فِي مَقۡعَدِ صِدۡقٍ عِندَ مَلِيكٖ مُّقۡتَدِرِۭ
A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko
Compartir :
إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ يَشۡرَبُونَ مِن كَأۡسٖ كَانَ مِزَاجُهَا كَافُورًا
Lalle mutane nagari suna sha daga wani kofin (giya) da mahaxinta ya kasance kafur ne[1]
1- Watau mai daxin qamshi.
عَيۡنٗا يَشۡرَبُ بِهَا عِبَادُ ٱللَّهِ يُفَجِّرُونَهَا تَفۡجِيرٗا
Wani marmaro ne da bayin Allah suke sha daga gare shi suna vuvvugo shi vuvvugowa ta haqiqa
يُوفُونَ بِٱلنَّذۡرِ وَيَخَافُونَ يَوۡمٗا كَانَ شَرُّهُۥ مُسۡتَطِيرٗا
Suna cika alqawari na bakance suna kuma tsoron ranar da sharrinta ya kasance mai bazuwa ne
وَيُطۡعِمُونَ ٱلطَّعَامَ عَلَىٰ حُبِّهِۦ مِسۡكِينٗا وَيَتِيمٗا وَأَسِيرًا
Suna kuma ciyar da abinci tare da suna son sa ga miskini da maraya da kuma ribataccen yaqi
إِنَّمَا نُطۡعِمُكُمۡ لِوَجۡهِ ٱللَّهِ لَا نُرِيدُ مِنكُمۡ جَزَآءٗ وَلَا شُكُورًا
(Suna cewa): “Mu kawai muna ciyar da ku ne saboda Allah, ba ma nufin sakamako ko godiya daga wurinka
إِنَّا نَخَافُ مِن رَّبِّنَا يَوۡمًا عَبُوسٗا قَمۡطَرِيرٗا
“Lalle mu muna jin tsoron rana mai sa xaure fuska, matsananciya daga Ubangijinmu
فَوَقَىٰهُمُ ٱللَّهُ شَرَّ ذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمِ وَلَقَّىٰهُمۡ نَضۡرَةٗ وَسُرُورٗا
Sai Allah Ya kare su (daga) sharrin wannan ranar Ya kuma ba su haske (a fuskokinsu) da kuma farin ciki
وَجَزَىٰهُم بِمَا صَبَرُواْ جَنَّةٗ وَحَرِيرٗا
Ya kuma saka musu da Aljanna da alharini saboda haqurin da suka yi
إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٖ
Lalle mutanen kirki tabbas suna cikin ni’ima
يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ
(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa
ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ
Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda
فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي
Don haka ka shiga cikin bayina
وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي
Ka kuma shiga Aljannata