Capítulo: Suratu Yusuf 

Verso : 56

وَكَذَٰلِكَ مَكَّنَّا لِيُوسُفَ فِي ٱلۡأَرۡضِ يَتَبَوَّأُ مِنۡهَا حَيۡثُ يَشَآءُۚ نُصِيبُ بِرَحۡمَتِنَا مَن نَّشَآءُۖ وَلَا نُضِيعُ أَجۡرَ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Kamar haka ne Muka kafa Yusufu a bayan qasa; yana zama a cikinta inda ya ga dama. Muna bayar da rahamarmu ga wanda Muka ga dama, ba kuwa za Mu tozarta ladan masu kyautatawa ba



Capítulo: Suratu Yusuf 

Verso : 67

وَقَالَ يَٰبَنِيَّ لَا تَدۡخُلُواْ مِنۢ بَابٖ وَٰحِدٖ وَٱدۡخُلُواْ مِنۡ أَبۡوَٰبٖ مُّتَفَرِّقَةٖۖ وَمَآ أُغۡنِي عَنكُم مِّنَ ٱللَّهِ مِن شَيۡءٍۖ إِنِ ٱلۡحُكۡمُ إِلَّا لِلَّهِۖ عَلَيۡهِ تَوَكَّلۡتُۖ وَعَلَيۡهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُتَوَكِّلُونَ

Ya kuma ce: “Ya ‘ya’yana, kada ku shiga (Masar) ta qofa guda; ku shiga ta qofofi daban-daban[1]. Ba zan kare muku komai daga Allah ba; ba wani hukunci sai na Allah; a gare Shi na dogara, kuma a gare Shi ne masu dogaro ya wajaba su dogara.”


1- Domi kauce wa wata cutarwa da za ta iya fuskantar su, don kada ta same su gaba xayansu a lokaci guda.


Capítulo: Suratu Yusuf 

Verso : 100

وَرَفَعَ أَبَوَيۡهِ عَلَى ٱلۡعَرۡشِ وَخَرُّواْ لَهُۥ سُجَّدٗاۖ وَقَالَ يَـٰٓأَبَتِ هَٰذَا تَأۡوِيلُ رُءۡيَٰيَ مِن قَبۡلُ قَدۡ جَعَلَهَا رَبِّي حَقّٗاۖ وَقَدۡ أَحۡسَنَ بِيٓ إِذۡ أَخۡرَجَنِي مِنَ ٱلسِّجۡنِ وَجَآءَ بِكُم مِّنَ ٱلۡبَدۡوِ مِنۢ بَعۡدِ أَن نَّزَغَ ٱلشَّيۡطَٰنُ بَيۡنِي وَبَيۡنَ إِخۡوَتِيٓۚ إِنَّ رَبِّي لَطِيفٞ لِّمَا يَشَآءُۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡعَلِيمُ ٱلۡحَكِيمُ

Ya kuma xora mahaifansa a kan gadon mulki, suka kuma faxi suna masu gaisuwa a gare shi, ya kuma ce: “Ya babanmu, wannan shi ne fassarar mafarkina na tun tuni. Lalle Ubangijina Ya mai da shi gaskiya; haqiqa kuma Ya kyautata min lokacin da Ya fitar da ni daga kurkuku, Ya kuma zo da ku daga qauye bayan Shaixan ya shiga tsakanina da ‘yan’uwana. Lalle Ubangijina Mai tausasawa ne ga wanda Ya ga dama. Lalle Shi ne Masani, Mai hikima



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 6

وَيَسۡتَعۡجِلُونَكَ بِٱلسَّيِّئَةِ قَبۡلَ ٱلۡحَسَنَةِ وَقَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلِهِمُ ٱلۡمَثُلَٰتُۗ وَإِنَّ رَبَّكَ لَذُو مَغۡفِرَةٖ لِّلنَّاسِ عَلَىٰ ظُلۡمِهِمۡۖ وَإِنَّ رَبَّكَ لَشَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Suna kuma nemanka da gaggauto musu da azaba tun kafin (su nemi) kyakkyawa (wato rahamar Allah), alhali kuwa haqiqa misalai (na waxanda aka halakar) a gabansu sun wuce. Lalle kuma Ubangijinka Ma’abocin gafara ne ga mutane a kan laifuffukansu, kuma lalle Ubangijinka tabbas Mai tsananin azaba ne



