Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 1

وَٱلذَّـٰرِيَٰتِ ذَرۡوٗا

Na rantse da iskoki masu ta da qura



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 2

فَٱلۡحَٰمِلَٰتِ وِقۡرٗا

Sannan da (giragizai) waxanda suke xauke da nauyin ruwa



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 3

فَٱلۡجَٰرِيَٰتِ يُسۡرٗا

Da jiragen ruwa masu gudu a sauqaqe



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 4

فَٱلۡمُقَسِّمَٰتِ أَمۡرًا

Da kuma mala’iku masu raba abubuwa



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 5

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٞ

Lalle abin da ake yi muku alqawarinsa tabbas gaskiya ne



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 6

وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٞ

Kuma lalle sakamako tabbas mai afkuwa ne



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 7

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡحُبُكِ

Na rantse da sama ma’abociyar hanyoyi



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 8

إِنَّكُمۡ لَفِي قَوۡلٖ مُّخۡتَلِفٖ

Lalle ku (mutanen Makka) tabbas kuna cikin magana mai sassavawa



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 9

يُؤۡفَكُ عَنۡهُ مَنۡ أُفِكَ

Ana karkatar da wanda aka karkatar daga gare shi (Annabi ko Alqur’ani)



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 10

قُتِلَ ٱلۡخَرَّـٰصُونَ

An la’anci maqaryata[1]


1- Watau game da Annabi () da kuma Alqur’ani.


Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 11

ٱلَّذِينَ هُمۡ فِي غَمۡرَةٖ سَاهُونَ

Waxanda suke rafkanannu a cikin jahilci



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 12

يَسۡـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Suna tambayar yaushe ne ranar sakamako?



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 13

يَوۡمَ هُمۡ عَلَى ٱلنَّارِ يُفۡتَنُونَ

A ranar da su za a azabtar da su kan wuta



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 14

ذُوقُواْ فِتۡنَتَكُمۡ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَسۡتَعۡجِلُونَ

(A ce da su): “Ku xanxani azabarku, wannan shi ne abin da kuka kasance kuna neman gaggautowarsa.”



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 15

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٍ

Lalle masu taqawa suna cikin gidajen Aljanna da idanuwan (ruwa)



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 16

ءَاخِذِينَ مَآ ءَاتَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَبۡلَ ذَٰلِكَ مُحۡسِنِينَ

Suna masu kwasar abin da Ubangijinsu Ya ba su. Lalle su sun zamanto kafin wannan (ranar) masu kyautata ayyuka ne



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 17

كَانُواْ قَلِيلٗا مِّنَ ٱلَّيۡلِ مَا يَهۡجَعُونَ

Sun kasance kaxan ne na dare suke bacci[1]


1- Watau sun kasance masu yawaita sallar dare.


Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 18

وَبِٱلۡأَسۡحَارِ هُمۡ يَسۡتَغۡفِرُونَ

A gefin asuba kuma su suna neman gafara



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 19

وَفِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

A cikin dukiyoyinsu kuma akwai wani haqqi na mai bara da mai kamewa daga yin ta



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 20

وَفِي ٱلۡأَرۡضِ ءَايَٰتٞ لِّلۡمُوقِنِينَ

A cikin qasa kuma akwai ayoyi ga masu sakankancewa



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 21

وَفِيٓ أَنفُسِكُمۡۚ أَفَلَا تُبۡصِرُونَ

Da kuma cikin kawunanku. Yanzu ba kwa lura ba?



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 22

وَفِي ٱلسَّمَآءِ رِزۡقُكُمۡ وَمَا تُوعَدُونَ

A cikin sammai kuma akwai arzikinku da kuma abin da aka yi muku alkawarinsa



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 23

فَوَرَبِّ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ إِنَّهُۥ لَحَقّٞ مِّثۡلَ مَآ أَنَّكُمۡ تَنطِقُونَ

To na rantse da Ubangijin sammai da qasa, lalle shi (abin da ake yi muku gargaxinsa) tabbas gaskiya ne kamar dai yadda kuke yin magana



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 24

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيۡفِ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلۡمُكۡرَمِينَ

Shin labarin baqin Ibrahimu masu girma[1] ya zo maka?


1- Su ne mala’iku da Allah ya aiko.


Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 25

إِذۡ دَخَلُواْ عَلَيۡهِ فَقَالُواْ سَلَٰمٗاۖ قَالَ سَلَٰمٞ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ

Lokacin da suka shiga wurinsa sai suka ce: “Muna maka sallama;” ya ce: “Aminci ya tabbata gare ku, (ku) mutane ne da ba sanannu ba.”



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 26

فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجۡلٖ سَمِينٖ

Sai ya saxaxa da sauri zuwa ga iyalinsa, sai ya zo da wani xan maraqi mai mai



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 27

فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيۡهِمۡ قَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ

Sai ya kusanta shi gare su, ya ce: “Yanzu ba za ku ci ba?”



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 28

فَأَوۡجَسَ مِنۡهُمۡ خِيفَةٗۖ قَالُواْ لَا تَخَفۡۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٖ

(Da suka qi ci) sai ya tsorata da su, suka ce: “Kada ka tsorata;” suka kuma yi masa albishir da samun yaro mai ilimi[1]


1- Watau Annabi Ishaq ().


Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 29

فَأَقۡبَلَتِ ٱمۡرَأَتُهُۥ فِي صَرَّةٖ فَصَكَّتۡ وَجۡهَهَا وَقَالَتۡ عَجُوزٌ عَقِيمٞ

Sannan sai matarsa ta gabato su cikin wata qara, sai ta mari fuskarta ta ce: “Yanzu tsohuwa bakarara (ita ce za ta haihu?)”



Sure: Suratuz Zariyat

Vers : 30

قَالُواْ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡعَلِيمُ

Suka ce, “Kamar haka Ubangijinki Ya ce, lalle Shi Mai hikima ne, Masani.”