Capítulo: Suratul Masad

Verso : 1

تَبَّتۡ يَدَآ أَبِي لَهَبٖ وَتَبَّ

Hannayen Abu Lahabi[1] sun halaka, shi ma kuma ya halaka


1- Abu Lahab, xaya ne daga baffannin Manzon Allah wanda ya nuna wa Annabi () qiyayya ya mutu yana kafiri.


Capítulo: Suratul Masad

Verso : 2

مَآ أَغۡنَىٰ عَنۡهُ مَالُهُۥ وَمَا كَسَبَ

Dukiyarsa da abin da ya tsuwurwurta ba su amfana masa komai ba



Capítulo: Suratul Masad

Verso : 3

سَيَصۡلَىٰ نَارٗا ذَاتَ لَهَبٖ

Ba da daxewa ba zai shiga wuta mai balbali



Capítulo: Suratul Masad

Verso : 4

وَٱمۡرَأَتُهُۥ حَمَّالَةَ ٱلۡحَطَبِ

Da kuma matarsa mai yawan xaukar kayan qaya[1]


1- Watau Ummu Jamil, ta kasance tana zuba wa Annabi () qaya a kan hanyarsa domin ya taka.


Capítulo: Suratul Masad

Verso : 5

فِي جِيدِهَا حَبۡلٞ مِّن مَّسَدِۭ

A wuyanta akwai igiyar kaba mai ingantacciyar tukka. (a ranar alqiyama)