Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 30

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ إِنَّا لَا نُضِيعُ أَجۡرَ مَنۡ أَحۡسَنَ عَمَلًا

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki nagari tabbas Mu ba ma tozarta ladan wanda ya kyautata aiki



Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 110

قُلۡ إِنَّمَآ أَنَا۠ بَشَرٞ مِّثۡلُكُمۡ يُوحَىٰٓ إِلَيَّ أَنَّمَآ إِلَٰهُكُمۡ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞۖ فَمَن كَانَ يَرۡجُواْ لِقَآءَ رَبِّهِۦ فَلۡيَعۡمَلۡ عَمَلٗا صَٰلِحٗا وَلَا يُشۡرِكۡ بِعِبَادَةِ رَبِّهِۦٓ أَحَدَۢا

Ka ce: “Ni dai mutum ne kawai kamarku da ake yi mini wahayi cewa abin bautarku abin bauta ne Xaya; don haka wanda ya kasance yana tsoron gamuwa da Ubangijinsa, to sai ya yi aiki nagari, kada kuma ya tara wani cikin bautar Ubangijinsa.”



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 83

تِلۡكَ ٱلدَّارُ ٱلۡأٓخِرَةُ نَجۡعَلُهَا لِلَّذِينَ لَا يُرِيدُونَ عُلُوّٗا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا فَسَادٗاۚ وَٱلۡعَٰقِبَةُ لِلۡمُتَّقِينَ

Wancan gida na lahira Muna ba da shi ga waxanda ba sa nufin girman kai da varna a bayan qasa. Kyakkyawan qarshe kuma yana ga masu kiyaye dokokin Allah ne



Capítulo: Suratur Rum

Verso : 44

مَن كَفَرَ فَعَلَيۡهِ كُفۡرُهُۥۖ وَمَنۡ عَمِلَ صَٰلِحٗا فَلِأَنفُسِهِمۡ يَمۡهَدُونَ

Wanda ya kafirta to zunubin kafircinsa yana kansa; waxanda kuwa suka yi aiki kyakkyawa, to kansu suke yi wa shimfixa (ta alheri)



Capítulo: Suratu Luqman

Verso : 13

وَإِذۡ قَالَ لُقۡمَٰنُ لِٱبۡنِهِۦ وَهُوَ يَعِظُهُۥ يَٰبُنَيَّ لَا تُشۡرِكۡ بِٱللَّهِۖ إِنَّ ٱلشِّرۡكَ لَظُلۡمٌ عَظِيمٞ

Kuma (ka tuna) lokacin da Luqumanu ya ce da xansa a yayin da yake yi masa wa’azi: “Ya kai xanxana, kada ka yi shirka da Allah; lalle ita shirka zalunci ne mai girma



Capítulo: Suratu Luqman

Verso : 14

وَوَصَّيۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ بِوَٰلِدَيۡهِ حَمَلَتۡهُ أُمُّهُۥ وَهۡنًا عَلَىٰ وَهۡنٖ وَفِصَٰلُهُۥ فِي عَامَيۡنِ أَنِ ٱشۡكُرۡ لِي وَلِوَٰلِدَيۡكَ إِلَيَّ ٱلۡمَصِيرُ

Kuma Mun yi wa mutum wasiyya game da iyayensa, mahaifiyarsa ta xauke shi a cikinta rauni a kan rauni, yaye shi kuwa a cikin shekara biyu ne, saboda haka ka gode min da kuma iyayenka, makoma gare Ni take



