وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا
Qasar kuma ta fitar da nauyaye-nauyayenta[1]
1- Watau ta fitar da mutanen da ke cikinta da sauran ma’adanan qarqashinta.
Compartir :
وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا
Mutum kuma ya ce: “Me ya same ta?”
يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا
A wannan ranar ne za ta ba da labaranta[1]
1- Watau ayyukan da aka yi a kanta masu kyau da munana.
بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا
Don Ubangijinka Ya umarce ta (da yin haka)
يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ
A wannan ranar mutane za su fito a warwatse, don a nuna musu ayyukansu
فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ
To duk wanda ya yi aikin alheri daidai da zarra zai gan shi
وَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ شَرّٗا يَرَهُۥ
Wanda kuma duk ya yi aikin sharri daidai da zarra zai gan shi
۞أَفَلَا يَعۡلَمُ إِذَا بُعۡثِرَ مَا فِي ٱلۡقُبُورِ
Shin bai sani ba ne idan aka bankaxo abubuwan da suke cikin qaburbura?
وَحُصِّلَ مَا فِي ٱلصُّدُورِ
Aka kuma tattaro abubuwan da suke cikin qiraza?
إِنَّ رَبَّهُم بِهِمۡ يَوۡمَئِذٖ لَّخَبِيرُۢ
Lalle a wannan ranar tabbas Ubangijinsu Masani ne game da su
ٱلۡقَارِعَةُ
Mai qwanqwasa (zukata da tsoro)
مَا ٱلۡقَارِعَةُ
Mece ce mai qwanqwsa (zukata da tsoro)?
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡقَارِعَةُ
Kuma me ya sanar da kai mece ce mai qwanqwasa (zukata da tsoro)?
يَوۡمَ يَكُونُ ٱلنَّاسُ كَٱلۡفَرَاشِ ٱلۡمَبۡثُوثِ
(Ita ce) ranar da mutane za su zama kamar xangon fari masu bazuwa
وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ ٱلۡمَنفُوشِ
Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga[1]
1- Watau saboda rashin nauyinsu da warwatsuwarsu a cikin sararin sama.
فَأَمَّا مَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ
To amma wanda ma’aunan ayyukansa suka yi nauyi
فَهُوَ فِي عِيشَةٖ رَّاضِيَةٖ
To shi kam yana cikin rayuwa mai gamsarwa
وَأَمَّا مَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ
Amma kuma duk wanda ma’aunan ayyukansa suka yi shafal
فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٞ
To shi makomarsa (wutar) Hawiya ce
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا هِيَهۡ
Kuma me ya sanar da kai mece ce ita?
نَارٌ حَامِيَةُۢ
Wuta ce mai tsananin zafi