Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 1

نٓۚ وَٱلۡقَلَمِ وَمَا يَسۡطُرُونَ

NUN[1]. (Allah ya ce): Na rantse da alqalami da abin da (mala’iku) suke rubutawa


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 2

مَآ أَنتَ بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ بِمَجۡنُونٖ

Kai ba mahaukaci ba ne saboda ni’imar Ubangijinka



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 3

وَإِنَّ لَكَ لَأَجۡرًا غَيۡرَ مَمۡنُونٖ

Kuma lalle tabbas kana da lada marar yankewa



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 4

وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٖ

Lalle kuma kai kana kan halaye masu girma



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 5

فَسَتُبۡصِرُ وَيُبۡصِرُونَ

To ba da daxewa ba za ka gani, su ma kuma su gani



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 6

بِأَييِّكُمُ ٱلۡمَفۡتُونُ

Wane ne daga cikinku mahaukaci?



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 7

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ

Lalle Ubangijinka Shi Ya fi sanin wanda ya kauce wa hanyarsa kuma Shi Ya fi sanin shiryayyu



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 8

فَلَا تُطِعِ ٱلۡمُكَذِّبِينَ

Saboda haka kada ka bi masu qaryatawa



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 9

وَدُّواْ لَوۡ تُدۡهِنُ فَيُدۡهِنُونَ

Sun yi burin da za ka sassauto, sai su ma su sassauto[1]


1- Watau ya daina aibata gumakansu da bautarsu, sai su ma su daina sukan sa da addininsa.


Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 10

وَلَا تُطِعۡ كُلَّ حَلَّافٖ مَّهِينٍ

Kada kuma ka bi duk wani mai yawan rantsuwa, wulaqantacce



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 11

هَمَّازٖ مَّشَّآءِۭ بِنَمِيمٖ

Mai yawan yin zunxe, mai yawan yawo da annamimanci



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 12

مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ

Mai yawan hana alheri, mai ta’addanci, mai yawan savo



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 13

عُتُلِّۭ بَعۡدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ

Mai busasshiyar zuciya, bayan wannan kuma marar asali ne



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 14

أَن كَانَ ذَا مَالٖ وَبَنِينَ

Don ya kasance mai dukiya da ‘ya’ya



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 15

إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan ana karanta masa ayoyinmu sai ya ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko ne.”



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 16

سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلۡخُرۡطُومِ

Ba da daxewa ba za Mu yi masa alama a kan hancinsa



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 17

إِنَّا بَلَوۡنَٰهُمۡ كَمَا بَلَوۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ إِذۡ أَقۡسَمُواْ لَيَصۡرِمُنَّهَا مُصۡبِحِينَ

Lalle Mu Mun jarrabe su (wato mutanen Makka) kamar yadda Muka jarrabi ma’abota gona, lokacin da suka rantse cewa, lalle tabbas za su girbe ta da asussuba



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 18

وَلَا يَسۡتَثۡنُونَ

Ba sa kuma togaciya (da faxar insha Allah)



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 19

فَطَافَ عَلَيۡهَا طَآئِفٞ مِّن رَّبِّكَ وَهُمۡ نَآئِمُونَ

Sai wani bala’i daga Ubangijinka ya kewaye ta alhali su suna bacci



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 20

فَأَصۡبَحَتۡ كَٱلصَّرِيمِ

Sai ta wayi gari (baqi qirin) kamar duhun dare



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 21

فَتَنَادَوۡاْ مُصۡبِحِينَ

Sai suka kirawo junansu da asussuba



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 22

أَنِ ٱغۡدُواْ عَلَىٰ حَرۡثِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰرِمِينَ

Cewa: “Ku yi sammako ga amfanin gonarku idan kun kasance masu yin girbi.”



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 23

فَٱنطَلَقُواْ وَهُمۡ يَتَخَٰفَتُونَ

Sai suka tafi alhali suna yi wa junansu raxa



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 24

أَن لَّا يَدۡخُلَنَّهَا ٱلۡيَوۡمَ عَلَيۡكُم مِّسۡكِينٞ

Cewa: “Lalle a yau kada wani miskini ya shigar muku cikinta.”



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 25

وَغَدَوۡاْ عَلَىٰ حَرۡدٖ قَٰدِرِينَ

Suka kuwa yi sammako suna masu zaton su masu iko ne a kan hana (mabuqata)



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 26

فَلَمَّا رَأَوۡهَا قَالُوٓاْ إِنَّا لَضَآلُّونَ

To lokacin da suka gan ta sai suka ce: “Lalle mu tabbas mun yi vatan kai



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 27

بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ

“A’a, mu dai an hana mu ne kawai.”



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 28

قَالَ أَوۡسَطُهُمۡ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ لَوۡلَا تُسَبِّحُونَ

Sai wanda ya fi su kirki ya ce: “Ban gaya muku ya kamata ku tsarkake Allah ba?”



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 29

قَالُواْ سُبۡحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

Suka ce, “Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu, lalle mu mun kasance azzalumai.”



Capítulo: Suratul Qalam

Verso : 30

فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَلَٰوَمُونَ

Sai sashinsu ya fuskanci sashi suna zargin juna