Sure: Suratu Fussilat

Vers : 1

حمٓ

HA MIM[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Sure: Suratu Fussilat

Vers : 2

تَنزِيلٞ مِّنَ ٱلرَّحۡمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

(Alqur’ani) saukakke ne daga (Allah) Mai rahama, Mai jin qai



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 3

كِتَٰبٞ فُصِّلَتۡ ءَايَٰتُهُۥ قُرۡءَانًا عَرَبِيّٗا لِّقَوۡمٖ يَعۡلَمُونَ

(Shi) Littafi ne Alqur’ani Balarabe da aka rarrabe ayoyinsa ga mutanen da suke sanin (ma’anarsa)



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 4

بَشِيرٗا وَنَذِيرٗا فَأَعۡرَضَ أَكۡثَرُهُمۡ فَهُمۡ لَا يَسۡمَعُونَ

Mai albishir ne kuma mai gargaxi, sai yawancinsu suka bijire, don haka su ba sa jin (kira)



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 5

وَقَالُواْ قُلُوبُنَا فِيٓ أَكِنَّةٖ مِّمَّا تَدۡعُونَآ إِلَيۡهِ وَفِيٓ ءَاذَانِنَا وَقۡرٞ وَمِنۢ بَيۡنِنَا وَبَيۡنِكَ حِجَابٞ فَٱعۡمَلۡ إِنَّنَا عَٰمِلُونَ

Suka kuma ce: “Zukatanmu suna cikin rufi game da abin da kuke kiran mu zuwa gare shi; a cikin kunnuwanmu kuma akwai nauyi[1], kuma tsakaninmu da kai akwai shamaki[2], sai ka yi aiki da (addininka), lalle mu ma masu yin aiki ne (da namu).”


1- Watau akwai kurumta tare da kunnuwansu, don haka ba sa jin duk wani kira da ake yi musu.


2- Wanda yake hana muryarsa isa zuwa inda suke.


Sure: Suratu Fussilat

Vers : 6

قُلۡ إِنَّمَآ أَنَا۠ بَشَرٞ مِّثۡلُكُمۡ يُوحَىٰٓ إِلَيَّ أَنَّمَآ إِلَٰهُكُمۡ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞ فَٱسۡتَقِيمُوٓاْ إِلَيۡهِ وَٱسۡتَغۡفِرُوهُۗ وَوَيۡلٞ لِّلۡمُشۡرِكِينَ

Ka ce: “Ni ba wani ba ne sai mutum kamarku, ana yiwo min wahayin cewa, abin bautarku abin bauta ne Guda Xaya, sai ku miqe kyam zuwa gare Shi, kuma ku nemi gafararsa. Tsananin azaba kuma ya tabbata ga mushirikai



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 7

ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡتُونَ ٱلزَّكَوٰةَ وَهُم بِٱلۡأٓخِرَةِ هُمۡ كَٰفِرُونَ

“Waxanda ba sa ba da zakka, kuma su masu kafircewa ne da (ranar) lahira.”



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 8

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ

Lalle waxanda suka yi imani kuma suka yi aiki nagari suna da lada marar yankewa



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 9

۞قُلۡ أَئِنَّكُمۡ لَتَكۡفُرُونَ بِٱلَّذِي خَلَقَ ٱلۡأَرۡضَ فِي يَوۡمَيۡنِ وَتَجۡعَلُونَ لَهُۥٓ أَندَادٗاۚ ذَٰلِكَ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ka ce: “Yanzu kwa riqa kafircewa da wanda Ya halicci qasa a cikin (gwargwadon) kwana biyu, kuna kuma sanya masa kishiyoyi? Wannan fa Shi ne Ubangijin talikai!