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 8

ٱللَّهُ يَعۡلَمُ مَا تَحۡمِلُ كُلُّ أُنثَىٰ وَمَا تَغِيضُ ٱلۡأَرۡحَامُ وَمَا تَزۡدَادُۚ وَكُلُّ شَيۡءٍ عِندَهُۥ بِمِقۡدَارٍ

Allah Yana sane da abin da (mahaifar) kowace mace take xauke da shi da kuma abin da mahaifa take ragewa da wanda take qarawa[1]; kowane abu kuma a wurinsa yana da gwargwado


1- Watau ana nufin lokacin haihuwarta, ko dai ta haihu kafin cikar wata tara, ko ta haihu bayan cikar wa’adin cikinta, ko xan ya zo cikakke da qoshin lafiya, ko kuma da wata nakasa ko rashin lafiya.


Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 9

عَٰلِمُ ٱلۡغَيۡبِ وَٱلشَّهَٰدَةِ ٱلۡكَبِيرُ ٱلۡمُتَعَالِ

(Shi) Masanin abin da ke voye da na sarari ne, Mai girma, Mai cikar xaukaka



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 11

لَهُۥ مُعَقِّبَٰتٞ مِّنۢ بَيۡنِ يَدَيۡهِ وَمِنۡ خَلۡفِهِۦ يَحۡفَظُونَهُۥ مِنۡ أَمۡرِ ٱللَّهِۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُغَيِّرُ مَا بِقَوۡمٍ حَتَّىٰ يُغَيِّرُواْ مَا بِأَنفُسِهِمۡۗ وَإِذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِقَوۡمٖ سُوٓءٗا فَلَا مَرَدَّ لَهُۥۚ وَمَا لَهُم مِّن دُونِهِۦ مِن وَالٍ

(Kowanensu) yana da (mala’iku) masu take masa baya a gabansa da kuma bayansa suna kiyaye shi da umarnin Allah. Lalle Allah ba Ya canja abin da mutane suke ciki har sai sun canja halayensu. Idan kuma Allah Ya yi nufin wata azaba ga mutane, to ba mai juyar da ita, ba su kuwa da wani mai jivintar su wanda ba Shi ba



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 16

قُلۡ مَن رَّبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ قُلِ ٱللَّهُۚ قُلۡ أَفَٱتَّخَذۡتُم مِّن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَ لَا يَمۡلِكُونَ لِأَنفُسِهِمۡ نَفۡعٗا وَلَا ضَرّٗاۚ قُلۡ هَلۡ يَسۡتَوِي ٱلۡأَعۡمَىٰ وَٱلۡبَصِيرُ أَمۡ هَلۡ تَسۡتَوِي ٱلظُّلُمَٰتُ وَٱلنُّورُۗ أَمۡ جَعَلُواْ لِلَّهِ شُرَكَآءَ خَلَقُواْ كَخَلۡقِهِۦ فَتَشَٰبَهَ ٱلۡخَلۡقُ عَلَيۡهِمۡۚ قُلِ ٱللَّهُ خَٰلِقُ كُلِّ شَيۡءٖ وَهُوَ ٱلۡوَٰحِدُ ٱلۡقَهَّـٰرُ

Ka ce (da su): “Wane ne Ubangijin sammai da qasa?” Ka ce: “Allah ne”. Ka ce (da su): “Amma yaya kuka riqi wasu iyayen giji ba Shi ba su zama majivinta (gare ku), ba sa mallakar wani amfani ko cuta ga kansu?” Ka ce: “Shin makaho da mai gani za su yi daidai, ko kuwa shin duhu da haske za su yi daidai? Ko sun sanya wa Allah wasu abokan tarayya ne waxanda suka yi halitta kamar halittarsa, sai halittar ta yi musu kama da juna?” Ka ce: “Allah ne Mahaliccin komai, kuma Shi ne Makaxaici, Mai rinjaye.”



