Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 61

وَإِذَا قِيلَ لَهُمۡ تَعَالَوۡاْ إِلَىٰ مَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ وَإِلَى ٱلرَّسُولِ رَأَيۡتَ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ يَصُدُّونَ عَنكَ صُدُودٗا

Kuma idan an ce da su: “Ku zo ga abin da Allah Ya saukar, kuma ku zo ga wannan Manzo,” sai kawai ka ga munafuqai suna bijire maka matuqar bijirewa



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 62

فَكَيۡفَ إِذَآ أَصَٰبَتۡهُم مُّصِيبَةُۢ بِمَا قَدَّمَتۡ أَيۡدِيهِمۡ ثُمَّ جَآءُوكَ يَحۡلِفُونَ بِٱللَّهِ إِنۡ أَرَدۡنَآ إِلَّآ إِحۡسَٰنٗا وَتَوۡفِيقًا

To yaya halinsu zai kasance idan wata musiba ta sauka a kansu saboda abin da hannayensu suka gabatar, sannan sai su zo maka suna rantsuwa da Allah, (suna cewa): “Ba ma nufin wani abu sai kyautatawa da kuma haxin kai.”?



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 63

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ يَعۡلَمُ ٱللَّهُ مَا فِي قُلُوبِهِمۡ فَأَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ وَعِظۡهُمۡ وَقُل لَّهُمۡ فِيٓ أَنفُسِهِمۡ قَوۡلَۢا بَلِيغٗا

Waxannan su ne waxanda Allah Yake sane da abin da ke cikin zukatansu, don haka ka kawar da kai daga kansu kuma ka yi musu wa’azi kuma ka faxa musu magana a karan-kawunansu magana mai shiga zukata



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 64

وَمَآ أَرۡسَلۡنَا مِن رَّسُولٍ إِلَّا لِيُطَاعَ بِإِذۡنِ ٱللَّهِۚ وَلَوۡ أَنَّهُمۡ إِذ ظَّلَمُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ جَآءُوكَ فَٱسۡتَغۡفَرُواْ ٱللَّهَ وَٱسۡتَغۡفَرَ لَهُمُ ٱلرَّسُولُ لَوَجَدُواْ ٱللَّهَ تَوَّابٗا رَّحِيمٗا

Kuma ba Mu tava aiko wani manzo ba, face sai don a yi masa xa’a da izinin Allah. Kuma da a ce lokacin da suka zalunci kawunansu sun zo maka, sun nemi Allah Ya gafarta musu, sannan Manzo ya roqa musu gafara, to tabbas da sun sami Allah Yana Mai yawan karvar tuba, Mai jin qai



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 65

فَلَا وَرَبِّكَ لَا يُؤۡمِنُونَ حَتَّىٰ يُحَكِّمُوكَ فِيمَا شَجَرَ بَيۡنَهُمۡ ثُمَّ لَا يَجِدُواْ فِيٓ أَنفُسِهِمۡ حَرَجٗا مِّمَّا قَضَيۡتَ وَيُسَلِّمُواْ تَسۡلِيمٗا

To ina rantsuwa da Ubangijinka, ba za su yi imani ba har sai sun kai hukunci a gabanka game da duk abin da ya faru na savani a tsakaninsu, sannan ba su ji wani qunci a cikin zukatansu ba game da abin da ka zartar na hukunci, kuma su miqa wuya miqawa gaba xaya



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 66

وَلَوۡ أَنَّا كَتَبۡنَا عَلَيۡهِمۡ أَنِ ٱقۡتُلُوٓاْ أَنفُسَكُمۡ أَوِ ٱخۡرُجُواْ مِن دِيَٰرِكُم مَّا فَعَلُوهُ إِلَّا قَلِيلٞ مِّنۡهُمۡۖ وَلَوۡ أَنَّهُمۡ فَعَلُواْ مَا يُوعَظُونَ بِهِۦ لَكَانَ خَيۡرٗا لَّهُمۡ وَأَشَدَّ تَثۡبِيتٗا

Kuma in da a ce lalle Mun wajabta musu cewa: “Ku kashe kawunanku ko ku fita daga gidajenku,” da ‘yan kaxan ne daga cikinsu za su aikata hakan. Da a ce sun aikata abin da ake musu wa’azi da shi, to da ya fi alheri, kuma da ya fi tsananin tabbatar da su (a kan hanya madaidaiciya)