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 10

وَجَعَلَ فِيهَا رَوَٰسِيَ مِن فَوۡقِهَا وَبَٰرَكَ فِيهَا وَقَدَّرَ فِيهَآ أَقۡوَٰتَهَا فِيٓ أَرۡبَعَةِ أَيَّامٖ سَوَآءٗ لِّلسَّآئِلِينَ

“Ya kuma sanya kafaffun duwatsu a cikinta daga samanta, Ya kuma yi albarka a cikinta, Ya kuma qaddara dangogin abincinta a cikin kwana huxu (tare da kwanaki biyu na halittar qasa) daidai da daidai ga masu tambaya



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 11

ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰٓ إِلَى ٱلسَّمَآءِ وَهِيَ دُخَانٞ فَقَالَ لَهَا وَلِلۡأَرۡضِ ٱئۡتِيَا طَوۡعًا أَوۡ كَرۡهٗا قَالَتَآ أَتَيۡنَا طَآئِعِينَ

“Sannan Ya nufi zuwa sama, (a sannan) ita kuma hayaqi ce, sai Ya ce da ita da kuma qasa: “Ku zo cikin biyayya ko kuma bisa tilas.” Suka ce: ‘Mun zo muna masu biyayya’



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 12

فَقَضَىٰهُنَّ سَبۡعَ سَمَٰوَاتٖ فِي يَوۡمَيۡنِ وَأَوۡحَىٰ فِي كُلِّ سَمَآءٍ أَمۡرَهَاۚ وَزَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنۡيَا بِمَصَٰبِيحَ وَحِفۡظٗاۚ ذَٰلِكَ تَقۡدِيرُ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡعَلِيمِ

“Sai Ya mayar da su sammai bakwai a cikin kwana biyu, Ya kuma yi wa kowacce sama wahayin umarninta. Muka kuma qawata saman duniya da taurari da kuma tsaro[1]. Wannan tsari ne na Allah Mabuwayi, Masani.”


1- Watau daga aljannu masu qoqarin satar sauraro.


Sure: Suratu Fussilat

Vers : 13

فَإِنۡ أَعۡرَضُواْ فَقُلۡ أَنذَرۡتُكُمۡ صَٰعِقَةٗ مِّثۡلَ صَٰعِقَةِ عَادٖ وَثَمُودَ

To idan suka bijire sai ka ce: “Na tsoratar da ku da tsawa irin tsawar Adawa da Samudawa



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 14

إِذۡ جَآءَتۡهُمُ ٱلرُّسُلُ مِنۢ بَيۡنِ أَيۡدِيهِمۡ وَمِنۡ خَلۡفِهِمۡ أَلَّا تَعۡبُدُوٓاْ إِلَّا ٱللَّهَۖ قَالُواْ لَوۡ شَآءَ رَبُّنَا لَأَنزَلَ مَلَـٰٓئِكَةٗ فَإِنَّا بِمَآ أُرۡسِلۡتُم بِهِۦ كَٰفِرُونَ

“Lokacin da manzanninsu suka zo musu ta gabansu da ta bayansu[1] cewa: ‘Kada ku bauta wa komai sai Allah.’” Suka ce: “Da Ubangijinmu Ya ga dama, da Ya saukar da mala’iku, saboda haka mu lalle masu kafirce wa abin da aka aiko ku da shi ne.’”


1- Watau suka yi amfani da hanyoyi daban-daban domin isar musu da saqon Allah.


Sure: Suratu Fussilat

Vers : 15

فَأَمَّا عَادٞ فَٱسۡتَكۡبَرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ بِغَيۡرِ ٱلۡحَقِّ وَقَالُواْ مَنۡ أَشَدُّ مِنَّا قُوَّةًۖ أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ أَنَّ ٱللَّهَ ٱلَّذِي خَلَقَهُمۡ هُوَ أَشَدُّ مِنۡهُمۡ قُوَّةٗۖ وَكَانُواْ بِـَٔايَٰتِنَا يَجۡحَدُونَ

Amma Adawa sai suka yi girman kai a bayan qasa ba a kan gaskiya ba, suka kuma ce: “Wane ne ya fi mu tsananin qarfi?” Yanzu ba su ga cewa lalle Allah wanda Ya halicce su Ya fi su tsananin qarfi ba? Sun kuma kasance suna musanta ayoyinmu



