Sure: Suratul Mursalat

Vers : 1

وَٱلۡمُرۡسَلَٰتِ عُرۡفٗا

Na rantse da iska mai bibiyar juna



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 2

فَٱلۡعَٰصِفَٰتِ عَصۡفٗا

Da kuma iska mai tasowa da tsanani



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 3

وَٱلنَّـٰشِرَٰتِ نَشۡرٗا

Da iska mai watso ruwa watsowa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 4

فَٱلۡفَٰرِقَٰتِ فَرۡقٗا

Da kuma (mala’iku) masu rarrabe qarya da gaskiya iya rarrabewa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 5

فَٱلۡمُلۡقِيَٰتِ ذِكۡرًا

Sannan masu sauko da wahayi



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 6

عُذۡرًا أَوۡ نُذۡرًا

Don yanke hanzari ko don gargaxi



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 7

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَوَٰقِعٞ

Lalle abin da ake yi muku alqawari tabbas mai afkuwa ne



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 8

فَإِذَا ٱلنُّجُومُ طُمِسَتۡ

To idan taurari aka shafe haskensu



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 9

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ فُرِجَتۡ

Idan kuma sama aka tsattsage ta



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 10

وَإِذَا ٱلۡجِبَالُ نُسِفَتۡ

Idan kuma duwatsu aka sheqe su



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 11

وَإِذَا ٱلرُّسُلُ أُقِّتَتۡ

Idan kuma manzanni aka tattara su[1]


1- Watau don su ba da shaida cewa sun isar wa al’ummunnsu saqon Allah.


Sure: Suratul Mursalat

Vers : 12

لِأَيِّ يَوۡمٍ أُجِّلَتۡ

Ga wacce rana ce aka qayyaje musu



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 13

لِيَوۡمِ ٱلۡفَصۡلِ

Ga rana ta yin hukunci[1]


1- Watau hukunci tsakanin bayi, a bayyana mai gaskiya da marar gaskiya da xan wuta da xan Aljanna.


Sure: Suratul Mursalat

Vers : 14

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلۡفَصۡلِ

Me kuma ya sanar da kai ranar yin hukunci



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 15

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 16

أَلَمۡ نُهۡلِكِ ٱلۡأَوَّلِينَ

Yanzu ba Mu hallakar da na farko ba?



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 17

ثُمَّ نُتۡبِعُهُمُ ٱلۡأٓخِرِينَ

Sannan Muka biyo su da na qarshe?



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 18

كَذَٰلِكَ نَفۡعَلُ بِٱلۡمُجۡرِمِينَ

Kamar haka Muke yi wa masu manyan laifuka



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 19

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 20

أَلَمۡ نَخۡلُقكُّم مِّن مَّآءٖ مَّهِينٖ

Yanzu ba Mu halicce ku daga wani wulaqantaccen ruwa ba?



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 21

فَجَعَلۡنَٰهُ فِي قَرَارٖ مَّكِينٍ

Sannan Muka sanya shi cikin matabbata mai aminci?



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 22

إِلَىٰ قَدَرٖ مَّعۡلُومٖ

Zuwa wani lokaci sananne?



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 23

فَقَدَرۡنَا فَنِعۡمَ ٱلۡقَٰدِرُونَ

Sannan Muka qaddara (komai ta yadda ya dace)? To madalla da Masu qaddarawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 24

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 25

أَلَمۡ نَجۡعَلِ ٱلۡأَرۡضَ كِفَاتًا

Yanzu ba Mu sanya qasa (ta zama) matattara ba?



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 26

أَحۡيَآءٗ وَأَمۡوَٰتٗا

(Ga) rayayyu da matattu[1]?


1- Watau masu rai a cikin gidajensu a bayanta, matatu kuma a binne a cikin qaburburansu a qarqashinta.


Sure: Suratul Mursalat

Vers : 27

وَجَعَلۡنَا فِيهَا رَوَٰسِيَ شَٰمِخَٰتٖ وَأَسۡقَيۡنَٰكُم مَّآءٗ فُرَاتٗا

Muka kuma sanya kafaffun duwatsu dogaye a cikinta, Muka kuma shayar da ku ruwa mai daxi?



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 28

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 29

ٱنطَلِقُوٓاْ إِلَىٰ مَا كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

Ku tafi zuwa ga abin da kuka kasance kuna qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 30

ٱنطَلِقُوٓاْ إِلَىٰ ظِلّٖ ذِي ثَلَٰثِ شُعَبٖ

Ku tafi zuwa wata inuwa mai rassa uku