Sure: Suratul Buruj

Vers : 1

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡبُرُوجِ

Na rantse da sama ma’abociyar manziloli[1]


1- Watau manziloli na rana da wata da taurari.


Sure: Suratul Buruj

Vers : 2

وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡمَوۡعُودِ

Da ranar da aka yi alqawarin zuwanta[1]


1- Watau ranar alqiyama.


Sure: Suratul Buruj

Vers : 3

وَشَاهِدٖ وَمَشۡهُودٖ

Da mai shaida[1] da kuma abin yi wa shaida


1- Watau kamar Annabi da zai ba da shaida game da al’ummarsa.


Sure: Suratul Buruj

Vers : 4

قُتِلَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡأُخۡدُودِ

An la’anci ma’abota rami (na azabtar da muminai)[1]


1- Wani azzalumin sarki ne da aka yi a Najrana ta qasar Yaman kafin aiko Annabi () wanda aka haqa masa rami aka hura wuta, ya riqa jefa muminai a cikinsa yana qona su da ransu.


Sure: Suratul Buruj

Vers : 5

ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلۡوَقُودِ

Na wuta mai ruruwa



Sure: Suratul Buruj

Vers : 6

إِذۡ هُمۡ عَلَيۡهَا قُعُودٞ

Yayin da suke zaune a gefenta



Sure: Suratul Buruj

Vers : 7

وَهُمۡ عَلَىٰ مَا يَفۡعَلُونَ بِٱلۡمُؤۡمِنِينَ شُهُودٞ

Alhali su suna kallon abin da suke aikata wa muminai



Sure: Suratul Buruj

Vers : 8

وَمَا نَقَمُواْ مِنۡهُمۡ إِلَّآ أَن يُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

Babu kuwa abin da suke tuhumar su da shi sai don kawai sun yi imani da Allah Mabuwayi, Sha-yabo



Sure: Suratul Buruj

Vers : 9

ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Wanda Yake da mulkin sammai da qasa. Allah kuma Mai ganin komai ne



Sure: Suratul Buruj

Vers : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُواْ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ ثُمَّ لَمۡ يَتُوبُواْ فَلَهُمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمۡ عَذَابُ ٱلۡحَرِيقِ

Lalle waxanda suka azabtar da muminai maza da muminai mata sannan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, suna kuma da azabar quna



Sure: Suratul Buruj

Vers : 11

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡكَبِيرُ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Wannan kuwa shi ne babban rabo



Sure: Suratul Buruj

Vers : 12

إِنَّ بَطۡشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ

Lalle damqar Ubangijinka tabbas mai tsanani ce



Sure: Suratul Buruj

Vers : 13

إِنَّهُۥ هُوَ يُبۡدِئُ وَيُعِيدُ

Lalle Shi ne Yake farar (da komai) Yake kuma dawo (da shi)



Sure: Suratul Buruj

Vers : 14

وَهُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلۡوَدُودُ

Shi ne kuma Mai gafara, Mai qaunar (bayinsa na qwarai)



Sure: Suratul Buruj

Vers : 15

ذُو ٱلۡعَرۡشِ ٱلۡمَجِيدُ

Ma’abocin Al’arshi Mai girma



Sure: Suratul Buruj

Vers : 16

فَعَّالٞ لِّمَا يُرِيدُ

Mai aikata abin da Yake nufi



Sure: Suratul Buruj

Vers : 17

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلۡجُنُودِ

Shin labarin rundunoni ya zo maka?



Sure: Suratul Buruj

Vers : 18

فِرۡعَوۡنَ وَثَمُودَ

(Su ne) Fir’auna da Samudawa



Sure: Suratul Buruj

Vers : 19

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي تَكۡذِيبٖ

A’a, su dai waxanda suka kafirta suna cikin qaryatawa ne



Sure: Suratul Buruj

Vers : 20

وَٱللَّهُ مِن وَرَآئِهِم مُّحِيطُۢ

Allah kuwa Yana kewaye da su (da iliminsa)



Sure: Suratul Buruj

Vers : 21

بَلۡ هُوَ قُرۡءَانٞ مَّجِيدٞ

A’a, shi dai Alqur’ani ne mai girma



Sure: Suratul Buruj

Vers : 22

فِي لَوۡحٖ مَّحۡفُوظِۭ

A cikin Lauhul-Mahafuzu