Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 31

قَالُواْ يَٰوَيۡلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَٰغِينَ

Suka ce: “Kaiconmu, lalle mu mun kasance masu shisshigi



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 32

عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبۡدِلَنَا خَيۡرٗا مِّنۡهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ

“Tsammanin Ubangijinmu zai musanya mana wadda ta fi ta, lalle mu masu kwaxayi ne a wurin Ubangijinmu[1].”


1- Watau zai ba su wata gonar da ta fi tasu, suna kuma fatan zai yi musu afuwa ya yafe musu kurakuransu.


Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 33

كَذَٰلِكَ ٱلۡعَذَابُۖ وَلَعَذَابُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَكۡبَرُۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Kamar haka ne azaba take tabbata; kuma tabbas azabar lahira ta fi girma. Da sun kasance sun san haka



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 34

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Lalle masu taqawa suna da gidajen Aljannar ni’ima a wurin Ubangijinsu



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 35

أَفَنَجۡعَلُ ٱلۡمُسۡلِمِينَ كَٱلۡمُجۡرِمِينَ

Yanzu za Mu sanya Musulmi kamar kangararru?



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 36

مَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ

Me ya same ku ne, yaya kuke irin wannan hukuncin?



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 37

أَمۡ لَكُمۡ كِتَٰبٞ فِيهِ تَدۡرُسُونَ

Ko kuna da wani littafi ne wanda a cikinsa kuke karantawa?



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 38

إِنَّ لَكُمۡ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ

(Cewa) a cikinsa lalle kuna da abin da kuke zava?



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 39

أَمۡ لَكُمۡ أَيۡمَٰنٌ عَلَيۡنَا بَٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ إِنَّ لَكُمۡ لَمَا تَحۡكُمُونَ

Ko kuwa kuna da wasu alqawura na rantsuwa ne (tabbatattu) a kanmu har zuwa ranar alqiyama cewa, lalle kuna da abin da kuke hukunta wa (kanku)?



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 40

سَلۡهُمۡ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ

Ka tambaye su wane ne a cikinsu ya yi lamuni game da wannan?



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 41

أَمۡ لَهُمۡ شُرَكَآءُ فَلۡيَأۡتُواْ بِشُرَكَآئِهِمۡ إِن كَانُواْ صَٰدِقِينَ

Ko kuwa suna da wasu ababan tarayya ne? To su kawo ababan tarayyar tasu idan sun kasance masu gaskiya



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 42

يَوۡمَ يُكۡشَفُ عَن سَاقٖ وَيُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسۡتَطِيعُونَ

(Ka tuna) ranar da za a yaye qwauri[1] a kuma kirawo su zuwa yin sujjada sannan su rasa ikon yi


1- Watau ranar da Allah () zai kware qwaurinsa mai daraja wanda bai yi kama da wani abu na halittarsa ba.


Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 43

خَٰشِعَةً أَبۡصَٰرُهُمۡ تَرۡهَقُهُمۡ ذِلَّةٞۖ وَقَدۡ كَانُواْ يُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمۡ سَٰلِمُونَ

Idanuwansu a qasqance, wulaqanci ya lulluve su. Haqiqa kuwa a duniya sun kasance ana kiran su zuwa yin sujjada alhali suna lafiyayyu



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 44

فَذَرۡنِي وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا ٱلۡحَدِيثِۖ سَنَسۡتَدۡرِجُهُم مِّنۡ حَيۡثُ لَا يَعۡلَمُونَ

Saboda haka ka bar Ni da wanda yake qaryata wannan Alqur’ani; ba da daxewa ba za Mu yi musu talala ta inda ba za su sani ba



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 45

وَأُمۡلِي لَهُمۡۚ إِنَّ كَيۡدِي مَتِينٌ

Kuma zan saurara musu. Lalle kaidina mai qarfi ne



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 46

أَمۡ تَسۡـَٔلُهُمۡ أَجۡرٗا فَهُم مِّن مَّغۡرَمٖ مُّثۡقَلُونَ

Ko kuwa kana tambayar su wani lada ne, saboda haka biyan (wannan lada) ya yi musu nauyi?



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 47

أَمۡ عِندَهُمُ ٱلۡغَيۡبُ فَهُمۡ يَكۡتُبُونَ

Ko kuwa sanin gaibu a wurinsu yake, saboda haka suke rubuto shi?



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 48

فَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلۡحُوتِ إِذۡ نَادَىٰ وَهُوَ مَكۡظُومٞ

To ka yi haquri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar ma’abocin kifi (Yunus) a yayin da ya yi kira, alhali shi yana cike da baqin ciki



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 49

لَّوۡلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعۡمَةٞ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ مَذۡمُومٞ

Ba don wata rahama daga Ubangijinsa ta riske shi ba, da an jefar da shi a qungurmin daji alhali shi yana abin suka



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 50

فَٱجۡتَبَٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Sai Ubangijinsa Ya zave shi Ya sanya shi daga (bayi) nagari



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 51

وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَيُزۡلِقُونَكَ بِأَبۡصَٰرِهِمۡ لَمَّا سَمِعُواْ ٱلذِّكۡرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجۡنُونٞ

Lalle kuma waxanda suka kafirta sun yi kusa su kayar da kai da kallonsu yayin da suka ji Alqur’ani, suka kuma riqa cewa: “Lalle shi tabbas mahaukaci ne!”



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 52

وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ

Shi kuwa (Alqur’ani) ba wani abu ba ne face gargaxi ga talikai