Capítulo: Suratux Xur

Verso : 1

وَٱلطُّورِ

Na rantse da dutsen Xuri



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 2

وَكِتَٰبٖ مَّسۡطُورٖ

Da kuma rubutaccen littafi



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 3

فِي رَقّٖ مَّنشُورٖ

Cikin buxaxxiyar takardar fata



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 4

وَٱلۡبَيۡتِ ٱلۡمَعۡمُورِ

Da kuma Al-Baitul-Ma’amur[1]


1- Shi ne xakin da ke a sama ta bakwai, wanda a koyaushe dandazon mala’iku suke raya shi da bautar Allah.


Capítulo: Suratux Xur

Verso : 5

وَٱلسَّقۡفِ ٱلۡمَرۡفُوعِ

Da kuma rufi abin xaukakawa[1]


1- Watau sama abar xaukakawa kamar rufi.


Capítulo: Suratux Xur

Verso : 6

وَٱلۡبَحۡرِ ٱلۡمَسۡجُورِ

Da kuma kogi cikakke maqil



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 7

إِنَّ عَذَابَ رَبِّكَ لَوَٰقِعٞ

Lalle azabar Ubangijinka tabbas mai aukuwa ce



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 8

مَّا لَهُۥ مِن دَافِعٖ

Ba wani mai ingije ta



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 9

يَوۡمَ تَمُورُ ٱلسَّمَآءُ مَوۡرٗا

A ranar da sama za ta yi matsananciyar jujjuyawa



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 10

وَتَسِيرُ ٱلۡجِبَالُ سَيۡرٗا

Duwatsu kuma su riqa tafiya (suna barin wurarensu)



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 11

فَوَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

To tsananin azaba a wanan ranar ya tabbata ga masu qaryatawa



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 12

ٱلَّذِينَ هُمۡ فِي خَوۡضٖ يَلۡعَبُونَ

Waxanda suke wasanni cikin varna



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 13

يَوۡمَ يُدَعُّونَ إِلَىٰ نَارِ جَهَنَّمَ دَعًّا

A ranar da za a ingiza su zuwa ga wutar Jahannama ingizawa



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 14

هَٰذِهِ ٱلنَّارُ ٱلَّتِي كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ

(Za a ce da su): “Wannan ita ce wutar da kuka kasance kuna qaryatawa



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 15

أَفَسِحۡرٌ هَٰذَآ أَمۡ أَنتُمۡ لَا تُبۡصِرُونَ

“Yanzu sihiri ne wannan ko kuwa ku ne ba kwa gani?



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 16

ٱصۡلَوۡهَا فَٱصۡبِرُوٓاْ أَوۡ لَا تَصۡبِرُواْ سَوَآءٌ عَلَيۡكُمۡۖ إِنَّمَا تُجۡزَوۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

“To ku shige ta, sai ku yi haquri ko kada ku yi haquri duk xaya ne; ana saka muku ne kawai da abin da kuka kasance kuna aikatawa.”



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 17

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَنَعِيمٖ

Lalle masu tsoron Allah suna cikin gidajen Aljanna da ni’ima



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 18

فَٰكِهِينَ بِمَآ ءَاتَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡ وَوَقَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡ عَذَابَ ٱلۡجَحِيمِ

Suna masu more abin da Ubangijisu Ya ba su, Ubangijinsu kuma Ya tserar da su daga azabar Jahima



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 19

كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ هَنِيٓـَٔۢا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Ku ci ku sha cikin jin xaxi saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 20

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ سُرُرٖ مَّصۡفُوفَةٖۖ وَزَوَّجۡنَٰهُم بِحُورٍ عِينٖ

Kuna masu kishingixa a kan gadaje waxanda aka jera su sahu-sahu; Muka kuma aura musu ‘yan matan Hurul-Ini



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 21

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱتَّبَعَتۡهُمۡ ذُرِّيَّتُهُم بِإِيمَٰنٍ أَلۡحَقۡنَا بِهِمۡ ذُرِّيَّتَهُمۡ وَمَآ أَلَتۡنَٰهُم مِّنۡ عَمَلِهِم مِّن شَيۡءٖۚ كُلُّ ٱمۡرِيِٕۭ بِمَا كَسَبَ رَهِينٞ

Waxanda kuwa suka yi imani, zuriyarsu kuma suka bi su a imani, za Mu haxa su da zuriyarsu[1], ba kuma za Mu tauye musu komai ba na aikinsu. Kowane mutum jingina ne ga abin da ya tsuwurwurta[2]


1- Watau sai Allah ya xaukaka darajar ‘ya’yansu don su haxu wuri guda a Aljanna, ko da kuwa ayyukan ‘ya’yan ba su kai na iyayen ba.


2- Watau ana tsare shi don abin da ya aikata kaxai, ba za a kama shi ne da laifin wani ba.


Capítulo: Suratux Xur

Verso : 22

وَأَمۡدَدۡنَٰهُم بِفَٰكِهَةٖ وَلَحۡمٖ مِّمَّا يَشۡتَهُونَ

Muka kuma daxe su da abin marmari da nama irin wanda suke sha’awa



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 23

يَتَنَٰزَعُونَ فِيهَا كَأۡسٗا لَّا لَغۡوٞ فِيهَا وَلَا تَأۡثِيمٞ

A cikinta (Aljannar) suna musayan kofuna na giya da babu wani zancen banza game da ita, kuma babu wani zunubi



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 24

۞وَيَطُوفُ عَلَيۡهِمۡ غِلۡمَانٞ لَّهُمۡ كَأَنَّهُمۡ لُؤۡلُؤٞ مَّكۡنُونٞ

Wasu yara nasu kuma waxanda suke kamar lu’u-lu’un da yake cikin kwasfa suna kaiwa da komowa a kansu



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 25

وَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَسَآءَلُونَ

Kuma shashinsu ya fuskanci shashi suna tambayar juna



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 26

قَالُوٓاْ إِنَّا كُنَّا قَبۡلُ فِيٓ أَهۡلِنَا مُشۡفِقِينَ

Suka ce: “Lalle sanda muke cikin iyalinmu (a duniya) kafin wannan, mun kasance masu tsoron azabar Allah



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 27

فَمَنَّ ٱللَّهُ عَلَيۡنَا وَوَقَىٰنَا عَذَابَ ٱلسَّمُومِ

“Sai Allah Ya yi mana baiwa ya kiyaye mu azabar wuta



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 28

إِنَّا كُنَّا مِن قَبۡلُ نَدۡعُوهُۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡبَرُّ ٱلرَّحِيمُ

“Lalle mu mun kasance a da can muna bauta masa; lalle shi Mai kyautatawa ne, Mai jin qai.”



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 29

فَذَكِّرۡ فَمَآ أَنتَ بِنِعۡمَتِ رَبِّكَ بِكَاهِنٖ وَلَا مَجۡنُونٍ

To ka yi wa’azi, don ba za ka zama boka ba ko mahaukaci saboda ni’imar Ubangijinka



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 30

أَمۡ يَقُولُونَ شَاعِرٞ نَّتَرَبَّصُ بِهِۦ رَيۡبَ ٱلۡمَنُونِ

A’a, cewa dai suka yi: “Shi mawaqi ne da muke saurara masa hanyar halaka.”