Capítulo: Suratul Insan

Verso : 22

إِنَّ هَٰذَا كَانَ لَكُمۡ جَزَآءٗ وَكَانَ سَعۡيُكُم مَّشۡكُورًا

Lalle wannan ya kasance sakamako ne a gare ku, kuma aikinku ya kasance abin godewa



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 25

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونِۭ

Sai dai waxanda suka yi imani, suka kuma yi ayyuka nagari, to suna da lada marar yankewa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 28

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ

Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 29

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي

Don haka ka shiga cikin bayina



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 30

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي

Ka kuma shiga Aljannata



Capítulo: Suratut Tin

Verso : 6

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ

Sai fa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, to su kam suna da lada ba mai yankewa ba



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 7

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ خَيۡرُ ٱلۡبَرِيَّةِ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, waxannan su ne mafiya alherin halitta



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 8

جَزَآؤُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتُ عَدۡنٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ رَّضِيَ ٱللَّهُ عَنۡهُمۡ وَرَضُواْ عَنۡهُۚ ذَٰلِكَ لِمَنۡ خَشِيَ رَبَّهُۥ

Sakamakonsu a wajen Ubangijinsu gidajen Aljanna ne na dawwama waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu suna madawwama a cikinsu har abada; Allah Ya yarda da su, su ma sun yarda da Shi. Wannan kuma (sakamako ne) ga wanda ya ji tsoron Ubangijinsa