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 16

فَأَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ رِيحٗا صَرۡصَرٗا فِيٓ أَيَّامٖ نَّحِسَاتٖ لِّنُذِيقَهُمۡ عَذَابَ ٱلۡخِزۡيِ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ وَلَعَذَابُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَخۡزَىٰۖ وَهُمۡ لَا يُنصَرُونَ

Sai Muka aiko musu da wata iska mai qara a wasu kwanaki masu cike da shu’umci don Mu xanxana musu azabar kunyata a rayuwar duniya; azabar lahira kuma ta fi kunyatarwa; alhalin su ba za a taimake su ba



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 17

وَأَمَّا ثَمُودُ فَهَدَيۡنَٰهُمۡ فَٱسۡتَحَبُّواْ ٱلۡعَمَىٰ عَلَى ٱلۡهُدَىٰ فَأَخَذَتۡهُمۡ صَٰعِقَةُ ٱلۡعَذَابِ ٱلۡهُونِ بِمَا كَانُواْ يَكۡسِبُونَ

Amma Samudawa kuma sai Muka nuna musu hanyar shiriya, sai suka zavi vata a kan shiriya, sai tsawar azabar wulaqanci ta kama su saboda abin da suka kasance suna tsuwurwuta



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 18

وَنَجَّيۡنَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَكَانُواْ يَتَّقُونَ

Muka kuma tserar da waxanda suka yi imani suka kuma kasance masu kiyaye dokokin Allah



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 19

وَيَوۡمَ يُحۡشَرُ أَعۡدَآءُ ٱللَّهِ إِلَى ٱلنَّارِ فَهُمۡ يُوزَعُونَ

(Ka tuna) kuma ranar da za a tara maqiya Allah zuwa wuta ana kuma kora su



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 20

حَتَّىٰٓ إِذَا مَا جَآءُوهَا شَهِدَ عَلَيۡهِمۡ سَمۡعُهُمۡ وَأَبۡصَٰرُهُمۡ وَجُلُودُهُم بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Har sai lokacin da suka zo mata, jinsu da ganinsu da fatunsu za su ba da shaida a kan abin da suka kasance suna aikatawa



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 21

وَقَالُواْ لِجُلُودِهِمۡ لِمَ شَهِدتُّمۡ عَلَيۡنَاۖ قَالُوٓاْ أَنطَقَنَا ٱللَّهُ ٱلَّذِيٓ أَنطَقَ كُلَّ شَيۡءٖۚ وَهُوَ خَلَقَكُمۡ أَوَّلَ مَرَّةٖ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Sai Suka ce da fatunsu: “Don me kuka ba da shaida a kanmu?” Suka ce: “Allah da Ya bai wa kowane abu ikon yin furuci mu ma Shi Ya ba mu ikon furuci, Shi ne kuma Ya halicce ku tun farko, gare Shi kuma kaxai za a mayar da ku.”



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 22

وَمَا كُنتُمۡ تَسۡتَتِرُونَ أَن يَشۡهَدَ عَلَيۡكُمۡ سَمۡعُكُمۡ وَلَآ أَبۡصَٰرُكُمۡ وَلَا جُلُودُكُمۡ وَلَٰكِن ظَنَنتُمۡ أَنَّ ٱللَّهَ لَا يَعۡلَمُ كَثِيرٗا مِّمَّا تَعۡمَلُونَ

Kuma ba ku kasance kuna voye (ayyukanku) ba, don gudun kada jinku da ganinku da fatunku su ba da shaida a kanku ba, sai dai kuna tsammanin cewa Allah ba Ya sane da yawancin abin da kuke aikatawa



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 23

وَذَٰلِكُمۡ ظَنُّكُمُ ٱلَّذِي ظَنَنتُم بِرَبِّكُمۡ أَرۡدَىٰكُمۡ فَأَصۡبَحۡتُم مِّنَ ٱلۡخَٰسِرِينَ

Wannan kuma shi ne zatonku da kuka yi ga Ubangijinku da ya hallakar da ku, sai kuka wayi gari cikin hasararru