Capítulo: Suratu Luqman

Verso : 15

وَإِن جَٰهَدَاكَ عَلَىٰٓ أَن تُشۡرِكَ بِي مَا لَيۡسَ لَكَ بِهِۦ عِلۡمٞ فَلَا تُطِعۡهُمَاۖ وَصَاحِبۡهُمَا فِي ٱلدُّنۡيَا مَعۡرُوفٗاۖ وَٱتَّبِعۡ سَبِيلَ مَنۡ أَنَابَ إِلَيَّۚ ثُمَّ إِلَيَّ مَرۡجِعُكُمۡ فَأُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Idan kuma suka matsa maka kan ka yi tarayya da Ni game da abin da ba ka da wani sani a kansa, to kada ka bi su; kuma ka yi zaman duniya da su ta kyakkyawar hanya; ka kuma bi hanyar wanda ya mayar da al’amarinsa gare Ni. Sannan kuma zuwa gare Ni ne kawai makomarku, sai in ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa



Capítulo: Suratu Luqman

Verso : 16

يَٰبُنَيَّ إِنَّهَآ إِن تَكُ مِثۡقَالَ حَبَّةٖ مِّنۡ خَرۡدَلٖ فَتَكُن فِي صَخۡرَةٍ أَوۡ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ أَوۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ يَأۡتِ بِهَا ٱللَّهُۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَطِيفٌ خَبِيرٞ

(Luqumanu ya ci gaba da cewa): “Ya kai xanxana, lalle ita (kyakkyawa ko mummuna) in ta kasance daidai da qwayar komayya, sannan kuma ta zamanto cikin qaton dutse ko kuma cikin sammai ko cikin qasa, to Allah zai zo da ita. Lalle Allah Mai tausasawa ne, Masanin (komai)



Capítulo: Suratu Luqman

Verso : 17

يَٰبُنَيَّ أَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَ وَأۡمُرۡ بِٱلۡمَعۡرُوفِ وَٱنۡهَ عَنِ ٱلۡمُنكَرِ وَٱصۡبِرۡ عَلَىٰ مَآ أَصَابَكَۖ إِنَّ ذَٰلِكَ مِنۡ عَزۡمِ ٱلۡأُمُورِ

“Ya kai xanxana, ka tsayar da salla kuma ka yi umarni da aikata alheri, ka kuma hana aikata mummunan aiki, kuma ka yi haquri bisa duk abin da ya same ka; lalle wannan yana daga manyan al’amura



Capítulo: Suratu Luqman

Verso : 18

وَلَا تُصَعِّرۡ خَدَّكَ لِلنَّاسِ وَلَا تَمۡشِ فِي ٱلۡأَرۡضِ مَرَحًاۖ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُحِبُّ كُلَّ مُخۡتَالٖ فَخُورٖ

“Kada kuma ka riqa xauke wa mutane fuskarka[1], kuma kada ka yi tafiya a ban qasa kana mai taqama. Lalle Allah ba Ya son duk wani mai taqama, mai fariya


1- Watau yana umartar sa da ya zama mai sakin fuska da haba-haba da jama’a.


Capítulo: Suratu Luqman

Verso : 19

وَٱقۡصِدۡ فِي مَشۡيِكَ وَٱغۡضُضۡ مِن صَوۡتِكَۚ إِنَّ أَنكَرَ ٱلۡأَصۡوَٰتِ لَصَوۡتُ ٱلۡحَمِيرِ

“Kuma ka tsakaita tafiyarka, kuma ka yi qasa-qasa da muryarka. Lalle mafi munin muryoyi ita ce muryar jakai.”



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 37

وَمَآ أَمۡوَٰلُكُمۡ وَلَآ أَوۡلَٰدُكُم بِٱلَّتِي تُقَرِّبُكُمۡ عِندَنَا زُلۡفَىٰٓ إِلَّا مَنۡ ءَامَنَ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا فَأُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ جَزَآءُ ٱلضِّعۡفِ بِمَا عَمِلُواْ وَهُمۡ فِي ٱلۡغُرُفَٰتِ ءَامِنُونَ

Kuma ba dukiyoyinku da ‘ya’yanku ne za su kusantar da ku gare Mu ba, sai wanda ya yi imani ya kuma yi aiki nagari, to waxannan suna da sakamako ninkin-baninki saboda abin da suka aikata, suna kuma amintattu cikin benaye



