Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ ٱتَّقِ ٱللَّهَ وَلَا تُطِعِ ٱلۡكَٰفِرِينَ وَٱلۡمُنَٰفِقِينَۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Ya kai wannan Annabi, ka kiyaye dokokin Allah, kada ka yi wa kafirai da munafukai xa’a. Lalle Allah Ya kasance Masani ne, Mai hikima



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 2

وَٱتَّبِعۡ مَا يُوحَىٰٓ إِلَيۡكَ مِن رَّبِّكَۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٗا

Kuma ka bi abin da ake yi maka wahayinsa daga Ubangijinka. Lalle Allah Ya kasance Masanin abin da kuke aikatawa ne



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 3

وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱللَّهِۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ وَكِيلٗا

Ka kuma dogara ga Allah. Allah kuwa Ya isa wakili



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 4

مَّا جَعَلَ ٱللَّهُ لِرَجُلٖ مِّن قَلۡبَيۡنِ فِي جَوۡفِهِۦۚ وَمَا جَعَلَ أَزۡوَٰجَكُمُ ٱلَّـٰٓـِٔي تُظَٰهِرُونَ مِنۡهُنَّ أُمَّهَٰتِكُمۡۚ وَمَا جَعَلَ أَدۡعِيَآءَكُمۡ أَبۡنَآءَكُمۡۚ ذَٰلِكُمۡ قَوۡلُكُم بِأَفۡوَٰهِكُمۡۖ وَٱللَّهُ يَقُولُ ٱلۡحَقَّ وَهُوَ يَهۡدِي ٱلسَّبِيلَ

Allah bai sanya wa wani mutum zuciya biyu ba a cikinsa. Kuma bai sanya matanku waxanda kuke yi musu zihari[1] (su zama) iyayenku ba. Bai kuma sanya ‘ya’yan riqonku (su zama) ‘ya’yanku ba[2]. Wannan magana ce da kuke yi da bakunanku; Allah kuwa Yana faxar gaskiya ne, kuma Shi ne Yake shiryarwa ga hanya (ta gaskiya)


1- Zihari, shi ne miji ya kwatanta matarsa da mahaifiyarsa wajen haramci. Wannan wata al’ada ce ta Larabawa a jahiliyya da Musulunci ya haramta ta.


2- Gabanin zuwa Musulunci Larabawa sukan mayar da ‘ya’yansu na riqo kamar ‘ya’yan da suka haifa wajen hukunce-hukunce. Sai Allah ya haramta aikata haka.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 5

ٱدۡعُوهُمۡ لِأٓبَآئِهِمۡ هُوَ أَقۡسَطُ عِندَ ٱللَّهِۚ فَإِن لَّمۡ تَعۡلَمُوٓاْ ءَابَآءَهُمۡ فَإِخۡوَٰنُكُمۡ فِي ٱلدِّينِ وَمَوَٰلِيكُمۡۚ وَلَيۡسَ عَلَيۡكُمۡ جُنَاحٞ فِيمَآ أَخۡطَأۡتُم بِهِۦ وَلَٰكِن مَّا تَعَمَّدَتۡ قُلُوبُكُمۡۚ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمًا

Ku danganta su (‘ya’yan riqo) ga iyayensu maza shi ne adalci a wurin Allah. Amma idan ba ku san iyayensu maza ba, to ‘yan’uwanku ne a addini, kuma bararrun bayinku ne. Babu kuma laifi a kanku game da abin da kuka yi kuskuren yin sa, sai dai abin da zukatanku suka yi gangancin (aikatawa). Allah kuwa Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 6

ٱلنَّبِيُّ أَوۡلَىٰ بِٱلۡمُؤۡمِنِينَ مِنۡ أَنفُسِهِمۡۖ وَأَزۡوَٰجُهُۥٓ أُمَّهَٰتُهُمۡۗ وَأُوْلُواْ ٱلۡأَرۡحَامِ بَعۡضُهُمۡ أَوۡلَىٰ بِبَعۡضٖ فِي كِتَٰبِ ٱللَّهِ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُهَٰجِرِينَ إِلَّآ أَن تَفۡعَلُوٓاْ إِلَىٰٓ أَوۡلِيَآئِكُم مَّعۡرُوفٗاۚ كَانَ ذَٰلِكَ فِي ٱلۡكِتَٰبِ مَسۡطُورٗا