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 24

فَإِن يَصۡبِرُواْ فَٱلنَّارُ مَثۡوٗى لَّهُمۡۖ وَإِن يَسۡتَعۡتِبُواْ فَمَا هُم مِّنَ ٱلۡمُعۡتَبِينَ

To idan ma sun yi haquri wuta ce dai makomarsu; idan kuma suka nemi kawo wani hanzari, to su ba sa cikin waxanda za a karvi hanzarinsu



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 25

۞وَقَيَّضۡنَا لَهُمۡ قُرَنَآءَ فَزَيَّنُواْ لَهُم مَّا بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَمَا خَلۡفَهُمۡ وَحَقَّ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقَوۡلُ فِيٓ أُمَمٖ قَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلِهِم مِّنَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِۖ إِنَّهُمۡ كَانُواْ خَٰسِرِينَ

Muka kuma haxa su da abokai (shaixanu), sai suka qawata musu abin da yake gabansu (na duniya) da abin da yake bayansu (na musun alqiyama), sai kalmar (azaba) ta tabbata a kansu (na zamantowa) cikin al’ummun da suka gabace su na aljannu da mutane; lalle su, sun kasance hasararru



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 26

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَا تَسۡمَعُواْ لِهَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ وَٱلۡغَوۡاْ فِيهِ لَعَلَّكُمۡ تَغۡلِبُونَ

Waxanda kuma suka kafirta suka ce: “Kada ku saurari wannan Alqur’ani, ku riqa yin hayaniya a cikinsa[1] don ku yi rinjaye.”


1- Watau ku riqa hayaniya da hargowa duk sanda ake karanta shi domin kada mutane su ji abin da ake faxa.


Sure: Suratu Fussilat

Vers : 27

فَلَنُذِيقَنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ عَذَابٗا شَدِيدٗا وَلَنَجۡزِيَنَّهُمۡ أَسۡوَأَ ٱلَّذِي كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

To tabbas za Mu xanxana wa waxanda suka kafirta azaba mai tsanani, kuma tabbas za mu saka musu da mafi munin abin da suka kasance suna aikatawa



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 28

ذَٰلِكَ جَزَآءُ أَعۡدَآءِ ٱللَّهِ ٱلنَّارُۖ لَهُمۡ فِيهَا دَارُ ٱلۡخُلۡدِ جَزَآءَۢ بِمَا كَانُواْ بِـَٔايَٰتِنَا يَجۡحَدُونَ

Wannan fa shi ne sakamakon maqiya Allah (watau) wuta; suna da gidan dawwama a cikinta; sakamako ne saboda abin da suka kasance suna musuntawa na ayoyinmu



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 29

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ رَبَّنَآ أَرِنَا ٱلَّذَيۡنِ أَضَلَّانَا مِنَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِ نَجۡعَلۡهُمَا تَحۡتَ أَقۡدَامِنَا لِيَكُونَا مِنَ ٱلۡأَسۡفَلِينَ

Waxanda kuma suka kafirta suka ce: “Ya Ubangijinmu, Ka nuna mana waxanda suka vatar da mu daga aljannu da mutane, mu sanya su a qarqashin dugaduganmu don su zamanto cikin na can qasan qasa.”



Sure: Suratu Fussilat

Vers : 30

إِنَّ ٱلَّذِينَ قَالُواْ رَبُّنَا ٱللَّهُ ثُمَّ ٱسۡتَقَٰمُواْ تَتَنَزَّلُ عَلَيۡهِمُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ أَلَّا تَخَافُواْ وَلَا تَحۡزَنُواْ وَأَبۡشِرُواْ بِٱلۡجَنَّةِ ٱلَّتِي كُنتُمۡ تُوعَدُونَ

Lalle waxanda suka ce: “Allah ne Ubangijinmu”, sannan suka tsaya kyam, to mala’iku za su sauko musu (lokacin mutuwa suna cewa): “Kada ku tsorata, kuma kada ku yi baqin ciki, kuma ku yi farin ciki da Aljanna wadda kuka kasance ana yi muku alqawarinta