Sure: Suratul Balad

Vers : 1

لَآ أُقۡسِمُ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ

Na rantse da wannan gari (na Makka)



Sure: Suratul Balad

Vers : 2

وَأَنتَ حِلُّۢ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ

Alhali kuwa kai an halatta maka wannan gari[1]


1- Watau an halatta masa kashe wanda ya cancanci kisa a garin Makka. Ko kuma ana nufin Allah ya yi rantsuwa da Makka musamman lokacin da Annabi () yake zaune a cikinta.


Sure: Suratul Balad

Vers : 3

وَوَالِدٖ وَمَا وَلَدَ

(Na rantse) da mahaifi da abin da ya haifa[1]


1- Watau Annabi Adamu () da zurriyarsa. Ko kuma duk wani mahaifi da duk wani wanda aka haifa.


Sure: Suratul Balad

Vers : 4

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِي كَبَدٍ

Haqiqa Mun halicci mutum cikin wahala



Sure: Suratul Balad

Vers : 5

أَيَحۡسَبُ أَن لَّن يَقۡدِرَ عَلَيۡهِ أَحَدٞ

Yanzu mutum yana tsammanin cewa wani ba zai sami iko a kansa ba?



Sure: Suratul Balad

Vers : 6

يَقُولُ أَهۡلَكۡتُ مَالٗا لُّبَدًا

Yana cewa: “Na vatar da dukiya mai ximbin yawa.”



Sure: Suratul Balad

Vers : 7

أَيَحۡسَبُ أَن لَّمۡ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ

Shin yana tsammanin cewa ba wanda ya gan shi?



Sure: Suratul Balad

Vers : 8

أَلَمۡ نَجۡعَل لَّهُۥ عَيۡنَيۡنِ

Shin ba Mu sanya masa idanuwa biyu ba ne?



Sure: Suratul Balad

Vers : 9

وَلِسَانٗا وَشَفَتَيۡنِ

Da harshe da kuma lavva biyu?



Sure: Suratul Balad

Vers : 10

وَهَدَيۡنَٰهُ ٱلنَّجۡدَيۡنِ

Muka kuma bayyana masa hanyoyi biyu[1]?


1- Watau hanyar alheri da hanyar sharri.


Sure: Suratul Balad

Vers : 11

فَلَا ٱقۡتَحَمَ ٱلۡعَقَبَةَ

Sai bai qetare hanya mai wahala[1] ba?


1- Watau hanyar da ta raba tsakaninsa da gidan Aljanna.


Sure: Suratul Balad

Vers : 12

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡعَقَبَةُ

Me kuma ya sanar da kai mece ce hanya mai wahala?



Sure: Suratul Balad

Vers : 13

فَكُّ رَقَبَةٍ

(Watau) ‘yanta wuyaye (bawa ko baiwa)



Sure: Suratul Balad

Vers : 14

أَوۡ إِطۡعَٰمٞ فِي يَوۡمٖ ذِي مَسۡغَبَةٖ

Ko kuma ciyarwa a wata rana ta yunwa



Sure: Suratul Balad

Vers : 15

يَتِيمٗا ذَا مَقۡرَبَةٍ

Ga maraya ma’abocin kusanci



Sure: Suratul Balad

Vers : 16

أَوۡ مِسۡكِينٗا ذَا مَتۡرَبَةٖ

Ko miskini ma’abocin talauci



Sure: Suratul Balad

Vers : 17

ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡمَرۡحَمَةِ

Sannan kuma ya zama daga waxanda suka yi imani, suka yi wa junansu wasiyya da yin haquri kuma suka yi wa juna wasiyya da tausayawa



Sure: Suratul Balad

Vers : 18

أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ

Waxannan su ne ma’abota dama[1]


1- Watau ‘yan Aljanna.


Sure: Suratul Balad

Vers : 19

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِنَا هُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ

Waxanda kuwa suka kafirce wa ayoyinmu, su ne ma’abota hagu[1]


1- Watau ‘yan wuta.


Sure: Suratul Balad

Vers : 20

عَلَيۡهِمۡ نَارٞ مُّؤۡصَدَةُۢ

A kansu akwai wuta abar kullewa