Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 1

وَيۡلٞ لِّكُلِّ هُمَزَةٖ لُّمَزَةٍ

Tsananin azaba ya tabbata ga duk wani mai yawan qyafice mai yawan suka[1]


1- Watau yawan qyafice ga mutane, yana kuma yawan sukan su da aibata su a bayan idanuwansu..


Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 2

ٱلَّذِي جَمَعَ مَالٗا وَعَدَّدَهُۥ

Wanda ya tara dukiya ya qididdige ta



Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 3

يَحۡسَبُ أَنَّ مَالَهُۥٓ أَخۡلَدَهُۥ

Yana zaton cewa dukiyarsa za ta dawwamar da shi



Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 4

كَلَّاۖ لَيُنۢبَذَنَّ فِي ٱلۡحُطَمَةِ

Faufau! Tabbas lalle sai an jefa shi cikin (wutar) ‘Huxama’[1]


1- Ita ce wuta mai kakkarya duk wani abu da aka jefa cikinta saboda tsananin zafinta da azabarta.


Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 5

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡحُطَمَةُ

Me kuma ya sanar da kai irin girman ‘Huxama’?



Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 6

نَارُ ٱللَّهِ ٱلۡمُوقَدَةُ

Wuta ce ta Allah abar hurawa



Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 7

ٱلَّتِي تَطَّلِعُ عَلَى ٱلۡأَفۡـِٔدَةِ

Wadda take mamaye zukata



Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 8

إِنَّهَا عَلَيۡهِم مُّؤۡصَدَةٞ

Lalle ita abar kullewa ce da su[1]


1- Watau za a kulle kafirai a cikin ruf babu fita.


Capítulo: Suratul Humaza

Verso : 9

فِي عَمَدٖ مُّمَدَّدَةِۭ

A cikin ginshiqai miqaqqu (da suka kewaye ta)