Sure: Suratus Sharh

Vers : 1

أَلَمۡ نَشۡرَحۡ لَكَ صَدۡرَكَ

Shin ba Mu yalwata maka qirjinka ba[1]?


1- Watau ya hore masa son sauraren wahayin da yake yiwo masa da kuma juriya a kan gallazawar mutanensa.


Sure: Suratus Sharh

Vers : 2

وَوَضَعۡنَا عَنكَ وِزۡرَكَ

Muka kuma sauke maka nauye-nauyenka[1]?


1- Watau Allah () ya gafarta masa duk wasu laifuka na baya da na nan gaba idan za su samu.


Sure: Suratus Sharh

Vers : 3

ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ

Wanda ya nauyayi bayanka?



Sure: Suratus Sharh

Vers : 4

وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ

Muka kuma xaukaka maka ambatonka[1]?


1- Watau kamar ambatonsa a cikin kiran salla da iqama da tahiya da sauransu.


Sure: Suratus Sharh

Vers : 5

فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا

To lalle tsanani yana tare da sauqi



Sure: Suratus Sharh

Vers : 6

إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا

Lalle tsananin yana tare da sauqi



Sure: Suratus Sharh

Vers : 7

فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ

Saboda haka idan ka gama (harkokinka) sai ka kafu (wajen bautar Allah)



Sure: Suratus Sharh

Vers : 8

وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب

Sannan kuma ka yi kwaxayi wajen Ubangijinka kawai