أَنَّا صَبَبۡنَا ٱلۡمَآءَ صَبّٗا
Cewa lalle Mu Muka zubo da ruwan sama zubowa
Compartir :
ثُمَّ شَقَقۡنَا ٱلۡأَرۡضَ شَقّٗا
Sannan Muka tsaga qasa tsagawa
فَأَنۢبَتۡنَا فِيهَا حَبّٗا
Sai Muka tsiro da qwaya daga cikinta
وَعِنَبٗا وَقَضۡبٗا
Da inabai da ciyayi
وَزَيۡتُونٗا وَنَخۡلٗا
Da zaitun da dabino
وَحَدَآئِقَ غُلۡبٗا
Da gonaki cike da itatuwa
وَفَٰكِهَةٗ وَأَبّٗا
Da kayan marmari da makiyaya
مَّتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ
Don jin daxinku da na dabbobinku
فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ مِمَّ خُلِقَ
To mutum ya duba mana, daga me aka halicce shi?
خُلِقَ مِن مَّآءٖ دَافِقٖ
An halicce shi ne daga wani ruwa mai ingizar juna[1]
1- Watau maniyyi.
يَخۡرُجُ مِنۢ بَيۡنِ ٱلصُّلۡبِ وَٱلتَّرَآئِبِ
Mai fita daga tsakanin tsatso da karankarma[1]
1- Watau daga tsakanin qashin bayan namiji da qasusuwan qirjinsa.
إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٞ
Lalle Shi (Allah) Mai iko ne a kan dawo da shi
أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ
Shin ba sa duban raqumi yadda aka halicce shi?
وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيۡفَ رُفِعَتۡ
Da kuma sama yadda aka xaga ta?
وَإِلَى ٱلۡجِبَالِ كَيۡفَ نُصِبَتۡ
Da kuma duwatsu yadda aka kakkafa su?
وَإِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَيۡفَ سُطِحَتۡ
Da kuma qasa yadda aka shimfixa ta?
ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta