Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 61

ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱللَّهَ يُولِجُ ٱلَّيۡلَ فِي ٱلنَّهَارِ وَيُولِجُ ٱلنَّهَارَ فِي ٱلَّيۡلِ وَأَنَّ ٱللَّهَ سَمِيعُۢ بَصِيرٞ

Wannan (taimakon kuwa zai kasance ne) saboda lalle Allah Shi Yake shigar da dare cikin rana, Yake kuma shigar da rana cikin dare, kuma lalle Allah Mai ji ne, Mai gani



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 62

ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡحَقُّ وَأَنَّ مَا يَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ هُوَ ٱلۡبَٰطِلُ وَأَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡعَلِيُّ ٱلۡكَبِيرُ

Wannan kuwa saboda lalle Allah Shi ne (abin bauta) na gaskiya, kuma lalle abin da suke bauta wa wanda ba Shi ba shi na qarya ne, kuma lalle Allah Shi ne Maxaukaki, Mai girma



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 63

أَلَمۡ تَرَ أَنَّ ٱللَّهَ أَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَتُصۡبِحُ ٱلۡأَرۡضُ مُخۡضَرَّةًۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَطِيفٌ خَبِيرٞ

Shin ba ka ga cewa Allah ne Ya saukar da ruwa daga sama ba, sai qasa ta zama koriya shar? Lalle Allah Mai tausasawa ne, Masani



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 64

لَّهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ لَهُوَ ٱلۡغَنِيُّ ٱلۡحَمِيدُ

Abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa nasa ne. Kuma lalle Allah tabbas Shi ne Mawadaci, Sha-Yabo



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 65

أَلَمۡ تَرَ أَنَّ ٱللَّهَ سَخَّرَ لَكُم مَّا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَٱلۡفُلۡكَ تَجۡرِي فِي ٱلۡبَحۡرِ بِأَمۡرِهِۦ وَيُمۡسِكُ ٱلسَّمَآءَ أَن تَقَعَ عَلَى ٱلۡأَرۡضِ إِلَّا بِإِذۡنِهِۦٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ بِٱلنَّاسِ لَرَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Shin ba ka ga cewa Allah Ya hore muku abin da yake cikin qasa, da kuma jiragen ruwa da suke gudu a cikin kogi da umarninsa, kuma Yake riqe sama don kada ta faxo a kan qasa, sai da izininsa? Lalle Allah Mai tausayi ne, Mai rahama ga mutane



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 66

وَهُوَ ٱلَّذِيٓ أَحۡيَاكُمۡ ثُمَّ يُمِيتُكُمۡ ثُمَّ يُحۡيِيكُمۡۗ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَكَفُورٞ

Shi ne kuma Wanda Ya raya ku sannan zai kashe ku sannan Ya (sake) raya ku. Lalle mutum tabbas mai yawan butulci ne



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 67

لِّكُلِّ أُمَّةٖ جَعَلۡنَا مَنسَكًا هُمۡ نَاسِكُوهُۖ فَلَا يُنَٰزِعُنَّكَ فِي ٱلۡأَمۡرِۚ وَٱدۡعُ إِلَىٰ رَبِّكَۖ إِنَّكَ لَعَلَىٰ هُدٗى مُّسۡتَقِيمٖ

Kowacce al’umma Mun sanya mata hanyar (shari’a) da za su yi aiki da ita; to lalle kada su yi jayayya da kai game da lamarin (addini). Kuma ka yi kira zuwa ga (addinin) Ubangijinka; lalle kai tabbas kana bisa shiriya madaidaiciya



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 68

وَإِن جَٰدَلُوكَ فَقُلِ ٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا تَعۡمَلُونَ

Idan kuwa suka yi maka jayayya, sai ka ce: “Allah ne Ya fi sanin abin da kuke aikatawa.”



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 69

ٱللَّهُ يَحۡكُمُ بَيۡنَكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فِيمَا كُنتُمۡ فِيهِ تَخۡتَلِفُونَ

Allah zai yi hukunci a tsakaninku ranar alqiyama game da abin da kuka kasance kuna sassavawa a kansa



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 70

أَلَمۡ تَعۡلَمۡ أَنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ مَا فِي ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِۚ إِنَّ ذَٰلِكَ فِي كِتَٰبٍۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٞ

Shin ba ka sani ba cewa lalle Allah Yana sane da abin da yake cikin sama da wanda yake qasa? Lalle wannan yana cikin littafi (wato Lauhul-Mahafuzu). Lalle wannan mai sauqi ne a wurin Allah



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 71

وَيَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ مَا لَمۡ يُنَزِّلۡ بِهِۦ سُلۡطَٰنٗا وَمَا لَيۡسَ لَهُم بِهِۦ عِلۡمٞۗ وَمَا لِلظَّـٰلِمِينَ مِن نَّصِيرٖ

Suna kuma bauta wa wanda ba Allah ba, abin da bai saukar da wani dalili ba game da shi, da kuma abin da ba su da ilimi game da shi. Azzalumai kuwa ba su da wani mataimaki



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 72

وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ تَعۡرِفُ فِي وُجُوهِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلۡمُنكَرَۖ يَكَادُونَ يَسۡطُونَ بِٱلَّذِينَ يَتۡلُونَ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتِنَاۗ قُلۡ أَفَأُنَبِّئُكُم بِشَرّٖ مِّن ذَٰلِكُمُۚ ٱلنَّارُ وَعَدَهَا ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Idan kuma ana karanta musu ayoyinmu bayyanannu, to za ka ga alamar musantawa a fuskokin waxanda suka kafirta, suna kamar za su auka wa waxanda suke karanta musu ayoyinmu. To ka ce: “Shin ba na ba ku labarin abin da ya fi wannan muni ba[1]? Wuta ce da Allah Ya yi alqawari ga waxanda suka kafirta; makoma kuwa ta munana.”


1- Watau fiye da abin da suke ganin muninsa idan ana karanta musu shi, watau ayoyin Alqur’ani.


Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 73

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ضُرِبَ مَثَلٞ فَٱسۡتَمِعُواْ لَهُۥٓۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ تَدۡعُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ لَن يَخۡلُقُواْ ذُبَابٗا وَلَوِ ٱجۡتَمَعُواْ لَهُۥۖ وَإِن يَسۡلُبۡهُمُ ٱلذُّبَابُ شَيۡـٔٗا لَّا يَسۡتَنقِذُوهُ مِنۡهُۚ ضَعُفَ ٱلطَّالِبُ وَٱلۡمَطۡلُوبُ

Ya ku mutane, an ba da misali, to sai ku saurare shi. Lalle waxanda kuke bauta wa ba Allah ba, ba za su tava iya halittar quda ba, ko da sun taru domin (halitta) shi; idan kuma da qudan zai cire musu (su gumakan) wani abu, to ba za su iya qwato shi ba daga wurinsa. Wanda yake nema da wanda ake nema (duka) sun yi rauni!



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 74

مَا قَدَرُواْ ٱللَّهَ حَقَّ قَدۡرِهِۦٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَقَوِيٌّ عَزِيزٌ

Ba su girmama Allah ba kamar yadda ya kamata su girmama Shi. Lalle Allah tabbas Qaqqarfa ne, Mabuwayi



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 75

ٱللَّهُ يَصۡطَفِي مِنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ رُسُلٗا وَمِنَ ٱلنَّاسِۚ إِنَّ ٱللَّهَ سَمِيعُۢ بَصِيرٞ

Allah Yana zavar manzanni daga mala’iku kuma daga mutane. Lalle Allah Mai ji ne, Mai gani



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 76

يَعۡلَمُ مَا بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَمَا خَلۡفَهُمۡۚ وَإِلَى ٱللَّهِ تُرۡجَعُ ٱلۡأُمُورُ

Yana sane da abin da yake gabansu da abin da yake bayansu. Zuwa ga Allah ne kawai ake komar da al’amura



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 77

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱرۡكَعُواْ وَٱسۡجُدُواْۤ وَٱعۡبُدُواْ رَبَّكُمۡ وَٱفۡعَلُواْ ٱلۡخَيۡرَ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ۩

Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi ruku’i kuma ku yi sujjada, ku kuma bauta wa Ubangijinku, kuma ku aikata alheri don ku rabauta



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 78

وَجَٰهِدُواْ فِي ٱللَّهِ حَقَّ جِهَادِهِۦۚ هُوَ ٱجۡتَبَىٰكُمۡ وَمَا جَعَلَ عَلَيۡكُمۡ فِي ٱلدِّينِ مِنۡ حَرَجٖۚ مِّلَّةَ أَبِيكُمۡ إِبۡرَٰهِيمَۚ هُوَ سَمَّىٰكُمُ ٱلۡمُسۡلِمِينَ مِن قَبۡلُ وَفِي هَٰذَا لِيَكُونَ ٱلرَّسُولُ شَهِيدًا عَلَيۡكُمۡ وَتَكُونُواْ شُهَدَآءَ عَلَى ٱلنَّاسِۚ فَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَٱعۡتَصِمُواْ بِٱللَّهِ هُوَ مَوۡلَىٰكُمۡۖ فَنِعۡمَ ٱلۡمَوۡلَىٰ وَنِعۡمَ ٱلنَّصِيرُ

Kuma ku yi jihadi wajen (xaukaka addinin) Allah iyakar iyawarku. Shi ne Ya zave ku, bai kuma sanya muku wani qunci ba cikin addini. Addinin Babanku ne Ibrahimu. (Allah) Shi ne Ya kira ku Musulmi tuntuni, da kuma cikin wannan (Alqur’ani) don Manzo ya zama shaida a gare ku, ku kuma ku zama shaida ga (sauran) mutane. To sai ku tsai da salla kuma ku ba da zakka, ku kuma yi riqo da (addinin) Allah, Shi ne Majivincin al’amarinku; to madalla da Majivinci, kuma madalla da Mataimaki