Capítulo: Suratul Haqqa

Verso : 15

فَيَوۡمَئِذٖ وَقَعَتِ ٱلۡوَاقِعَةُ

To a wannan rana ce mai afkuwa ta afku (watau alqiyama)



Capítulo: Suratul Haqqa

Verso : 16

وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِيَ يَوۡمَئِذٖ وَاهِيَةٞ

Sama kuma ta kekkece, don kuwa a wannan ranar ita mai rauni ce



Capítulo: Suratul Haqqa

Verso : 17

وَٱلۡمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرۡجَآئِهَاۚ وَيَحۡمِلُ عَرۡشَ رَبِّكَ فَوۡقَهُمۡ يَوۡمَئِذٖ ثَمَٰنِيَةٞ

Mala’iku kuma suna a sasanninta. A wannan ranar kuma (mala’iku) takwas za su xauki Al’arshin Ubangijinka a samansu



Capítulo: Suratul Haqqa

Verso : 18

يَوۡمَئِذٖ تُعۡرَضُونَ لَا تَخۡفَىٰ مِنكُمۡ خَافِيَةٞ

A wannan ranar ne kuma za a bujuro da ku, ba wani abu naku mai vuya



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 8

يَوۡمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلۡمُهۡلِ

A ranar da sama za ta kasance kamar narkakkiyar dalma



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 9

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga (ta gashin tumaki)



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 10

وَلَا يَسۡـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمٗا

Kuma aboki ba ya tambayar aboki



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 7

فَإِذَا بَرِقَ ٱلۡبَصَرُ

To lokacin da gani ya ruxe



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 8

وَخَسَفَ ٱلۡقَمَرُ

Wata kuma ya yi duhu



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 9

وَجُمِعَ ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ

Aka kuma haxe rana da wata (a mafitarsu)



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 10

يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ

A wannan rana ne mutum zai ce: “Ina wurin gudu?”



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 11

كَلَّا لَا وَزَرَ

Faufau, babu mafaka



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 12

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ

Zuwa ga Ubangijinka ne kawai matabbata take a wannan rana



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 13

يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ

Za a bai wa mutum labari a wannan rana na abin da ya gabatar da kuma (abin da) ya jinkirtar (na ayyukansa)



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 14

بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ

A’a, shi dai mutum mai shaida ne a kan kansa



Capítulo: Suratul Qiyama

Verso : 15

وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ

Ko da kuwa ya kawo uzururrukansa



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 17

إِنَّ يَوۡمَ ٱلۡفَصۡلِ كَانَ مِيقَٰتٗا

Lalle ranar hukunci ta kasance (rana ce) mai tsayayyen lokaci



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 18

يَوۡمَ يُنفَخُ فِي ٱلصُّورِ فَتَأۡتُونَ أَفۡوَاجٗا

Ranar da za a busa qaho[1] sai ku zo jama’a-jama’a


1- Watau busa ta biyu.


Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 19

وَفُتِحَتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتۡ أَبۡوَٰبٗا

Aka kuma buxe sama sai ta zama qofofi[1]


1- Watau inda mala’iku za su yi ta sauka da umarnin Allah.


Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 20

وَسُيِّرَتِ ٱلۡجِبَالُ فَكَانَتۡ سَرَابًا

Aka kuma tafiyar da duwatsu sai suka zama kawalwalniya



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 38

يَوۡمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ صَفّٗاۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنۡ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَقَالَ صَوَابٗا

Ranar da Jibrilu da mala’iku za su tsaya sahu-sahu; (halittu) ba sa iya magana sai fa wanda (Allah) Mai rahama Ya yi wa izini, ya kuma faxi abin da ya dace[1]


1- Watau kalmar tauhidi.


Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 39

ذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمُ ٱلۡحَقُّۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا

Wannan rana ce tabbatacciya; saboda haka wanda ya ga dama sai ya riqi kyakkyawar makoma zuwa ga Ubangijinsa



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 40

إِنَّآ أَنذَرۡنَٰكُمۡ عَذَابٗا قَرِيبٗا يَوۡمَ يَنظُرُ ٱلۡمَرۡءُ مَا قَدَّمَتۡ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلۡكَافِرُ يَٰلَيۡتَنِي كُنتُ تُرَٰبَۢا

Lalle Mun yi muku gargaxin azaba ta kurkusa, a ranar da mutum zai ga abin da hannayensa suka gabatar (na alheri ko na sharri), kafiri kuma ya riqa cewa: “Ina ma da na zama turvaya[1]!”


1- Watau kamar sauran dabbobi da za a ce musu su zama turvaya.


Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 34

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلۡكُبۡرَىٰ

Sannan idan mafi girman busar qaho ta zo (watau busa ta biyu)



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 35

يَوۡمَ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ

A ranar da mutum zai tuna abin da ya aikata



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 36

وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ

Aka kuma bayyana (wutar) Jahimu ga kowane mai gani



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 37

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ

To (a wannan ranar) duk wanda ya yi xagawa



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 38

وَءَاثَرَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا

Ya kuma fifita rayuwar duniya



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 39

فَإِنَّ ٱلۡجَحِيمَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle (wutar) Jahimu ita ce makoma



Capítulo: Suratun Nazi’at

Verso : 40

وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ

Duk wanda kuma ya ji tsoron tsayuwa gaban Ubangijinsa, ya kuma hana zuciya bin abin da take so