Annabi shi ya fi cancanta ga muminai fiye da kansu[1]; matansa kuma iyayensu ne. Dangi na zumunta kuma shashinsu ya fi kusanci daga wani shashi[2] a cikin Littafin Allah daga kusancin muminai da masu hijira, sai dai idan za ku aikata wani alheri ne ga masoyanku (muminai). Wannan ya kasance a rubuce a cikin Lauhul Mahafuzu


1- Watau shi ya fi cancanta su qaunace shi fiye da kawunansu.


2- Watau dangi na zumunci su ne suka fi cancanta su ci gadon junansu.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 7

وَإِذۡ أَخَذۡنَا مِنَ ٱلنَّبِيِّـۧنَ مِيثَٰقَهُمۡ وَمِنكَ وَمِن نُّوحٖ وَإِبۡرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ وَعِيسَى ٱبۡنِ مَرۡيَمَۖ وَأَخَذۡنَا مِنۡهُم مِّيثَٰقًا غَلِيظٗا

Kuma (ka tuna) lokacin da Muka riqi alqawura daga annabawa (na isar da aike), kuma daga gare ka, kuma daga Nuhu da Ibrahimu da Musa da Isa xan Maryamu; Muka kuma riqi alqawari mai kauri daga gare su



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 8

لِّيَسۡـَٔلَ ٱلصَّـٰدِقِينَ عَن صِدۡقِهِمۡۚ وَأَعَدَّ لِلۡكَٰفِرِينَ عَذَابًا أَلِيمٗا

Don (Allah) Ya tambayi masu gaskiya game da gaskiyarsu[1], Ya kuma tanadi azaba mai raxaxi ga kafirai


1- Watau ya tambati annabawa ko sun isar da saqon da ya aiko su da shi.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 9

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَةَ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ إِذۡ جَآءَتۡكُمۡ جُنُودٞ فَأَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ رِيحٗا وَجُنُودٗا لَّمۡ تَرَوۡهَاۚ وَكَانَ ٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرًا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku tuna ni’imar Allah a gare ku lokacin da wasu rundunoni (na gangankon kafurai) suka zo muku, sai Muka aiko musu iska da wasu rundunoni da ba ku gan su ba[1]. Allah kuwa Ya kasance Mai ganin abin da kuke aikatawa ne


1- Watau su ne rundunonin kafiran Quraishawa da qawayensu waxanda suka nufo Madina a shekara ta 5 don su yaqi Musulmi, amma Allah ya karya su.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 10

إِذۡ جَآءُوكُم مِّن فَوۡقِكُمۡ وَمِنۡ أَسۡفَلَ مِنكُمۡ وَإِذۡ زَاغَتِ ٱلۡأَبۡصَٰرُ وَبَلَغَتِ ٱلۡقُلُوبُ ٱلۡحَنَاجِرَ وَتَظُنُّونَ بِٱللَّهِ ٱلظُّنُونَا۠

A lokacin da suka zo muku ta samanku da qasanku, da kuma yayin da idanuwa suka kauce wa (ganin komai sai maqiya), zukatanku kuma suka cika da tsoro kuka riqa zace-zace game da Allah



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 11

هُنَالِكَ ٱبۡتُلِيَ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَزُلۡزِلُواْ زِلۡزَالٗا شَدِيدٗا

A nan ne fa aka jarrabi muminai, aka kuma girgiza su girgizawa mai tsanani



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 12

وَإِذۡ يَقُولُ ٱلۡمُنَٰفِقُونَ وَٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ مَّا وَعَدَنَا ٱللَّهُ وَرَسُولُهُۥٓ إِلَّا غُرُورٗا

Kuma (ka tuna) lokacin da munafukai da waxanda suke da cuta a zukatansu suke cewa: “Allah da Manzonsa ba wani alqawarin da suka yi mana sai na ruxi.”