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 67

وَإِذٗا لَّأٓتَيۡنَٰهُم مِّن لَّدُنَّآ أَجۡرًا عَظِيمٗا

Da sun yi hakan kuwa tabbas da Mun ba su wani babban lada daga wajenmu



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 68

وَلَهَدَيۡنَٰهُمۡ صِرَٰطٗا مُّسۡتَقِيمٗا

Kuma tabbas da Mun shiryar da su tafarki madaidaici



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 69

وَمَن يُطِعِ ٱللَّهَ وَٱلرَّسُولَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ مَعَ ٱلَّذِينَ أَنۡعَمَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلنَّبِيِّـۧنَ وَٱلصِّدِّيقِينَ وَٱلشُّهَدَآءِ وَٱلصَّـٰلِحِينَۚ وَحَسُنَ أُوْلَـٰٓئِكَ رَفِيقٗا

Kuma duk waxanda suka yi wa Allah xa’a da wannan Manzon, to waxannan suna tare da waxanda Allah Ya yi musu ni’ima, su ne annabawa da siddiqai da shahidai da salihan bayi. Kuma madalla da waxannan abokai



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 70

ذَٰلِكَ ٱلۡفَضۡلُ مِنَ ٱللَّهِۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ عَلِيمٗا

Wannan falala ce daga Allah. Kuma Allah Ya isa masanin (dukkan lamura)



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 71

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ خُذُواْ حِذۡرَكُمۡ فَٱنفِرُواْ ثُبَاتٍ أَوِ ٱنفِرُواْ جَمِيعٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi taka-tsantsan, kuma ku fita qungiya-qungiya, ko kuma ku fita gaba xaya



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 72

وَإِنَّ مِنكُمۡ لَمَن لَّيُبَطِّئَنَّ فَإِنۡ أَصَٰبَتۡكُم مُّصِيبَةٞ قَالَ قَدۡ أَنۡعَمَ ٱللَّهُ عَلَيَّ إِذۡ لَمۡ أَكُن مَّعَهُمۡ شَهِيدٗا

Kuma lalle a cikinku akwai wanda yake daqilewa, idan wata musiba ta same ku, sai ya ce: “Haqiqa Allah Ya yi mini ni’ima da ban halarci (yaqin) tare da su ba.”



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 73

وَلَئِنۡ أَصَٰبَكُمۡ فَضۡلٞ مِّنَ ٱللَّهِ لَيَقُولَنَّ كَأَن لَّمۡ تَكُنۢ بَيۡنَكُمۡ وَبَيۡنَهُۥ مَوَدَّةٞ يَٰلَيۡتَنِي كُنتُ مَعَهُمۡ فَأَفُوزَ فَوۡزًا عَظِيمٗا

Amma idan wata falala ta same ku daga Allah, tabbas zai riqa cewa, kamar daxai ba wata soyayya tsakaninku da shi: “Ina ma na kasance tare da su, don ni ma in rabauta rabo mai girma?”[1]


1- Watau a raba ganimar da aka samo tare da shi, shi ma ya more sosai.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 74

۞فَلۡيُقَٰتِلۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ ٱلَّذِينَ يَشۡرُونَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا بِٱلۡأٓخِرَةِۚ وَمَن يُقَٰتِلۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ فَيُقۡتَلۡ أَوۡ يَغۡلِبۡ فَسَوۡفَ نُؤۡتِيهِ أَجۡرًا عَظِيمٗا

To waxanda suke sayen rayuwar lahira da ta duniya, sai su yi yaqi don xaukaka kalmar Allah. Duk wanda yake yin yaqi don xaukaka kalmar Allah kuwa, sai aka kashe shi ko kuma ya yi galaba, to za Mu ba shi lada mai girma



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 75

وَمَا لَكُمۡ لَا تُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَٱلۡمُسۡتَضۡعَفِينَ مِنَ ٱلرِّجَالِ وَٱلنِّسَآءِ وَٱلۡوِلۡدَٰنِ ٱلَّذِينَ يَقُولُونَ رَبَّنَآ أَخۡرِجۡنَا مِنۡ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةِ ٱلظَّالِمِ أَهۡلُهَا وَٱجۡعَل لَّنَا مِن لَّدُنكَ وَلِيّٗا وَٱجۡعَل لَّنَا مِن لَّدُنكَ نَصِيرًا

Kuma me ya same ku ne, da ba za ku yi yaqi don xaukaka kalmar Allah ba, da kuma kuvutar da raunana maza da mata da yara qanana, waxanda suke cewa: “Ya Ubangijinmu, Ka fitar da mu daga wannan alqaryar wadda mutanenta suke azzalumai, kuma Ka sanya mana wani majivincin lamari daga wurinka, kuma Ka sanya mana wani mai taimako daga wurinka?”



