Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 1

طسٓمٓ

XA SIN MIM[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 2

تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ

Waxannan ayoyi ne na Littafi mabayyani



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 3

نَتۡلُواْ عَلَيۡكَ مِن نَّبَإِ مُوسَىٰ وَفِرۡعَوۡنَ بِٱلۡحَقِّ لِقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ

Muna karanta maka labarin Musa da Fir’auna da gaskiya don mutane da suke yin imani



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 4

إِنَّ فِرۡعَوۡنَ عَلَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَجَعَلَ أَهۡلَهَا شِيَعٗا يَسۡتَضۡعِفُ طَآئِفَةٗ مِّنۡهُمۡ يُذَبِّحُ أَبۡنَآءَهُمۡ وَيَسۡتَحۡيِۦ نِسَآءَهُمۡۚ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلۡمُفۡسِدِينَ

Lalle Fir’auna ya yi xagawa a cikin qasar (Masar) ya kuma mayar da mutanenta qungiyoyi daban-daban, yana bautar da wata qungiyar daga cikinsu, yana yanka ‘ya’yayensu maza, yana kuma qyale matansu da rai. Lalle shi ya kasance cikin mavarnata



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 5

وَنُرِيدُ أَن نَّمُنَّ عَلَى ٱلَّذِينَ ٱسۡتُضۡعِفُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَنَجۡعَلَهُمۡ أَئِمَّةٗ وَنَجۡعَلَهُمُ ٱلۡوَٰرِثِينَ

Muna kuma nufin za Mu yi baiwa ga waxanda aka wulaqanta a cikin qasar (Masar) Mu kuma mayar da su shugabanni, kuma Mu mayar da su magadan (mulkin Fir’auna)



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 6

وَنُمَكِّنَ لَهُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَنُرِيَ فِرۡعَوۡنَ وَهَٰمَٰنَ وَجُنُودَهُمَا مِنۡهُم مَّا كَانُواْ يَحۡذَرُونَ

Mu kuma kafa su a qasar, kuma Mu nuna wa Fir’auna da Hamana da rundunoninsu gaba xayansu abin da suke jin tsoro game da su (Banu Isra’ila)



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 7

وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰٓ أُمِّ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَرۡضِعِيهِۖ فَإِذَا خِفۡتِ عَلَيۡهِ فَأَلۡقِيهِ فِي ٱلۡيَمِّ وَلَا تَخَافِي وَلَا تَحۡزَنِيٓۖ إِنَّا رَآدُّوهُ إِلَيۡكِ وَجَاعِلُوهُ مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Muka kuma yi wa mahaifiyar Musa wahayi da cewa: “Ki shayar da shi; to yayin da kika ji masa tsoro, sai ki jefa shi a cikin kogi, kada kuma ki ji tsoro, kuma kada ki yi baqin ciki; lalle Mu Masu dawo miki da shi ne, kuma Masu sanya shi ne cikin manzanni.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 8

فَٱلۡتَقَطَهُۥٓ ءَالُ فِرۡعَوۡنَ لِيَكُونَ لَهُمۡ عَدُوّٗا وَحَزَنًاۗ إِنَّ فِرۡعَوۡنَ وَهَٰمَٰنَ وَجُنُودَهُمَا كَانُواْ خَٰطِـِٔينَ

Sai mutanen Fir’auna suka tsince shi domin (daga baya) ya zama abokin gaba da kuma baqin ciki a gare su. Lalle Fir’auna da Hamana da rundunoninsu sun kasance masu laifi



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 9

وَقَالَتِ ٱمۡرَأَتُ فِرۡعَوۡنَ قُرَّتُ عَيۡنٖ لِّي وَلَكَۖ لَا تَقۡتُلُوهُ عَسَىٰٓ أَن يَنفَعَنَآ أَوۡ نَتَّخِذَهُۥ وَلَدٗا وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Matar Fir’auna kuma ta ce: “(Shi) farin ciki ne a gare ni har da kai; kada ku kashe shi, muna fatan ya amfane mu ko kuma mu xauke shi a matsayin xa,” alhali kuwa su ba su san (abin da zai faru ba)



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 10

وَأَصۡبَحَ فُؤَادُ أُمِّ مُوسَىٰ فَٰرِغًاۖ إِن كَادَتۡ لَتُبۡدِي بِهِۦ لَوۡلَآ أَن رَّبَطۡنَا عَلَىٰ قَلۡبِهَا لِتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Zuciyar mahaifiyar Musa kuma ta wayi gari ba komai a cikinta (sai tunaninsa); ba shakka sauran qiris ta bayyana shi, ba don Mun xaure zuciyarta ba don ta zama cikin muminai



