasa da sharholiya da qyale-qyale da kuma fariya a tsakaninku da takara wajan nuna yawan dukiya da ‘ya’yaye; ta yi kama da ruwan saman da tsirransa suka bai wa manoma sha’awa, sannan duk ya bushe, sai ka gan shi fatsi-fatsi, sannan kuma ya zama dudduga; a lahira kuwa akwai azaba mai tsanani da gafara daga Allah da kuma yarda. Rayuwar duniya ba komai ba ce sai jin daxi mai ruxi



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 21

سَابِقُوٓاْ إِلَىٰ مَغۡفِرَةٖ مِّن رَّبِّكُمۡ وَجَنَّةٍ عَرۡضُهَا كَعَرۡضِ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ أُعِدَّتۡ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦۚ ذَٰلِكَ فَضۡلُ ٱللَّهِ يُؤۡتِيهِ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ

Ku yi rige-rige zuwa neman gafara daga Ubangijinku da Aljanna wadda faxinta kamar faxin sammai da qasa yake, an tanade ta don waxanda suka yi imani da Allah da manzanninsa. Wannan falalar Allah ce da Yake ba da ita ga wanda Ya ga dama. Allah kuwa Ma’abocin falala ne, Mai girma



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 22

مَآ أَصَابَ مِن مُّصِيبَةٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا فِيٓ أَنفُسِكُمۡ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مِّن قَبۡلِ أَن نَّبۡرَأَهَآۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٞ

Babu wani abu da ya samu na musiba a bayan qasa, ko kuma ga kawunanku face yana cikin Littafin (Lauhul Mahafuzu) tun kafin Mu halicce ta (watau halittar). Lalle wannan (a wurin Allah) mai sauqi ne



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 23

لِّكَيۡلَا تَأۡسَوۡاْ عَلَىٰ مَا فَاتَكُمۡ وَلَا تَفۡرَحُواْ بِمَآ ءَاتَىٰكُمۡۗ وَٱللَّهُ لَا يُحِبُّ كُلَّ مُخۡتَالٖ فَخُورٍ

Don kada ku yi baqin ciki a kan abin da ya kuvuce muku, kada kuma ku yi fariya da abin da Ya ba ku, Allah kuwa ba Ya son duk wani mai taqama, mai fariya



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 24

ٱلَّذِينَ يَبۡخَلُونَ وَيَأۡمُرُونَ ٱلنَّاسَ بِٱلۡبُخۡلِۗ وَمَن يَتَوَلَّ فَإِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡغَنِيُّ ٱلۡحَمِيدُ

(Su ne) waxanda suke yin rowa, suke kuma umartar mutane da yin rowar. Wanda kuwa ya ba da baya, to lalle Allah Shi Mawadaci ne, Sha-Yabo



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 25

لَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا رُسُلَنَا بِٱلۡبَيِّنَٰتِ وَأَنزَلۡنَا مَعَهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمِيزَانَ لِيَقُومَ ٱلنَّاسُ بِٱلۡقِسۡطِۖ وَأَنزَلۡنَا ٱلۡحَدِيدَ فِيهِ بَأۡسٞ شَدِيدٞ وَمَنَٰفِعُ لِلنَّاسِ وَلِيَعۡلَمَ ٱللَّهُ مَن يَنصُرُهُۥ وَرُسُلَهُۥ بِٱلۡغَيۡبِۚ إِنَّ ٱللَّهَ قَوِيٌّ عَزِيزٞ

Haqiqa Mun aiko manzanninmu da (ayoyi) mabayyana, Muka kuma saukar da littafi da ma’auni a tare da su (manzannin) don mutane su tsaya da adalci; Muka kuma saukar da baqin qarfe wanda a tare da shi akwai tsananin qarfi da kuma amfani ga mutane, don kuma Allah Ya bayyanar da wanda yake taimakon Sa da manzanninsa a voye. Lalle Allah Mai qarfi ne, Mabuwayi



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 26

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا نُوحٗا وَإِبۡرَٰهِيمَ وَجَعَلۡنَا فِي ذُرِّيَّتِهِمَا ٱلنُّبُوَّةَ وَٱلۡكِتَٰبَۖ فَمِنۡهُم مُّهۡتَدٖۖ وَكَثِيرٞ مِّنۡهُمۡ فَٰسِقُونَ

Haqiqa kuma Mun aiko Nuhu da Ibrahimu, Muka kuma sanya annabta da littafi cikin zuriyarsu; To daga cikinsu akwai shiryayyu, masu yawa kuwa daga cikinsu fasiqai ne



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 27

ثُمَّ قَفَّيۡنَا عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِم بِرُسُلِنَا وَقَفَّيۡنَا بِعِيسَى ٱبۡنِ مَرۡيَمَ وَءَاتَيۡنَٰهُ ٱلۡإِنجِيلَۖ وَجَعَلۡنَا فِي قُلُوبِ ٱلَّذِينَ ٱتَّبَعُوهُ رَأۡفَةٗ وَرَحۡمَةٗۚ وَرَهۡبَانِيَّةً ٱبۡتَدَعُوهَا مَا كَتَبۡنَٰهَا عَلَيۡهِمۡ إِلَّا ٱبۡتِغَآءَ رِضۡوَٰنِ ٱللَّهِ فَمَا رَعَوۡهَا حَقَّ رِعَايَتِهَاۖ فَـَٔاتَيۡنَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مِنۡهُمۡ أَجۡرَهُمۡۖ وَكَثِيرٞ مِّنۡهُمۡ فَٰسِقُونَ

Sannan a bayansu Muka biyar da manzanninmu, Muka kuma biyar da Isa xan Maryamu Muka kuma ba shi Linjila, kuma Muka sanya jin qai da rahama a cikin zukatan waxanda suka bi shi. Rahbaniyanci[1] kuma su ne suka qago shi, ba Mu wajabta musu shi ba, sai dai (Mun wajabta musu) neman yardar Allah, amma ba su kiyaye shi ba kamar yadda ya kamata; sai Muka bai wa waxanda suka yi imani daga cikinsu ladansu; da yawa kuwa fasiqai ne


1- Bidi’ar Rahbaniyanci ita ce, qaurace wa aure da barin cin daxaxan abubuwa na halal da haramta wa kai wasu abubuwa da Allah ya halatta.


Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 28

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَءَامِنُواْ بِرَسُولِهِۦ يُؤۡتِكُمۡ كِفۡلَيۡنِ مِن رَّحۡمَتِهِۦ وَيَجۡعَل لَّكُمۡ نُورٗا تَمۡشُونَ بِهِۦ وَيَغۡفِرۡ لَكُمۡۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ya ku waxanda suka imani, ku kiyaye dokokin Allah, ku kuma yi imani da Manzonsa, zai ba ku rivi biyu na rahamarsa, Ya kuma sanya muku haske da za ku riqa tafiya da shi, kuma Ya gafarta muku. Domin kuwa Allah Mai gafara ne, Mai rahama



Capítulo: Suratul Hadid

Verso : 29

لِّئَلَّا يَعۡلَمَ أَهۡلُ ٱلۡكِتَٰبِ أَلَّا يَقۡدِرُونَ عَلَىٰ شَيۡءٖ مِّن فَضۡلِ ٱللَّهِ وَأَنَّ ٱلۡفَضۡلَ بِيَدِ ٱللَّهِ يُؤۡتِيهِ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ

Don ma’abota littafi su san cewa ba su da hannu a falalar Allah, don ko lalle falala a hannun Allah take, Yana ba da ita ga wanda Ya ga dama. Allah kuma Ma’abocin babbar falala ne