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 33

وَٱلَّذِي جَآءَ بِٱلصِّدۡقِ وَصَدَّقَ بِهِۦٓ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُتَّقُونَ

Wanda kuwa ya zo da gaskiya ya kuma gaskata ta, waxannan su ne masu taqawa



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 40

مَنۡ عَمِلَ سَيِّئَةٗ فَلَا يُجۡزَىٰٓ إِلَّا مِثۡلَهَاۖ وَمَنۡ عَمِلَ صَٰلِحٗا مِّن ذَكَرٍ أَوۡ أُنثَىٰ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَأُوْلَـٰٓئِكَ يَدۡخُلُونَ ٱلۡجَنَّةَ يُرۡزَقُونَ فِيهَا بِغَيۡرِ حِسَابٖ

“Wanda ya aikata wani mummunan aiki, to ba za a saka masa ba sai da kwatankwacinsa, wanda kuwa ya aikata wani kyakkyawan aiki, namiji ne ko mace alhali shi yana mumini, to waxannan za su shiga Aljanna, a riqa arzuta su a cikinta ba tare da lissafi ba



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 33

وَمَنۡ أَحۡسَنُ قَوۡلٗا مِّمَّن دَعَآ إِلَى ٱللَّهِ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا وَقَالَ إِنَّنِي مِنَ ٱلۡمُسۡلِمِينَ

Wane ne ya fi kyakkyawar magana fiye da wanda ya yi kira zuwa ga Allah ya kuma yi aiki nagari, kuma ya ce: “Lalle ni ina daga cikin Musulmi?”



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 46

مَّنۡ عَمِلَ صَٰلِحٗا فَلِنَفۡسِهِۦۖ وَمَنۡ أَسَآءَ فَعَلَيۡهَاۗ وَمَا رَبُّكَ بِظَلَّـٰمٖ لِّلۡعَبِيدِ

Wanda ya yi aiki nagari, to kansa ya yi wa, wanda kuma ya munana, to a kan kansa ya yi wa. Ubangijnka ba Mai zaluntar bayi ba ne



Capítulo: Suratul Ahqaf 

Verso : 15

وَوَصَّيۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ بِوَٰلِدَيۡهِ إِحۡسَٰنًاۖ حَمَلَتۡهُ أُمُّهُۥ كُرۡهٗا وَوَضَعَتۡهُ كُرۡهٗاۖ وَحَمۡلُهُۥ وَفِصَٰلُهُۥ ثَلَٰثُونَ شَهۡرًاۚ حَتَّىٰٓ إِذَا بَلَغَ أَشُدَّهُۥ وَبَلَغَ أَرۡبَعِينَ سَنَةٗ قَالَ رَبِّ أَوۡزِعۡنِيٓ أَنۡ أَشۡكُرَ نِعۡمَتَكَ ٱلَّتِيٓ أَنۡعَمۡتَ عَلَيَّ وَعَلَىٰ وَٰلِدَيَّ وَأَنۡ أَعۡمَلَ صَٰلِحٗا تَرۡضَىٰهُ وَأَصۡلِحۡ لِي فِي ذُرِّيَّتِيٓۖ إِنِّي تُبۡتُ إِلَيۡكَ وَإِنِّي مِنَ ٱلۡمُسۡلِمِينَ

Kuma Mun yi wa mutum wasiyya da kyautata wa mahaifansa; mahaifiyarsa ta xauki cikinsa a wahalce, ta kuma haife shi a wahalce; xaukan cikinsa da yaye shi kuma wata talatin ne, har lokacin da ya cika qarfinsa ya kai shekara arba’in ya ce: “Ya Ubangijina, Ka kimsa min yadda zan gode wa ni’imarka, wadda Ka ni’imta ni da ita da kuma mahaifana, kuma (Ka ba ni iko) in yi aiki nagari wanda za Ka yarda da shi, kuma Ka kyautata min zurriyata; lalle ni na tuba a gare Ka, kuma lalle ni ina daga cikin Musulmi.”