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 76

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱلطَّـٰغُوتِ فَقَٰتِلُوٓاْ أَوۡلِيَآءَ ٱلشَّيۡطَٰنِۖ إِنَّ كَيۡدَ ٱلشَّيۡطَٰنِ كَانَ ضَعِيفًا

Waxanda suka yi imani suna yaqi ne don xaukaka kalmar Allah; waxanda kuma suka kafirce suna yin yaqi ne don kare Xagutu; to ku yaqi masoya Shaixan; lalle makircin Shaixan rarrauna ne



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 77

أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلَّذِينَ قِيلَ لَهُمۡ كُفُّوٓاْ أَيۡدِيَكُمۡ وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ فَلَمَّا كُتِبَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقِتَالُ إِذَا فَرِيقٞ مِّنۡهُمۡ يَخۡشَوۡنَ ٱلنَّاسَ كَخَشۡيَةِ ٱللَّهِ أَوۡ أَشَدَّ خَشۡيَةٗۚ وَقَالُواْ رَبَّنَا لِمَ كَتَبۡتَ عَلَيۡنَا ٱلۡقِتَالَ لَوۡلَآ أَخَّرۡتَنَآ إِلَىٰٓ أَجَلٖ قَرِيبٖۗ قُلۡ مَتَٰعُ ٱلدُّنۡيَا قَلِيلٞ وَٱلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لِّمَنِ ٱتَّقَىٰ وَلَا تُظۡلَمُونَ فَتِيلًا

Shin ba ka ganin waxanda aka ce da su: “Ku kame hannayenku kuma ku tsayar da salla kuma ku bayar da zakka?”[1] To yayin da aka wajabta musu yaqi, sai ga wani vangare daga cikinsu suna jin tsoron mutane kamar yadda suke jin tsoron Allah, ko ma fiye da hakan. Kuma sai suka ce: “Ya Ubangijinmu, don me Ka wajabta mana yin yaqi, me ya hana Ka jinkirta mana zuwa wani lokaci makusanci?” Ka ce: “Jin daxin duniya kaxan ne, lahira kuwa ita ce mafi alheri ga wanda ya yi taqawa, kuma ba za a zalunce ku ba, ko da gwargwadon zaren qwallon dabino ne.”


1- Watau wasu daga cikin sahabbai waxanda suke ta roqon a farlanta musu jihadi, amma ana nuna musu su bar wannan maganar, su dai tsayar da salla su ba da zakka.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 78

أَيۡنَمَا تَكُونُواْ يُدۡرِككُّمُ ٱلۡمَوۡتُ وَلَوۡ كُنتُمۡ فِي بُرُوجٖ مُّشَيَّدَةٖۗ وَإِن تُصِبۡهُمۡ حَسَنَةٞ يَقُولُواْ هَٰذِهِۦ مِنۡ عِندِ ٱللَّهِۖ وَإِن تُصِبۡهُمۡ سَيِّئَةٞ يَقُولُواْ هَٰذِهِۦ مِنۡ عِندِكَۚ قُلۡ كُلّٞ مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِۖ فَمَالِ هَـٰٓؤُلَآءِ ٱلۡقَوۡمِ لَا يَكَادُونَ يَفۡقَهُونَ حَدِيثٗا

Duk inda kuka kasance mutuwa za ta riske ku, ko da kuna cikin waxansu ganuwoyi masu tsawo. Kuma idan wani kyakkyawan abu ya same su, sai su ce: “Wannan ai daga Allah ne.” Idan kuma wani mummunan abu ya same su, sai su ce: “Wannan daga wajenka ne.”[1] Ka ce: “Dukkansu daga Allah ne.” Shin me ya sami waxannan mutane ne ba sa kusa ma da su fahimci zance?


1- Watau sai su camfa Manzon Allah () su ce saboda shi ne wannan masifar ta same su.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 79

مَّآ أَصَابَكَ مِنۡ حَسَنَةٖ فَمِنَ ٱللَّهِۖ وَمَآ أَصَابَكَ مِن سَيِّئَةٖ فَمِن نَّفۡسِكَۚ وَأَرۡسَلۡنَٰكَ لِلنَّاسِ رَسُولٗاۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ شَهِيدٗا

Duk wani kyakkyawan abu da ya same ka, to daga Allah ne; duk kuma wani mummunan abu da ya same ka, to daga wajen ka ne[1]. Kuma Mun aiko ka Manzo ga mutane. Kuma Allah Ya isa Mai shaida (a kan haka)


1- Watau saboda laifukansa ne da zunubansa.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 80

