Sure: Suratul A’ala

Vers : 1

سَبِّحِ ٱسۡمَ رَبِّكَ ٱلۡأَعۡلَى

Ka tsarkake sunan Ubangijinka Mafi xaukaka



Sure: Suratul A’ala

Vers : 2

ٱلَّذِي خَلَقَ فَسَوَّىٰ

Wanda Ya yi halitta sai Ya daidaita (ta)



Sure: Suratul A’ala

Vers : 3

وَٱلَّذِي قَدَّرَ فَهَدَىٰ

Wanda kuma Ya qaddara (abubuwa) sannan Ya shiryar (da halittarsa)



Sure: Suratul A’ala

Vers : 4

وَٱلَّذِيٓ أَخۡرَجَ ٱلۡمَرۡعَىٰ

Wanda kuma Ya fitar da makiyaya



Sure: Suratul A’ala

Vers : 5

فَجَعَلَهُۥ غُثَآءً أَحۡوَىٰ

Sai Ya mayar da ita duddugaggiya mai baqi



Sure: Suratul A’ala

Vers : 6

سَنُقۡرِئُكَ فَلَا تَنسَىٰٓ

Za Mu karantar da kai (Alqur’ani) don haka ba za ka manta ba



Sure: Suratul A’ala

Vers : 7

إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلۡجَهۡرَ وَمَا يَخۡفَىٰ

Sai abin da Allah Ya ga dama, Lalle Shi Yana sane da bayyanannen (abu) da kuma abin da yake vuya



Sure: Suratul A’ala

Vers : 8

وَنُيَسِّرُكَ لِلۡيُسۡرَىٰ

Kuma za Mu sauqaqe maka (al’umara) mafiya sauqi[1]


1- Watau al’ummuransa na addini da na rayuwa, domin ya sa damar da saqon Allah a cikin nutsuwa.


Sure: Suratul A’ala

Vers : 9

فَذَكِّرۡ إِن نَّفَعَتِ ٱلذِّكۡرَىٰ

To ka yi wa’azi idan wa’azin zai yi amfani



Sure: Suratul A’ala

Vers : 10

سَيَذَّكَّرُ مَن يَخۡشَىٰ

Wanda yake tsoron Allah zai wa’azantu



Sure: Suratul A’ala

Vers : 11

وَيَتَجَنَّبُهَا ٱلۡأَشۡقَى

Mafi shaqiyanci[1] kuma zai nesance shi


1- Watau kafiri tavavve.


Sure: Suratul A’ala

Vers : 12

ٱلَّذِي يَصۡلَى ٱلنَّارَ ٱلۡكُبۡرَىٰ

Wanda zai shiga wuta mafi girma



Sure: Suratul A’ala

Vers : 13

ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحۡيَىٰ

Sannan ba zai mutu a cikinta ba kuma ba zai rayu (rayuwa mai daxi) ba



Sure: Suratul A’ala

Vers : 14

قَدۡ أَفۡلَحَ مَن تَزَكَّىٰ

Haqiqa wanda ya tsarkaka ya rabauta



Sure: Suratul A’ala

Vers : 15

وَذَكَرَ ٱسۡمَ رَبِّهِۦ فَصَلَّىٰ

Ya kuma ambaci sunan Ubangijinsa sannan ya yi salla



Sure: Suratul A’ala

Vers : 16

بَلۡ تُؤۡثِرُونَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا

Ba haka ba, ku dai kuna fifita rayuwar duniya ne



Sure: Suratul A’ala

Vers : 17

وَٱلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ وَأَبۡقَىٰٓ

Lahira kuwa ita ta fi alheri ta kuma fi wanzuwa



Sure: Suratul A’ala

Vers : 18

إِنَّ هَٰذَا لَفِي ٱلصُّحُفِ ٱلۡأُولَىٰ

Lalle wannan (batu) tabbas yana cikin littattafan farko



Sure: Suratul A’ala

Vers : 19

صُحُفِ إِبۡرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ

Littattafan Ibrahimu da Musa