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 13

وَإِذۡ قَالَت طَّآئِفَةٞ مِّنۡهُمۡ يَـٰٓأَهۡلَ يَثۡرِبَ لَا مُقَامَ لَكُمۡ فَٱرۡجِعُواْۚ وَيَسۡتَـٔۡذِنُ فَرِيقٞ مِّنۡهُمُ ٱلنَّبِيَّ يَقُولُونَ إِنَّ بُيُوتَنَا عَوۡرَةٞ وَمَا هِيَ بِعَوۡرَةٍۖ إِن يُرِيدُونَ إِلَّا فِرَارٗا

Kuma (ka tuna) lokacin da wata jama’a daga cikinsu ta ce: “Ya ku mutanen Yasriba[1], ba ku da wurin zama, sai ku koma.” Wata qungiya kuma daga cikinsu tana neman izinin Annabi da cewa: “Lalle gidajenmu tsirara tuqwi suke,” alhali kuwa ba tsirara tuqwi suke ba; ba abin da suke nufi sai gudu


1- Yasrib, tsohon sunan Madina ne tun gabanin Musulunci. Annabi ya canja shi zuwa Madina.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 14

وَلَوۡ دُخِلَتۡ عَلَيۡهِم مِّنۡ أَقۡطَارِهَا ثُمَّ سُئِلُواْ ٱلۡفِتۡنَةَ لَأٓتَوۡهَا وَمَا تَلَبَّثُواْ بِهَآ إِلَّا يَسِيرٗا

Da kuwa za a shigo musu ta kowane vangare sannan a neme su da yin fitinar (komawa ga kafirci), to Wallahi da sun aikata (hakan) ba kuwa za su jinkirta da shi ba (wato kafircin) sai xan lokacin qanqani



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 15

وَلَقَدۡ كَانُواْ عَٰهَدُواْ ٱللَّهَ مِن قَبۡلُ لَا يُوَلُّونَ ٱلۡأَدۡبَٰرَۚ وَكَانَ عَهۡدُ ٱللَّهِ مَسۡـُٔولٗا

Tun da can kuwa haqiqa sun yi wa Allah alqawarin (cewa) ba za su ba da baya ba. Alqawarin Allah kuwa ya kasance abin tambaya ne



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 16

قُل لَّن يَنفَعَكُمُ ٱلۡفِرَارُ إِن فَرَرۡتُم مِّنَ ٱلۡمَوۡتِ أَوِ ٱلۡقَتۡلِ وَإِذٗا لَّا تُمَتَّعُونَ إِلَّا قَلِيلٗا

Ka ce: “In kuna guje wa mutuwa ne ko kisa, to gudun ba zai amfane ku ba, a yayin nan kuwa ba za a jiyar da ku wani daxi ba sai xan kaxan.”



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 17

قُلۡ مَن ذَا ٱلَّذِي يَعۡصِمُكُم مِّنَ ٱللَّهِ إِنۡ أَرَادَ بِكُمۡ سُوٓءًا أَوۡ أَرَادَ بِكُمۡ رَحۡمَةٗۚ وَلَا يَجِدُونَ لَهُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ وَلِيّٗا وَلَا نَصِيرٗا

Ka ce: “Wane ne zai kare ku daga Allah idan Ya nufe ku da wani mummunan abu ko kuma Ya nufe ku da wata rahama?” Ba kuma za su sama wa kansu wani majivinci ko mai taimako ba in ba Allah ba



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 18

۞قَدۡ يَعۡلَمُ ٱللَّهُ ٱلۡمُعَوِّقِينَ مِنكُمۡ وَٱلۡقَآئِلِينَ لِإِخۡوَٰنِهِمۡ هَلُمَّ إِلَيۡنَاۖ وَلَا يَأۡتُونَ ٱلۡبَأۡسَ إِلَّا قَلِيلًا

Haqiqa Allah Yana sane da masu hana ruwa gudu[1] daga cikinku, da masu ce wa ‘yan’uwansu: “Ku zo wurinmu,” kuma ba sa zuwa yaqi sai kaxan


1- Su ne munafukai masu daqile Musulmi da karya musu gwiwa wajen fita yaqi.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 19