مَّن يُطِعِ ٱلرَّسُولَ فَقَدۡ أَطَاعَ ٱللَّهَۖ وَمَن تَوَلَّىٰ فَمَآ أَرۡسَلۡنَٰكَ عَلَيۡهِمۡ حَفِيظٗا

Duk wanda ya yi wa wannan Manzo xa’a, to haqiqa ya yi wa Allah xa’a ne; wanda kuwa ya bijire, to ba Mu aiko ka a matsayin mai tsaron su ba



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 81

وَيَقُولُونَ طَاعَةٞ فَإِذَا بَرَزُواْ مِنۡ عِندِكَ بَيَّتَ طَآئِفَةٞ مِّنۡهُمۡ غَيۡرَ ٱلَّذِي تَقُولُۖ وَٱللَّهُ يَكۡتُبُ مَا يُبَيِّتُونَۖ فَأَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱللَّهِۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ وَكِيلًا

Kuma sukan ce: “Ai ba mu da wani abu sai biyayya.” To idan suka fita daga wajenka, sai wata qungiya daga cikinsu, su riqa qulla wani abu daban cikin dare, savanin abin da suke faxa; Allah kuwa Yana rubuta duk wani abu da suke qullawa da daddare; to ka kawar da kai daga kansu, kuma ka dogara ga Allah. Allah kuwa Ya isa abin dogaro



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 82

أَفَلَا يَتَدَبَّرُونَ ٱلۡقُرۡءَانَۚ وَلَوۡ كَانَ مِنۡ عِندِ غَيۡرِ ٱللَّهِ لَوَجَدُواْ فِيهِ ٱخۡتِلَٰفٗا كَثِيرٗا

Shin ba za su yi zuzzurfan tunani game da (ayoyin) Alqur’ani ba ne? Kuma da a ce ya kasance daga wajen wani yake ba Allah ba, tabbas da sun sami savani mai yawa a cikinsa



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 83

وَإِذَا جَآءَهُمۡ أَمۡرٞ مِّنَ ٱلۡأَمۡنِ أَوِ ٱلۡخَوۡفِ أَذَاعُواْ بِهِۦۖ وَلَوۡ رَدُّوهُ إِلَى ٱلرَّسُولِ وَإِلَىٰٓ أُوْلِي ٱلۡأَمۡرِ مِنۡهُمۡ لَعَلِمَهُ ٱلَّذِينَ يَسۡتَنۢبِطُونَهُۥ مِنۡهُمۡۗ وَلَوۡلَا فَضۡلُ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ وَرَحۡمَتُهُۥ لَٱتَّبَعۡتُمُ ٱلشَّيۡطَٰنَ إِلَّا قَلِيلٗا

Kuma idan wani lamari ya zo musu wanda ya shafi zaman lafiya ko tsoro, sai su yaxa shi. Da a ce sun mayar da shi zuwa ga wannan Manzo da shugabanni daga cikinsu, da lalle wanxanda suke bin qwaqqwafin al’amarin sun san (dacewar a yaxa shi ko a’a). Kuma ba don falalar Allah da rahamarsa a gare ku ba, tabbas da kun bi Shaixan, in ban da ‘yan kaxan (daga cikinku)



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 84

فَقَٰتِلۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ لَا تُكَلَّفُ إِلَّا نَفۡسَكَۚ وَحَرِّضِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۖ عَسَى ٱللَّهُ أَن يَكُفَّ بَأۡسَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۚ وَٱللَّهُ أَشَدُّ بَأۡسٗا وَأَشَدُّ تَنكِيلٗا

To ka yi yaqi domin xaukaka kalmar Allah, ba a xora maka nauyin tilasta kowa ba sai kanka. Kuma ka zaburar da muminai; Allah zai dankwafe qarfin waxanda suka kafirta; kuma Allah Shi ne Mafi tsananin qarfi, kuma Mafi tsananin uquba



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 85

مَّن يَشۡفَعۡ شَفَٰعَةً حَسَنَةٗ يَكُن لَّهُۥ نَصِيبٞ مِّنۡهَاۖ وَمَن يَشۡفَعۡ شَفَٰعَةٗ سَيِّئَةٗ يَكُن لَّهُۥ كِفۡلٞ مِّنۡهَاۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ مُّقِيتٗا

Duk wanda ya yi (ma wani) kyakkyawar alfarma, zai samu rabonsa na lada daga gare ta; kuma duk wanda ya yi wa wani mummunar alfarma, zai samu rabonsa na zunubi daga gare ta. Kuma Allah Ya kasance Mai kiyaye komai ne[1]


1- Watau zai yi wa kowa sakamako gwargwadon aikinsa mai kyau ko mummuna.