Capítulo: Suratul Ahqaf 

Verso : 16

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ نَتَقَبَّلُ عَنۡهُمۡ أَحۡسَنَ مَا عَمِلُواْ وَنَتَجَاوَزُ عَن سَيِّـَٔاتِهِمۡ فِيٓ أَصۡحَٰبِ ٱلۡجَنَّةِۖ وَعۡدَ ٱلصِّدۡقِ ٱلَّذِي كَانُواْ يُوعَدُونَ

Waxannan su ne waxanda Muke karvar mafi kyan abin da suka aikata, kuma Muke yafe musu munanan ayyukansu, suna cikin ‘yan Aljanna; (wannan) alqawari ne na gaskiya wanda suka kasance ana yi musu alqawarinsa (a duniya)



Capítulo: Suratu Muhammad

Verso : 17

وَٱلَّذِينَ ٱهۡتَدَوۡاْ زَادَهُمۡ هُدٗى وَءَاتَىٰهُمۡ تَقۡوَىٰهُمۡ

Waxanda kuwa suka shiryu Ya qara musu shiriya, Ya kuma kimsa musu taqawarsu



Capítulo: Suratul Hujurat

Verso : 13

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ إِنَّا خَلَقۡنَٰكُم مِّن ذَكَرٖ وَأُنثَىٰ وَجَعَلۡنَٰكُمۡ شُعُوبٗا وَقَبَآئِلَ لِتَعَارَفُوٓاْۚ إِنَّ أَكۡرَمَكُمۡ عِندَ ٱللَّهِ أَتۡقَىٰكُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمٌ خَبِيرٞ

Ya ku mutane, lalle Mu Muka halicce ku daga namiji da mace, Muka kuma sanya ku al’ummu da qabilu don ku san juna. Lalle mafi girmanku a wurin Allah shi ne wanda ya fi ku taqawa. Lalle Allah Masanin sarari ne, Masanin voye



Capítulo: Suratul Hashr

Verso : 7

مَّآ أَفَآءَ ٱللَّهُ عَلَىٰ رَسُولِهِۦ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡقُرَىٰ فَلِلَّهِ وَلِلرَّسُولِ وَلِذِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينِ وَٱبۡنِ ٱلسَّبِيلِ كَيۡ لَا يَكُونَ دُولَةَۢ بَيۡنَ ٱلۡأَغۡنِيَآءِ مِنكُمۡۚ وَمَآ ءَاتَىٰكُمُ ٱلرَّسُولُ فَخُذُوهُ وَمَا نَهَىٰكُمۡ عَنۡهُ فَٱنتَهُواْۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Abin da Allah ya bai wa Manzonsa na wata dukiya daga mutanen alqaryu, to na Allah ne da Manzonsa da kuma danginsa na kusa[1] da marayu da miskinai da matafiyin (da guzuri ya yanke wa), don kada ya zama mai juyawa tsakanin mawadata daga cikinku. Kuma abin da Manzo ya ba ku sai ku karve shi, abin kuma da ya hana ku sai ku hanu. Ku kuma kiyaye dokokin Allah; lalle Allah Mai tsananin uquba ne


1- Watau Banu Hashim da Banul Muxxalib, waxanda aka haramta musu karvar sadaka ko zakka.


Capítulo: Suratut Taghabun

Verso : 16

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ مَا ٱسۡتَطَعۡتُمۡ وَٱسۡمَعُواْ وَأَطِيعُواْ وَأَنفِقُواْ خَيۡرٗا لِّأَنفُسِكُمۡۗ وَمَن يُوقَ شُحَّ نَفۡسِهِۦ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

Saboda haka ku kiyaye dokokin Allah gwargwadon ikonku, kuma ku yi sauraro, ku bi, ku kuma ciyar, shi ya fi alheri a gare ku. Duk kuwa wanda aka kare shi daga tsananin son kansa, to waxannan su ne masu babban rabo