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 11

وَقَالَتۡ لِأُخۡتِهِۦ قُصِّيهِۖ فَبَصُرَتۡ بِهِۦ عَن جُنُبٖ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Ta kuma ce da ‘yar’uwarsa: “Ki bi sawunsa”; sai ta hango shi daga nesa, su kuwa ba su gane ita (‘yar’uwarsa ba ce)



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 12

۞وَحَرَّمۡنَا عَلَيۡهِ ٱلۡمَرَاضِعَ مِن قَبۡلُ فَقَالَتۡ هَلۡ أَدُلُّكُمۡ عَلَىٰٓ أَهۡلِ بَيۡتٖ يَكۡفُلُونَهُۥ لَكُمۡ وَهُمۡ لَهُۥ نَٰصِحُونَ

Da ma kuma can Mun haramta masa (nonon) masu shayarwa[1], sai (‘yar’uwar tasa) ta ce: “Yanzu ba na nuna muku mutanen wani gida da za su shayar muku da shi ba, su kuma za su kyautata masa?”


1- Watau ya qi karvar nonon duk wata mai shayarwa da aka kawo don shayar da shi a gidan Fir’auna.


Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 13

فَرَدَدۡنَٰهُ إِلَىٰٓ أُمِّهِۦ كَيۡ تَقَرَّ عَيۡنُهَا وَلَا تَحۡزَنَ وَلِتَعۡلَمَ أَنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Sai Muka dawo da shi wurin mahaifiyarsa don hankalinta ya kwanta kuma don kada ta yi baqin ciki, don kuma ta san cewa alqawarin Allah gaskiya ne, sai dai kuma yawancinsu ba sa fahimtar (haka)



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 14

وَلَمَّا بَلَغَ أَشُدَّهُۥ وَٱسۡتَوَىٰٓ ءَاتَيۡنَٰهُ حُكۡمٗا وَعِلۡمٗاۚ وَكَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lokacin kuma da ya kai ganiyar qarfinsa ya kuma kammala, sai Muka ba shi hukunci da ilimi. Kamar haka kuwa Muke saka wa masu kyautatawa



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 15

وَدَخَلَ ٱلۡمَدِينَةَ عَلَىٰ حِينِ غَفۡلَةٖ مِّنۡ أَهۡلِهَا فَوَجَدَ فِيهَا رَجُلَيۡنِ يَقۡتَتِلَانِ هَٰذَا مِن شِيعَتِهِۦ وَهَٰذَا مِنۡ عَدُوِّهِۦۖ فَٱسۡتَغَٰثَهُ ٱلَّذِي مِن شِيعَتِهِۦ عَلَى ٱلَّذِي مِنۡ عَدُوِّهِۦ فَوَكَزَهُۥ مُوسَىٰ فَقَضَىٰ عَلَيۡهِۖ قَالَ هَٰذَا مِنۡ عَمَلِ ٱلشَّيۡطَٰنِۖ إِنَّهُۥ عَدُوّٞ مُّضِلّٞ مُّبِينٞ

Sai ya shiga cikin birnin a lokacin hutawar mutanensa, sai ya sami mutum biyu a cikinsa suna faxa; wannan xan qabilarsa ne, wannan kuma daga maqiyansa, sai xan qabilar tasa ya nemi taimakonsa a kan wanda yake daga maqiyansa; to sai Musa ya naushe shi, sai kuwa ya kashe shi; (da ya ga haka sai) ya ce: “Wannan yana daga aikin Shaixan, lalle shi kuwa maqiyi ne mai vatarwa na fili.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 16

قَالَ رَبِّ إِنِّي ظَلَمۡتُ نَفۡسِي فَٱغۡفِرۡ لِي فَغَفَرَ لَهُۥٓۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni na zalunci kaina, sai Ka yi min gafara,” sai ko Ya yi masa gafara. Lalle Shi kuwa Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 17

قَالَ رَبِّ بِمَآ أَنۡعَمۡتَ عَلَيَّ فَلَنۡ أَكُونَ ظَهِيرٗا لِّلۡمُجۡرِمِينَ

Ya ce: “Ya Ubangijina, saboda ni’imar da Ka yi min, ba zan tava zama mai taimakon masu laifi ba.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 18