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 86

وَإِذَا حُيِّيتُم بِتَحِيَّةٖ فَحَيُّواْ بِأَحۡسَنَ مِنۡهَآ أَوۡ رُدُّوهَآۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٍ حَسِيبًا

Kuma idan an gaishe ku da wata gaisuwa, to ku amsa da gaisuwar da ta fi wadda aka yi muku kyau, ko ku mayar da irinta. Lalle Allah Ya kasance Mai hisabi ne a kan kowane abu



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 87

ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۚ لَيَجۡمَعَنَّكُمۡ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ لَا رَيۡبَ فِيهِۗ وَمَنۡ أَصۡدَقُ مِنَ ٱللَّهِ حَدِيثٗا

Allah, babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. Lalle zai tattara ku a ranar alqiyama, wadda babu kokwanto a cikinsa. Kuma wane ne ya fi Allah gaskiyar zance?



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 88

۞فَمَا لَكُمۡ فِي ٱلۡمُنَٰفِقِينَ فِئَتَيۡنِ وَٱللَّهُ أَرۡكَسَهُم بِمَا كَسَبُوٓاْۚ أَتُرِيدُونَ أَن تَهۡدُواْ مَنۡ أَضَلَّ ٱللَّهُۖ وَمَن يُضۡلِلِ ٱللَّهُ فَلَن تَجِدَ لَهُۥ سَبِيلٗا

Shin me ya sa kuka kasu gida biyu dangane da lamarin munafuqai[1], alhali Allah ne Ya mayar da su baya saboda abin da suka aikata?[2] Shin kuna nufin ku shiryar da wanda Allah Ya riga Ya vatar da shi ne? Duk wanda Allah Ya vatar da shi kuwa, to ba za ka iya samar masa wata mafita ba


1- Watau wasu daga cikin muminai suna kafirta su wasu kuma ba sa kafirta su.


2- Watau na rashin biyayya da xa’a ga Allah da Manzonsa ().


Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 89

وَدُّواْ لَوۡ تَكۡفُرُونَ كَمَا كَفَرُواْ فَتَكُونُونَ سَوَآءٗۖ فَلَا تَتَّخِذُواْ مِنۡهُمۡ أَوۡلِيَآءَ حَتَّىٰ يُهَاجِرُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۚ فَإِن تَوَلَّوۡاْ فَخُذُوهُمۡ وَٱقۡتُلُوهُمۡ حَيۡثُ وَجَدتُّمُوهُمۡۖ وَلَا تَتَّخِذُواْ مِنۡهُمۡ وَلِيّٗا وَلَا نَصِيرًا

Sun yi fatan ina ma za ku kafirta kamar yadda suka kafirta, sai ku zama xaya. Don haka kar ku riqi masoya a cikinsu har sai sun yi hijira don Allah. Idan kuwa suka juya baya, to ku kama su, kuma ku kashe su a duk inda kuka same su; kuma kada ku riqi wani masoyi ko mai taimako daga cikinsu



Capítulo: Suratun Nisa’i

Verso : 90

إِلَّا ٱلَّذِينَ يَصِلُونَ إِلَىٰ قَوۡمِۭ بَيۡنَكُمۡ وَبَيۡنَهُم مِّيثَٰقٌ أَوۡ جَآءُوكُمۡ حَصِرَتۡ صُدُورُهُمۡ أَن يُقَٰتِلُوكُمۡ أَوۡ يُقَٰتِلُواْ قَوۡمَهُمۡۚ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَسَلَّطَهُمۡ عَلَيۡكُمۡ فَلَقَٰتَلُوكُمۡۚ فَإِنِ ٱعۡتَزَلُوكُمۡ فَلَمۡ يُقَٰتِلُوكُمۡ وَأَلۡقَوۡاْ إِلَيۡكُمُ ٱلسَّلَمَ فَمَا جَعَلَ ٱللَّهُ لَكُمۡ عَلَيۡهِمۡ سَبِيلٗا

Sai dai (ban da) waxanda suke fakewa a wajen waxansu mutane da kuke da yarjejeniya ta zaman lafiya a tsakaninku (da su), ko kuma waxanda suka zo muku zukatansu sun quntata game da yaqar ku ko yaqar mutanensu. Da kuwa Allah Ya ga dama da Ya xora su a kanku, kuma tabbas da sun yaqe ku. Don haka idan suka bar ku ba su yaqe ku ba, kuma suka miqa muku saqo na sulhu, to Allah bai ba ku wata dama ta ku yaqe su ba