أَشِحَّةً عَلَيۡكُمۡۖ فَإِذَا جَآءَ ٱلۡخَوۡفُ رَأَيۡتَهُمۡ يَنظُرُونَ إِلَيۡكَ تَدُورُ أَعۡيُنُهُمۡ كَٱلَّذِي يُغۡشَىٰ عَلَيۡهِ مِنَ ٱلۡمَوۡتِۖ فَإِذَا ذَهَبَ ٱلۡخَوۡفُ سَلَقُوكُم بِأَلۡسِنَةٍ حِدَادٍ أَشِحَّةً عَلَى ٱلۡخَيۡرِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ لَمۡ يُؤۡمِنُواْ فَأَحۡبَطَ ٱللَّهُ أَعۡمَٰلَهُمۡۚ وَكَانَ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٗا

(Su ne) masu yi muku rowar (taimako); sannan idan (abin) tsoro ya zo, sai ka gan su suna duban ka idanuwansu suna jujjuyawa kamar wanda yake suman mutuwa; sannan idan tsoron ya yaye, sai su riqa cutar da ku da harsuna kaifafa, suna masu rowar alheri. Waxannan ba su yi imani ba, don haka Allah Ya lalata ayyukansu. Wannan kuwa ya kasance abu ne mai sauqi a wurin Allah



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 20

يَحۡسَبُونَ ٱلۡأَحۡزَابَ لَمۡ يَذۡهَبُواْۖ وَإِن يَأۡتِ ٱلۡأَحۡزَابُ يَوَدُّواْ لَوۡ أَنَّهُم بَادُونَ فِي ٱلۡأَعۡرَابِ يَسۡـَٔلُونَ عَنۡ أَنۢبَآئِكُمۡۖ وَلَوۡ كَانُواْ فِيكُم مَّا قَٰتَلُوٓاْ إِلَّا قَلِيلٗا

Suna zaton rundunonin gangami ba su tafi ba; da a ce kuwa rundunonin na gangami za su sake dawowa to da sai su riqa burin ina ma suna can tare da mutanen qauye suna tambayar labaranku; ko ma da za su kasance a cikinku to da ba za su yi yaqi ba sai xan kaxan



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 21

لَّقَدۡ كَانَ لَكُمۡ فِي رَسُولِ ٱللَّهِ أُسۡوَةٌ حَسَنَةٞ لِّمَن كَانَ يَرۡجُواْ ٱللَّهَ وَٱلۡيَوۡمَ ٱلۡأٓخِرَ وَذَكَرَ ٱللَّهَ كَثِيرٗا

Haqiqa kuna da kyakkyawan abin koyi tare da Manzon Allah, ga wanda yake yin kyakkyawan fata game da Allah da ranar lahira, ya kuma ambaci Allah da yawa



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 22

وَلَمَّا رَءَا ٱلۡمُؤۡمِنُونَ ٱلۡأَحۡزَابَ قَالُواْ هَٰذَا مَا وَعَدَنَا ٱللَّهُ وَرَسُولُهُۥ وَصَدَقَ ٱللَّهُ وَرَسُولُهُۥۚ وَمَا زَادَهُمۡ إِلَّآ إِيمَٰنٗا وَتَسۡلِيمٗا

Lokacin kuwa da muminai suka ga rundunonin gangami sai suka ce: “Wannan shi ne abin da Allah da Manzonsa suka yi mana alqawari, Allah kuwa da Manzonsa sun yi gaskiya. Ba kuwa abin da (wannan) ya qara musu sai imani da miqa wuya



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 23

مِّنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ رِجَالٞ صَدَقُواْ مَا عَٰهَدُواْ ٱللَّهَ عَلَيۡهِۖ فَمِنۡهُم مَّن قَضَىٰ نَحۡبَهُۥ وَمِنۡهُم مَّن يَنتَظِرُۖ وَمَا بَدَّلُواْ تَبۡدِيلٗا

Akwai wasu mazaje daga muminai da suka cika abin da suka yi wa Allah alqawari da shi; akwai daga cikinsu wanda ya haxu da ajalinsa, akwai kuma daga cikinsu wanda yake sauraron (ajalin); kuma ba su yi kowace irin savawa ba (game da alqawarin)