فَأَصۡبَحَ فِي ٱلۡمَدِينَةِ خَآئِفٗا يَتَرَقَّبُ فَإِذَا ٱلَّذِي ٱسۡتَنصَرَهُۥ بِٱلۡأَمۡسِ يَسۡتَصۡرِخُهُۥۚ قَالَ لَهُۥ مُوسَىٰٓ إِنَّكَ لَغَوِيّٞ مُّبِينٞ

Sai ya wayi gari a cikin birnin a tsorace yana xar-xar, sai ga wanda ya nemi taimakon nan nasa a jiya yana sake neman taimakonsa, (sai) Musa ya ce da shi: “Lalle kai dai vatacce ne a fili!”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 19

فَلَمَّآ أَنۡ أَرَادَ أَن يَبۡطِشَ بِٱلَّذِي هُوَ عَدُوّٞ لَّهُمَا قَالَ يَٰمُوسَىٰٓ أَتُرِيدُ أَن تَقۡتُلَنِي كَمَا قَتَلۡتَ نَفۡسَۢا بِٱلۡأَمۡسِۖ إِن تُرِيدُ إِلَّآ أَن تَكُونَ جَبَّارٗا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا تُرِيدُ أَن تَكُونَ مِنَ ٱلۡمُصۡلِحِينَ

To lokacin da ya nufi wawurar abokin gabar tasu (sai mai neman taimakon) ya ce: “Ya Musa, shin yanzu nufi kake ka kashe ni kamar yadda ka kashe rai a jiya? Ba abin da kake nufi sai ka zama mai tsaurin rai a bayan qasa; ba ka kuma nufin ka zama cikin masu kawo gyara.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 20

وَجَآءَ رَجُلٞ مِّنۡ أَقۡصَا ٱلۡمَدِينَةِ يَسۡعَىٰ قَالَ يَٰمُوسَىٰٓ إِنَّ ٱلۡمَلَأَ يَأۡتَمِرُونَ بِكَ لِيَقۡتُلُوكَ فَٱخۡرُجۡ إِنِّي لَكَ مِنَ ٱلنَّـٰصِحِينَ

Sai wani mutum (mumini daga mutanen Fir’auna) ya zo daga can qarshen birnin yana gaggawa, ya ce: “Ya Musa, lalle manyan gari (suna can) suna shawara a kanka don su kashe ka, to ka fita (daga birnin nan), lalle ni ina cikin masu yi maka nasiha.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 21

فَخَرَجَ مِنۡهَا خَآئِفٗا يَتَرَقَّبُۖ قَالَ رَبِّ نَجِّنِي مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Sai ya fita daga cikinsa (wato birnin) a tsorace yana ta xar-xar, ya ce: “Ya Ubangijina, Ka tserar da ni daga azzaluman mutanen nan.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 22

وَلَمَّا تَوَجَّهَ تِلۡقَآءَ مَدۡيَنَ قَالَ عَسَىٰ رَبِّيٓ أَن يَهۡدِيَنِي سَوَآءَ ٱلسَّبِيلِ

Yayin da kuma ya sa gaba ya nufi wajen (birnin) Madyana, sai ya ce: “Ina fatan Ubangijina Ya shiryar da ni hanyar da ta fi dacewa.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 23

وَلَمَّا وَرَدَ مَآءَ مَدۡيَنَ وَجَدَ عَلَيۡهِ أُمَّةٗ مِّنَ ٱلنَّاسِ يَسۡقُونَ وَوَجَدَ مِن دُونِهِمُ ٱمۡرَأَتَيۡنِ تَذُودَانِۖ قَالَ مَا خَطۡبُكُمَاۖ قَالَتَا لَا نَسۡقِي حَتَّىٰ يُصۡدِرَ ٱلرِّعَآءُۖ وَأَبُونَا شَيۡخٞ كَبِيرٞ

Lokacin da kuma ya iso mashayar ruwa ta Madyana sai ya sami wani gungun mutane suna shayar (da dabbobinsu), ya kuma sami wasu mata su biyu a gefensu suna kare (dabbobinsu); sai ya ce (da su): “Me ya same ku ne?” Sai suka ce: “Mu ai ba ma shayarwa har sai duk makiyaya sun watse, kuma mahaifinmu tsoho ne tukub.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 24

فَسَقَىٰ لَهُمَا ثُمَّ تَوَلَّىٰٓ إِلَى ٱلظِّلِّ فَقَالَ رَبِّ إِنِّي لِمَآ أَنزَلۡتَ إِلَيَّ مِنۡ خَيۡرٖ فَقِيرٞ

To sai ya shayar musu (da dabbobin nasu), sannan ya koma wurin wata inuwa ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni mabuqacin duk wani alhairi ne da za ka hore mini!”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 25

