Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 61

مَّلۡعُونِينَۖ أَيۡنَمَا ثُقِفُوٓاْ أُخِذُواْ وَقُتِّلُواْ تَقۡتِيلٗا

(Su) la’anannu ne; duk inda aka gamu da su a kama su, kuma a yi musu mummunan kisa



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 62

سُنَّةَ ٱللَّهِ فِي ٱلَّذِينَ خَلَوۡاْ مِن قَبۡلُۖ وَلَن تَجِدَ لِسُنَّةِ ٱللَّهِ تَبۡدِيلٗا

(Wannan) Sunnar Allah ce ga waxanda suka gabata a da; ba kuma za ka sami wani canji ba game da sunnar Allah



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 63

يَسۡـَٔلُكَ ٱلنَّاسُ عَنِ ٱلسَّاعَةِۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ ٱللَّهِۚ وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّ ٱلسَّاعَةَ تَكُونُ قَرِيبًا

Mutane suna tambayar ka game da (ranar) alqiyama; ka ce (da su): “Saninta a wajen Allah kawai yake.” Ba ka sani ba ko watakila alqiyamar za ta kasance kusa



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 64

إِنَّ ٱللَّهَ لَعَنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ وَأَعَدَّ لَهُمۡ سَعِيرًا

Lalle Allah Ya la’anci kafirai Ya kuma tanadar musu da (wutar) Sa’ira



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 65

خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ لَّا يَجِدُونَ وَلِيّٗا وَلَا نَصِيرٗا

Masu dawwama ne a cikinta har abada; ba kuma za su sami wani majivinci ko mataimaki ba



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 66

يَوۡمَ تُقَلَّبُ وُجُوهُهُمۡ فِي ٱلنَّارِ يَقُولُونَ يَٰلَيۡتَنَآ أَطَعۡنَا ٱللَّهَ وَأَطَعۡنَا ٱلرَّسُولَا۠

A ranar da za a riqa jujjuya fuskokinsu cikin wuta, suna cewa: “Kaiconmu, ina ma da mun bi Allah mun bi Manzo!”



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 67

وَقَالُواْ رَبَّنَآ إِنَّآ أَطَعۡنَا سَادَتَنَا وَكُبَرَآءَنَا فَأَضَلُّونَا ٱلسَّبِيلَا۠

Suka kuma ce: “Ya Ubangijinmu, lalle mu mun bi shugabanninmu da manyanmu sai suka vatar da mu hanya



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 68

رَبَّنَآ ءَاتِهِمۡ ضِعۡفَيۡنِ مِنَ ٱلۡعَذَابِ وَٱلۡعَنۡهُمۡ لَعۡنٗا كَبِيرٗا

“Ya Ubangijinmu, Ka ba su azaba rivi biyu, Ka kuma la’ance su babbar la’ana.”



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 69

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَكُونُواْ كَٱلَّذِينَ ءَاذَوۡاْ مُوسَىٰ فَبَرَّأَهُ ٱللَّهُ مِمَّا قَالُواْۚ وَكَانَ عِندَ ٱللَّهِ وَجِيهٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku zamanto kamar waxanda suka cuci Musa sai Allah Ya wanke shi daga abin da suka faxa (a kansa). Ya kuma kasance mai alfarma ne a wurin Allah



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 70

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَقُولُواْ قَوۡلٗا سَدِيدٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku faxi Magana wadda take daidai ce



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 71

يُصۡلِحۡ لَكُمۡ أَعۡمَٰلَكُمۡ وَيَغۡفِرۡ لَكُمۡ ذُنُوبَكُمۡۗ وَمَن يُطِعِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ فَقَدۡ فَازَ فَوۡزًا عَظِيمًا

Zai kyautata muku ayyukanku, Ya kuma gafarta muku zunubanku. Duk kuwa wanda ya bi Allah da Manzonsa, to haqiqa ya rabauta rabauta mai girma



Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 72

إِنَّا عَرَضۡنَا ٱلۡأَمَانَةَ عَلَى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَٱلۡجِبَالِ فَأَبَيۡنَ أَن يَحۡمِلۡنَهَا وَأَشۡفَقۡنَ مِنۡهَا وَحَمَلَهَا ٱلۡإِنسَٰنُۖ إِنَّهُۥ كَانَ ظَلُومٗا جَهُولٗا

Lalle Mun bijiro da amana[1] ga sammai da qasa da duwatsu sai suka qi xaukar ta suka ji tsoron ta, sai kuwa mutum ya xauke ta; lalle shi (mutum) ya kasance mai zaluntar kansa ne, mai jahilci


1- Amana a nan, su ne dokokin shari’a na umarni da hani.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 73

لِّيُعَذِّبَ ٱللَّهُ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱلۡمُنَٰفِقَٰتِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ وَٱلۡمُشۡرِكَٰتِ وَيَتُوبَ ٱللَّهُ عَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِۗ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمَۢا

Don Allah Ya azabtar da munafukai maza da munafukai mata, da mushirikai maza da mushirikai mata, Ya kuma karvi tubar muminai maza da muminai mata. Allah kuwa Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai