Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 42

قَالَ نَعَمۡ وَإِنَّكُمۡ إِذٗا لَّمِنَ ٱلۡمُقَرَّبِينَ

(Fir’auna) ya ce: “Na’am, kuma ma idan haka ya faru, to tabbas za ku zama daga makusanta.”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 43

قَالَ لَهُم مُّوسَىٰٓ أَلۡقُواْ مَآ أَنتُم مُّلۡقُونَ

(Sai Musa) ya ce da su: “Ku jefa duk abin da za ku jefa.”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 44

فَأَلۡقَوۡاْ حِبَالَهُمۡ وَعِصِيَّهُمۡ وَقَالُواْ بِعِزَّةِ فِرۡعَوۡنَ إِنَّا لَنَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبُونَ

Sai suka jefa igiyoyinsu da sandunansu suka kuma ce: “Lalle da izzar Fir’auna tabbas mu ne masu galaba.”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 45

فَأَلۡقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ تَلۡقَفُ مَا يَأۡفِكُونَ

Sai Musa ya jefa sandarsa, sai ga ta tana lanqwame duk abin da suke qagowa (na sihiri)



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 46

فَأُلۡقِيَ ٱلسَّحَرَةُ سَٰجِدِينَ

Sai aka durqusar da masu sihirin suna masu sujjada



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 47

قَالُوٓاْ ءَامَنَّا بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Suka ce: “Mun yi imani da Ubangijin talikai



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 48

رَبِّ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

“Ubangijin Musa da Haruna.”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 49

قَالَ ءَامَنتُمۡ لَهُۥ قَبۡلَ أَنۡ ءَاذَنَ لَكُمۡۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِي عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحۡرَ فَلَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيۡدِيَكُمۡ وَأَرۡجُلَكُم مِّنۡ خِلَٰفٖ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمۡ أَجۡمَعِينَ

(Sai Fir’auna) ya ce: “Yanzu kwa yi imani da shi tun kafin in ba ku izini? Lalle tabbas shi ne babbanku wanda ya koya muku sihiri; to tabbas kuwa kwa sani. Lalle zan yanyanke hannayenku da qafafuwanku a tarnaqe, kuma tabbas zan gicciye ku gaba xaya!”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 50

قَالُواْ لَا ضَيۡرَۖ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ

Sai suka ce: “Ai ba damuwa; lalle mu masu komawa ne zuwa ga Ubangijinmu



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 51

إِنَّا نَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَٰيَٰنَآ أَن كُنَّآ أَوَّلَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

“Lalle mu muna kwaxayin Ubangijinmu Ya gafarta mana kurakuranmu saboda zamantowarmu farkon muminai.”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 52

۞وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَسۡرِ بِعِبَادِيٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

Muka kuma yi wa Musa wahayi cewa: “Ka tafi cikin dare tare da bayina, lalle ku za a biyo bayanku.”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 53

فَأَرۡسَلَ فِرۡعَوۡنُ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ

Sai Fir’auna ya aika zuwa birane don a tattaro (mayaqa)



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 54

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَشِرۡذِمَةٞ قَلِيلُونَ

(Fir’auna yana cewa): “Lalle waxannan tabbas ‘yan tsirarin jama’a ne



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 55

وَإِنَّهُمۡ لَنَا لَغَآئِظُونَ

“Kuma haqiqa su lalle suna fusata mu



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 56

وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَٰذِرُونَ

“Lalle kuma mu tabbas gaba xayanmu masu kwana cikin shiri ne.”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 57

فَأَخۡرَجۡنَٰهُم مِّن جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

(Allah Ya ce): Sai Muka fitar da su daga gonaki da kuma idandunan ruwa



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 58

وَكُنُوزٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ

Da taskoki da kuma mazauni na alfarma



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 59

كَذَٰلِكَۖ وَأَوۡرَثۡنَٰهَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Kamar haka ne Muka gadar da su ga Banu-Isra’ila



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 60

فَأَتۡبَعُوهُم مُّشۡرِقِينَ

Sai suka bi bayansu a lokacin fitowar rana



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 61

فَلَمَّا تَرَـٰٓءَا ٱلۡجَمۡعَانِ قَالَ أَصۡحَٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدۡرَكُونَ

To lokacin da jama’ar biyu suka ga juna, sai sahabban Musa suka ce: “Lalle tabbas mu za a cim mana.”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 62

قَالَ كَلَّآۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهۡدِينِ

(Musa) ya ce: “A’a; Ubangijina Yana tare da ni, zai kuwa shiryar da ni (hanyar tsira).”



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 63

فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡبَحۡرَۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرۡقٖ كَٱلطَّوۡدِ ٱلۡعَظِيمِ

Sai Muka yi wahayi ga Musa cewa: “Ka bugi kogin da sandarka;” (da ya buge shi) sai ya dare, kowanne yanki sai ya zama kamar qaton dutse



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 64

وَأَزۡلَفۡنَا ثَمَّ ٱلۡأٓخَرِينَ

Muka kuma kusantar da waxancan (watau mutanen Fir’auna) zuwa can (kusa da kogin)



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 65

وَأَنجَيۡنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

Muka kuma tserar da Musa da waxanda suke tare da shi gaba xaya



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 66

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka nutsar da sauran mutanen (watau Fir’auna da mutanensa)



Capítulo: Suratus Shu’ara

Verso : 67

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 7

إِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِأَهۡلِهِۦٓ إِنِّيٓ ءَانَسۡتُ نَارٗا سَـَٔاتِيكُم مِّنۡهَا بِخَبَرٍ أَوۡ ءَاتِيكُم بِشِهَابٖ قَبَسٖ لَّعَلَّكُمۡ تَصۡطَلُونَ

Ka tuna lokacin da Musa ya ce da iyalinsa: “Lalle ni na hango wata wuta, to (zan je) in zo muku da labari, ko kuma in zo muku da xosanen garwashi don ku ji xumi.”



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 8

فَلَمَّا جَآءَهَا نُودِيَ أَنۢ بُورِكَ مَن فِي ٱلنَّارِ وَمَنۡ حَوۡلَهَا وَسُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

To lokacin da ya zo mata (wutar) sai aka kira shi cewa, an tsarkake wanda yake cikin wutar da waxanda suke daura da ita (wato mala’iku), kuma tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 9

يَٰمُوسَىٰٓ إِنَّهُۥٓ أَنَا ٱللَّهُ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Ya Musa, lalle lamarin dai, Ni ne Allah Mabuwayi, Mai hikima



Capítulo: Suratun Namli

Verso : 10

وَأَلۡقِ عَصَاكَۚ فَلَمَّا رَءَاهَا تَهۡتَزُّ كَأَنَّهَا جَآنّٞ وَلَّىٰ مُدۡبِرٗا وَلَمۡ يُعَقِّبۡۚ يَٰمُوسَىٰ لَا تَخَفۡ إِنِّي لَا يَخَافُ لَدَيَّ ٱلۡمُرۡسَلُونَ

Kuma ka jefar da sandarka. To lokacin da ya gan ta tana jujjuyawa kamar macijiya, sai ya juya da baya a guje bai dawo ba. (Allah ya ce): Ya Musa, kada ka ji tsoro, lalle Ni manzanni ba sa jin tsoro a wurina