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 26

ٱللَّهُ يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ وَيَقۡدِرُۚ وَفَرِحُواْ بِٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَمَا ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا فِي ٱلۡأٓخِرَةِ إِلَّا مَتَٰعٞ

Allah ne Yake shimfixa arziki ga wanda Ya ga dama, Yake kuma quntatawa (ga wanda Ya ga dama. (Kafirai) kuma sun yi farin ciki da rayuwar duniya, rayuwar duniya kuwa ba komai ba ce illa xan jin daxi kaxan dangane da na lahira



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 27

وَيَقُولُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَوۡلَآ أُنزِلَ عَلَيۡهِ ءَايَةٞ مِّن رَّبِّهِۦۚ قُلۡ إِنَّ ٱللَّهَ يُضِلُّ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِيٓ إِلَيۡهِ مَنۡ أَنَابَ

Waxanda suka kafirta kuma suna cewa: “Me ya hana a saukar masa da aya daga Ubangijinsa?” Ka ce: “Lalle Allah Yana vatar da wanda Ya ga dama, Yana kuma shiryar da wanda ya koma gare Shi



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 28

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَتَطۡمَئِنُّ قُلُوبُهُم بِذِكۡرِ ٱللَّهِۗ أَلَا بِذِكۡرِ ٱللَّهِ تَطۡمَئِنُّ ٱلۡقُلُوبُ

“(Su ne) waxanda suka yi imani, zukatansu kuma suna nutsuwa da ambaton Allah. Ku saurara, da ambaton Allah ne zukata suke nutsuwa



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 30

كَذَٰلِكَ أَرۡسَلۡنَٰكَ فِيٓ أُمَّةٖ قَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلِهَآ أُمَمٞ لِّتَتۡلُوَاْ عَلَيۡهِمُ ٱلَّذِيٓ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ وَهُمۡ يَكۡفُرُونَ بِٱلرَّحۡمَٰنِۚ قُلۡ هُوَ رَبِّي لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ عَلَيۡهِ تَوَكَّلۡتُ وَإِلَيۡهِ مَتَابِ

Kamar haka Muka aiko ka cikin al’umma wadda tuni wasu al’ummun sun wuce kafinta, don ka karanta musu abin da Muka yi maka wahayinsa, alhali kuwa su suna kafirce wa Arrahamanu[1]. Ka ce: “Shi ne Ubangijina, babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi, gare Shi kawai na dogara, kuma gare Shi kawai tubata take.”


1- Kafiran Quraishawa suna qyamar su siffanta Allah da suna Arrahman, watau Mai rahma, kamar yadda ya zo a cikin Suratul Furqan aya ta 60.


Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 37

وَكَذَٰلِكَ أَنزَلۡنَٰهُ حُكۡمًا عَرَبِيّٗاۚ وَلَئِنِ ٱتَّبَعۡتَ أَهۡوَآءَهُم بَعۡدَ مَا جَآءَكَ مِنَ ٱلۡعِلۡمِ مَا لَكَ مِنَ ٱللَّهِ مِن وَلِيّٖ وَلَا وَاقٖ

Kamar haka Muka saukar da shi (Alqur’ani), ya zama hukunci, da harshen Larabci. Lalle kuma idan ka bi son ransu bayan abin da ya zo maka na ilimi, to ba ka da wani majivinci ko mai kariya daga (azabar) Allah



Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 42

وَقَدۡ مَكَرَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ فَلِلَّهِ ٱلۡمَكۡرُ جَمِيعٗاۖ يَعۡلَمُ مَا تَكۡسِبُ كُلُّ نَفۡسٖۗ وَسَيَعۡلَمُ ٱلۡكُفَّـٰرُ لِمَنۡ عُقۡبَى ٱلدَّارِ

Haqiqa kuma waxanda suke gabaninsu sun qulla makirci, (sakamakon) qulle-qulle dukkaninsa ga Allah yake; Yana sane da abin da kowane rai yake aikatawa. Ba da daxewa ba kuma kafirai za su san wane ne mai kyakkyawan gidan (qarshe)