فَجَآءَتۡهُ إِحۡدَىٰهُمَا تَمۡشِي عَلَى ٱسۡتِحۡيَآءٖ قَالَتۡ إِنَّ أَبِي يَدۡعُوكَ لِيَجۡزِيَكَ أَجۡرَ مَا سَقَيۡتَ لَنَاۚ فَلَمَّا جَآءَهُۥ وَقَصَّ عَلَيۡهِ ٱلۡقَصَصَ قَالَ لَا تَخَفۡۖ نَجَوۡتَ مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Sai xayarsu ta zo masa tana tafiya cikin jin kunya ta ce: “Babana yana kiran ka don ya saka maka ladan shayarwar da ka yi mana.” To lokacin da ya zo wurinsa ya kuma ba shi labarin(sa) sai ya ce da shi: “Kada ka ji tsoro, ka tsira daga azzaluman mutane.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 26

قَالَتۡ إِحۡدَىٰهُمَا يَـٰٓأَبَتِ ٱسۡتَـٔۡجِرۡهُۖ إِنَّ خَيۡرَ مَنِ ٱسۡتَـٔۡجَرۡتَ ٱلۡقَوِيُّ ٱلۡأَمِينُ

Sai xayarsu ta ce: “Babana, ka xauke shi aiki mana; don kuwa lalle ba wanda ya fi dacewa ka xauka aiki sai qaqqarfa, amintacce.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 27

قَالَ إِنِّيٓ أُرِيدُ أَنۡ أُنكِحَكَ إِحۡدَى ٱبۡنَتَيَّ هَٰتَيۡنِ عَلَىٰٓ أَن تَأۡجُرَنِي ثَمَٰنِيَ حِجَجٖۖ فَإِنۡ أَتۡمَمۡتَ عَشۡرٗا فَمِنۡ عِندِكَۖ وَمَآ أُرِيدُ أَنۡ أَشُقَّ عَلَيۡكَۚ سَتَجِدُنِيٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Sai ya ce da (Musa): “Ina so in aura maka xaya daga ‘ya’yayen nan nawa guda biyu, a kan ka yi min aiki na shekara takwas; to amma idan ka cika goma to wannan raxin kanka ne; ba na kuwa nufin in quntata maka. Za ka same ni kuwa in Allah Ya yarda daga cikin nagartattun mutane.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 28

قَالَ ذَٰلِكَ بَيۡنِي وَبَيۡنَكَۖ أَيَّمَا ٱلۡأَجَلَيۡنِ قَضَيۡتُ فَلَا عُدۡوَٰنَ عَلَيَّۖ وَٱللَّهُ عَلَىٰ مَا نَقُولُ وَكِيلٞ

(Musa) ya ce: “Wannan tsakanina da kai ne; kowanne xayan lokatan biyu na cika to kada a qware ni; Allah kuwa shaida ne game da abin da muke faxa.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 29

۞فَلَمَّا قَضَىٰ مُوسَى ٱلۡأَجَلَ وَسَارَ بِأَهۡلِهِۦٓ ءَانَسَ مِن جَانِبِ ٱلطُّورِ نَارٗاۖ قَالَ لِأَهۡلِهِ ٱمۡكُثُوٓاْ إِنِّيٓ ءَانَسۡتُ نَارٗا لَّعَلِّيٓ ءَاتِيكُم مِّنۡهَا بِخَبَرٍ أَوۡ جَذۡوَةٖ مِّنَ ٱلنَّارِ لَعَلَّكُمۡ تَصۡطَلُونَ

To yayin da Musa ya cika lokacinsa ya kuma tafi da iyalinsa, sai ya hango wuta daga gefen (dutsen) Xuri, ya ce: “Lalle na hango wuta, (zan je don) in zo muku da labari daga wurinta ko kuma (in samo muku) wani garwashi na wutar don ku ji xumi.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 30

فَلَمَّآ أَتَىٰهَا نُودِيَ مِن شَٰطِيِٕ ٱلۡوَادِ ٱلۡأَيۡمَنِ فِي ٱلۡبُقۡعَةِ ٱلۡمُبَٰرَكَةِ مِنَ ٱلشَّجَرَةِ أَن يَٰمُوسَىٰٓ إِنِّيٓ أَنَا ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

To lokacin da ya zo wurinta sai aka yi kira daga gefen kwari na damarsa a wani wuri mai albarka na bishiya, cewa: “Ya Musa, lalle Ni ne Allah Ubangijin talikai!