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 24

لِّيَجۡزِيَ ٱللَّهُ ٱلصَّـٰدِقِينَ بِصِدۡقِهِمۡ وَيُعَذِّبَ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ إِن شَآءَ أَوۡ يَتُوبَ عَلَيۡهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Don Allah Ya saka wa masu gaskiya a kan gaskiyarsu, Ya kuma azabtar da munafukai idan Ya ga dama, ko kuma Ya karvi tubarsu. Lalle Allah Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 25

وَرَدَّ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِغَيۡظِهِمۡ لَمۡ يَنَالُواْ خَيۡرٗاۚ وَكَفَى ٱللَّهُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ ٱلۡقِتَالَۚ وَكَانَ ٱللَّهُ قَوِيًّا عَزِيزٗا

Allah kuma Ya komar da waxanda suka kafirta da fushinsu ba su sami wani alheri ba. Allah kuma Ya xauke wa muminai yin yaqi. Domin kuwa Allah Ya kasance Mai qarfi ne, Mabuwayi



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 26

وَأَنزَلَ ٱلَّذِينَ ظَٰهَرُوهُم مِّنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ مِن صَيَاصِيهِمۡ وَقَذَفَ فِي قُلُوبِهِمُ ٱلرُّعۡبَ فَرِيقٗا تَقۡتُلُونَ وَتَأۡسِرُونَ فَرِيقٗا

Ya kuma sauko da waxanda suka taimake su daga ma’abota littafi[1] daga ganuwoyinsu Ya kuma jefa tsoro a zukatansu, wasu jama’ar kuke kashe su kuna kuma ribace wasu jama’ar


1- Watau Yahudawan Banu Quraiza. Ya sauko da su daga ganuwoyinsu da suka tanada don kare kansu.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 27

وَأَوۡرَثَكُمۡ أَرۡضَهُمۡ وَدِيَٰرَهُمۡ وَأَمۡوَٰلَهُمۡ وَأَرۡضٗا لَّمۡ تَطَـُٔوهَاۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٗا

Ya kuma gadar muku qasarsu da gidajensu da dukiyoyinsu, da kuma wata qasa ma da ba ku tava taka ta ba[1]. Allah kuwa Ya kasance Mai iko ne a kan komai


1- Watau ita ce qasar Khaibar wadda Musulmi suka samu bayan shekara ta biyu da gama yaqin Ahzab.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 28

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ قُل لِّأَزۡوَٰجِكَ إِن كُنتُنَّ تُرِدۡنَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا وَزِينَتَهَا فَتَعَالَيۡنَ أُمَتِّعۡكُنَّ وَأُسَرِّحۡكُنَّ سَرَاحٗا جَمِيلٗا

Ya kai wannan Annabi, ka gaya wa matanka: “Idan kun kasance kuna son rayuwar duniya ne da kuma adonta, to sai ku zo in jiyar da ku daxi, in kuma sake ku kyakkyawan saki



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 29

وَإِن كُنتُنَّ تُرِدۡنَ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ وَٱلدَّارَ ٱلۡأٓخِرَةَ فَإِنَّ ٱللَّهَ أَعَدَّ لِلۡمُحۡسِنَٰتِ مِنكُنَّ أَجۡرًا عَظِيمٗا

“Idan kuwa kun kasance kuna qaunar Allah ne da Manzonsa da kuma ranar lahira, to haqiqa Allah Ya tanadi lada mai girma ga masu kyautatawa daga cikinku



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 30

يَٰنِسَآءَ ٱلنَّبِيِّ مَن يَأۡتِ مِنكُنَّ بِفَٰحِشَةٖ مُّبَيِّنَةٖ يُضَٰعَفۡ لَهَا ٱلۡعَذَابُ ضِعۡفَيۡنِۚ وَكَانَ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٗا

Ya ku matan Annabi, duk wadda ta zo da wani abin qi na sarari daga cikinku to za a ninninka mata azaba ninki biyu. Yin wannan kuma ya kasance abu ne mai sauqi ga Allah