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 10

۞قَالَتۡ رُسُلُهُمۡ أَفِي ٱللَّهِ شَكّٞ فَاطِرِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ يَدۡعُوكُمۡ لِيَغۡفِرَ لَكُم مِّن ذُنُوبِكُمۡ وَيُؤَخِّرَكُمۡ إِلَىٰٓ أَجَلٖ مُّسَمّٗىۚ قَالُوٓاْ إِنۡ أَنتُمۡ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا تُرِيدُونَ أَن تَصُدُّونَا عَمَّا كَانَ يَعۡبُدُ ءَابَآؤُنَا فَأۡتُونَا بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ

Mazanninsu suka ce: “Yanzu kuwa ashe akwai wata shakka game da Allah, Maqagin sammai da qasa? Yana kiran ku ne don ya gafarta muku zunubanku kuma ya saurara muku har zuwa wani lokaci qayyadajje.” Suka ce: “Ku ba wasu ba ne daban in ban da mutane kamar mu, kuna so ne ku hana mu bin abin da iyanenmu suka kasance suna bauta wa, to sai ku kawo mana hujjoji bayyanannu.”



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 11

قَالَتۡ لَهُمۡ رُسُلُهُمۡ إِن نَّحۡنُ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُكُمۡ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ يَمُنُّ عَلَىٰ مَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦۖ وَمَا كَانَ لَنَآ أَن نَّأۡتِيَكُم بِسُلۡطَٰنٍ إِلَّا بِإِذۡنِ ٱللَّهِۚ وَعَلَى ٱللَّهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ

Manzanninsu suka ce: “Mu ba kowa ba ne in ban da mutane kamarku, sai dai Allah Yana yin baiwa ga wanda Ya ga dama ne daga bayinsa, kuma ba zai yiwu ba a gare mu mu zo muku da wata hujja sai dai da izinin Allah. Muminai kuwa lalle su dogara ga Allah kawai



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 12

وَمَا لَنَآ أَلَّا نَتَوَكَّلَ عَلَى ٱللَّهِ وَقَدۡ هَدَىٰنَا سُبُلَنَاۚ وَلَنَصۡبِرَنَّ عَلَىٰ مَآ ءَاذَيۡتُمُونَاۚ وَعَلَى ٱللَّهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُتَوَكِّلُونَ

“Kuma me zai hana mu mu dogara ga Allah, alhali kuwa haqiqa Ya shiryar da mu hanyoyinmu? Lalle kuwa tabbas za mu yi haquri bisa irin cutar mu da kuka yi. Masu dogaro kuma sai su dogara ga Allah kaxai.”



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 19

أَلَمۡ تَرَ أَنَّ ٱللَّهَ خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۚ إِن يَشَأۡ يُذۡهِبۡكُمۡ وَيَأۡتِ بِخَلۡقٖ جَدِيدٖ

Ashe ba ka ga cewa, lalle Allah Ya halicci sammai da qasa kan gaskiya ba? Idan Ya ga dama sai Ya hallakar da ku Ya kuma zo da wata halitta sabuwa



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 27

يُثَبِّتُ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱلۡقَوۡلِ ٱلثَّابِتِ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَفِي ٱلۡأٓخِرَةِۖ وَيُضِلُّ ٱللَّهُ ٱلظَّـٰلِمِينَۚ وَيَفۡعَلُ ٱللَّهُ مَا يَشَآءُ

Allah Yana tabbatar da waxanda suka yi imani a kan magana tabbatacciya a rayuwar duniya da kuma a lahira; Yana kuma vatar da azzalumai. Allah kuma Yana aikata abin da Ya ga dama



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 32

ٱللَّهُ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَأَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَأَخۡرَجَ بِهِۦ مِنَ ٱلثَّمَرَٰتِ رِزۡقٗا لَّكُمۡۖ وَسَخَّرَ لَكُمُ ٱلۡفُلۡكَ لِتَجۡرِيَ فِي ٱلۡبَحۡرِ بِأَمۡرِهِۦۖ وَسَخَّرَ لَكُمُ ٱلۡأَنۡهَٰرَ

