-
Sure :
Suratuz Zariyat
-
Teil:
26
-
Verszahl :
60
-
Versnummer :
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 1
وَٱلذَّـٰرِيَٰتِ ذَرۡوٗا
Na rantse da iskoki masu ta da qura
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 2
فَٱلۡحَٰمِلَٰتِ وِقۡرٗا
Sannan da (giragizai) waxanda suke xauke da nauyin ruwa
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 3
فَٱلۡجَٰرِيَٰتِ يُسۡرٗا
Da jiragen ruwa masu gudu a sauqaqe
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 4
فَٱلۡمُقَسِّمَٰتِ أَمۡرًا
Da kuma mala’iku masu raba abubuwa
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 5
إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٞ
Lalle abin da ake yi muku alqawarinsa tabbas gaskiya ne
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 6
وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٞ
Kuma lalle sakamako tabbas mai afkuwa ne
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 7
وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡحُبُكِ
Na rantse da sama ma’abociyar hanyoyi
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 8
إِنَّكُمۡ لَفِي قَوۡلٖ مُّخۡتَلِفٖ
Lalle ku (mutanen Makka) tabbas kuna cikin magana mai sassavawa
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 9
يُؤۡفَكُ عَنۡهُ مَنۡ أُفِكَ
Ana karkatar da wanda aka karkatar daga gare shi (Annabi ko Alqur’ani)
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 10
قُتِلَ ٱلۡخَرَّـٰصُونَ
An la’anci maqaryata[1]
1- Watau game da Annabi () da kuma Alqur’ani.
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 11
ٱلَّذِينَ هُمۡ فِي غَمۡرَةٖ سَاهُونَ
Waxanda suke rafkanannu a cikin jahilci
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 12
يَسۡـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Suna tambayar yaushe ne ranar sakamako?
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 13
يَوۡمَ هُمۡ عَلَى ٱلنَّارِ يُفۡتَنُونَ
A ranar da su za a azabtar da su kan wuta
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 14
ذُوقُواْ فِتۡنَتَكُمۡ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَسۡتَعۡجِلُونَ
(A ce da su): “Ku xanxani azabarku, wannan shi ne abin da kuka kasance kuna neman gaggautowarsa.”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 15
إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٍ
Lalle masu taqawa suna cikin gidajen Aljanna da idanuwan (ruwa)
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 16
ءَاخِذِينَ مَآ ءَاتَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَبۡلَ ذَٰلِكَ مُحۡسِنِينَ
Suna masu kwasar abin da Ubangijinsu Ya ba su. Lalle su sun zamanto kafin wannan (ranar) masu kyautata ayyuka ne
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 17
كَانُواْ قَلِيلٗا مِّنَ ٱلَّيۡلِ مَا يَهۡجَعُونَ
Sun kasance kaxan ne na dare suke bacci[1]
1- Watau sun kasance masu yawaita sallar dare.
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 18
وَبِٱلۡأَسۡحَارِ هُمۡ يَسۡتَغۡفِرُونَ
A gefin asuba kuma su suna neman gafara
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 19
وَفِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ
A cikin dukiyoyinsu kuma akwai wani haqqi na mai bara da mai kamewa daga yin ta
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 20
وَفِي ٱلۡأَرۡضِ ءَايَٰتٞ لِّلۡمُوقِنِينَ
A cikin qasa kuma akwai ayoyi ga masu sakankancewa
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 21
وَفِيٓ أَنفُسِكُمۡۚ أَفَلَا تُبۡصِرُونَ
Da kuma cikin kawunanku. Yanzu ba kwa lura ba?
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 22
وَفِي ٱلسَّمَآءِ رِزۡقُكُمۡ وَمَا تُوعَدُونَ
A cikin sammai kuma akwai arzikinku da kuma abin da aka yi muku alkawarinsa
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 23
فَوَرَبِّ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ إِنَّهُۥ لَحَقّٞ مِّثۡلَ مَآ أَنَّكُمۡ تَنطِقُونَ
To na rantse da Ubangijin sammai da qasa, lalle shi (abin da ake yi muku gargaxinsa) tabbas gaskiya ne kamar dai yadda kuke yin magana
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 24
هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيۡفِ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلۡمُكۡرَمِينَ
Shin labarin baqin Ibrahimu masu girma[1] ya zo maka?
1- Su ne mala’iku da Allah ya aiko.
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 25
إِذۡ دَخَلُواْ عَلَيۡهِ فَقَالُواْ سَلَٰمٗاۖ قَالَ سَلَٰمٞ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ
Lokacin da suka shiga wurinsa sai suka ce: “Muna maka sallama;” ya ce: “Aminci ya tabbata gare ku, (ku) mutane ne da ba sanannu ba.”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 26
فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجۡلٖ سَمِينٖ
Sai ya saxaxa da sauri zuwa ga iyalinsa, sai ya zo da wani xan maraqi mai mai
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 27
فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيۡهِمۡ قَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ
Sai ya kusanta shi gare su, ya ce: “Yanzu ba za ku ci ba?”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 28
فَأَوۡجَسَ مِنۡهُمۡ خِيفَةٗۖ قَالُواْ لَا تَخَفۡۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٖ
(Da suka qi ci) sai ya tsorata da su, suka ce: “Kada ka tsorata;” suka kuma yi masa albishir da samun yaro mai ilimi[1]
1- Watau Annabi Ishaq ().
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 29
فَأَقۡبَلَتِ ٱمۡرَأَتُهُۥ فِي صَرَّةٖ فَصَكَّتۡ وَجۡهَهَا وَقَالَتۡ عَجُوزٌ عَقِيمٞ
Sannan sai matarsa ta gabato su cikin wata qara, sai ta mari fuskarta ta ce: “Yanzu tsohuwa bakarara (ita ce za ta haihu?)”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratuz Zariyat
Vers : 30
قَالُواْ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡعَلِيمُ
Suka ce, “Kamar haka Ubangijinki Ya ce, lalle Shi Mai hikima ne, Masani.”
-
-
Fertig
Fehler
-