Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 1

عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ

Game da me suke tambayar junansu?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 2

عَنِ ٱلنَّبَإِ ٱلۡعَظِيمِ

Game da labari ne mai girma[1]


1- Watau Alqur’ani wanda ya qunshi magana a kan ranar alqiyama da za a yi wa mutane hisabi a ciki.


Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 3

ٱلَّذِي هُمۡ فِيهِ مُخۡتَلِفُونَ

Wanda game da shi ne suke savani



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 4

كَلَّا سَيَعۡلَمُونَ

Ba haka ne ba, da sannu za su sani[1]


1- Watau za su san mummunan sakamakon qaryata shi da suke yi.


Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 5

ثُمَّ كَلَّا سَيَعۡلَمُونَ

Sannan kuma tabbas, da sannu za su sani



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 6

أَلَمۡ نَجۡعَلِ ٱلۡأَرۡضَ مِهَٰدٗا

Yanzu ba mu sanya qasa shimfixa ba?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 7

وَٱلۡجِبَالَ أَوۡتَادٗا

Duwatsu kuma turaku?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 8

وَخَلَقۡنَٰكُمۡ أَزۡوَٰجٗا

Muka kuma halicce ku bibbiyu (watau maza da mata)?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 9

وَجَعَلۡنَا نَوۡمَكُمۡ سُبَاتٗا

Muka kuma sanya baccinku (ya zama) hutu?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 10

وَجَعَلۡنَا ٱلَّيۡلَ لِبَاسٗا

Muka kuma sanya dare (ya zama) sutura[1]?


1- Watau idan ya lulluve da duhunsa.


Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 11

وَجَعَلۡنَا ٱلنَّهَارَ مَعَاشٗا

Muka kuma sanya yini don neman abinci?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 12

وَبَنَيۡنَا فَوۡقَكُمۡ سَبۡعٗا شِدَادٗا

Muka kuma gina (sammai) bakwai qarfafa a sama da ku?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 13

وَجَعَلۡنَا سِرَاجٗا وَهَّاجٗا

Muka kuma sanya wata fitila mai tsananin haske (watau rana)?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 14

وَأَنزَلۡنَا مِنَ ٱلۡمُعۡصِرَٰتِ مَآءٗ ثَجَّاجٗا

Muka kuma saukar da ruwa mai kwarara daga (hadari) da ya batse da ruwa?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 15

لِّنُخۡرِجَ بِهِۦ حَبّٗا وَنَبَاتٗا

Domin Mu fitar da qwayoyi da tsirrai da shi?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 16

وَجَنَّـٰتٍ أَلۡفَافًا

Da kuma gonaki masu itatuwa sassarqe da juna?



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 17

إِنَّ يَوۡمَ ٱلۡفَصۡلِ كَانَ مِيقَٰتٗا

Lalle ranar hukunci ta kasance (rana ce) mai tsayayyen lokaci



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 18

يَوۡمَ يُنفَخُ فِي ٱلصُّورِ فَتَأۡتُونَ أَفۡوَاجٗا

Ranar da za a busa qaho[1] sai ku zo jama’a-jama’a


1- Watau busa ta biyu.


Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 19

وَفُتِحَتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتۡ أَبۡوَٰبٗا

Aka kuma buxe sama sai ta zama qofofi[1]


1- Watau inda mala’iku za su yi ta sauka da umarnin Allah.


Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 20

وَسُيِّرَتِ ٱلۡجِبَالُ فَكَانَتۡ سَرَابًا

Aka kuma tafiyar da duwatsu sai suka zama kawalwalniya



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 21

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتۡ مِرۡصَادٗا

Lalle Jahannama ta kasance madakata ce



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 22

لِّلطَّـٰغِينَ مَـَٔابٗا

Makoma ce ga masu xagawa



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 23

لَّـٰبِثِينَ فِيهَآ أَحۡقَابٗا

Masu zama ne a cikinta shekaru aru-aru



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 24

لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرۡدٗا وَلَا شَرَابًا

Ba sa xanxanar wani sanyi a cikinta ko wani abin sha



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 25

إِلَّا حَمِيمٗا وَغَسَّاقٗا

Sai tafasasshen ruwa da ruwan mugunya



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 26

جَزَآءٗ وِفَاقًا

Don sakayya da ta dace



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 27

إِنَّهُمۡ كَانُواْ لَا يَرۡجُونَ حِسَابٗا

Lalle su sun kasance ba sa tsoron hisabi



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 28

وَكَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا كِذَّابٗا

Suka kuma qaryata ayoyinmu iyakar qaryatawa



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 29

وَكُلَّ شَيۡءٍ أَحۡصَيۡنَٰهُ كِتَٰبٗا

Kuma kowane abu Mun qididdige shi a rubuce



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 30

فَذُوقُواْ فَلَن نَّزِيدَكُمۡ إِلَّا عَذَابًا

(Sai a ce da su): To ku xanxana, don ba za Mu qara muku ba sai dai wata azaba.”