Allah ne Wanda Ya halicci sammai da qasa, Ya kuma saukar da ruwa daga sama, sai Ya fitar da ‘ya’yan itace don arzuta ku; Ya kuma hore muku jiragen ruwa don ku yi tafiya a cikin kogi da umarninsa, Ya kuma hore muku qoramu



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 34

وَءَاتَىٰكُم مِّن كُلِّ مَا سَأَلۡتُمُوهُۚ وَإِن تَعُدُّواْ نِعۡمَتَ ٱللَّهِ لَا تُحۡصُوهَآۗ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَظَلُومٞ كَفَّارٞ

Ya kuma ba ku daga duk abin da kuka roqe Shi. In da za ku qirga ni’imomin Allah to ba za ku iya qididdige su ba. Lalle mutum mai yawan zalunci ne mai yawan butulci



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 38

رَبَّنَآ إِنَّكَ تَعۡلَمُ مَا نُخۡفِي وَمَا نُعۡلِنُۗ وَمَا يَخۡفَىٰ عَلَى ٱللَّهِ مِن شَيۡءٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا فِي ٱلسَّمَآءِ

“Ya Ubangijinmu, lalle Kai Ka san abin da muke voyewa da abin da muke bayyanawa. Babu wani abu a cikin qasa ko a cikin sama da zai vuya ga Allah



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 47

فَلَا تَحۡسَبَنَّ ٱللَّهَ مُخۡلِفَ وَعۡدِهِۦ رُسُلَهُۥٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَزِيزٞ ذُو ٱنتِقَامٖ

To kada ka yi tsammanin Allah Mai sava wa manzanninsa alqawarinsa ne. Lalle Allah Mabuwayi ne Ma’abocin uquba



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 52

هَٰذَا بَلَٰغٞ لِّلنَّاسِ وَلِيُنذَرُواْ بِهِۦ وَلِيَعۡلَمُوٓاْ أَنَّمَا هُوَ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞ وَلِيَذَّكَّرَ أُوْلُواْ ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Wannan (Alqur’ani) saqo ne ga mutane don kuma a gargaxe su da shi, kuma su san cewa Shi Allah Xaya ne, don kuma ma’abota hankali su wa’azantu



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 23

وَإِنَّا لَنَحۡنُ نُحۡيِۦ وَنُمِيتُ وَنَحۡنُ ٱلۡوَٰرِثُونَ

Lalle kuma tabbas Mu Muke rayawa kuma Muke kashewa, Mu ne kuma Masu gaje (komai)



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 24

وَلَقَدۡ عَلِمۡنَا ٱلۡمُسۡتَقۡدِمِينَ مِنكُمۡ وَلَقَدۡ عَلِمۡنَا ٱلۡمُسۡتَـٔۡخِرِينَ

Haqiqa kuma Mun san marigaya daga cikinku kuma haqiqa Mun san masu biyowa baya[1]


1- Watau Allah () ya san waxanda za a riga haihuwarsu su riga mutuwa, ya san kuma waxanda za a haife su, daga baya su mutu.


Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 26

وَلَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ مِن صَلۡصَٰلٖ مِّنۡ حَمَإٖ مَّسۡنُونٖ

Kuma haqiqa Mun halicci mutum daga busasshen tavo mai amo na wani yumvu mai wari



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 27

وَٱلۡجَآنَّ خَلَقۡنَٰهُ مِن قَبۡلُ مِن نَّارِ ٱلسَّمُومِ

Aljani kuwa Mun halicce shi ne gabanin (halittar mutum) daga wuta mai tsananin zafi



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 49

۞نَبِّئۡ عِبَادِيٓ أَنِّيٓ أَنَا ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Ka bai wa bayina labarin cewa lalle Ni, Ni ne Mai gafara, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 56

قَالَ وَمَن يَقۡنَطُ مِن رَّحۡمَةِ رَبِّهِۦٓ إِلَّا ٱلضَّآلُّونَ

Ya ce: “Ba wanda zai xebe qauna daga rahamar Ubangijinsa, sai vatattun (mutane).”