Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 181

۞أَوۡفُواْ ٱلۡكَيۡلَ وَلَا تَكُونُواْ مِنَ ٱلۡمُخۡسِرِينَ

“Ku cika mudu kada kuma ku zamanto daga masu tauye (shi)



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 182

وَزِنُواْ بِٱلۡقِسۡطَاسِ ٱلۡمُسۡتَقِيمِ

“Kuma ku riqa yin awon nauyi da ma’auni na adalci



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 183

وَلَا تَبۡخَسُواْ ٱلنَّاسَ أَشۡيَآءَهُمۡ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

“Kada kuma ku tauye wa mutane kayayyakinsu, kuma kada ku yawaita varna a bayan qasa



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 184

وَٱتَّقُواْ ٱلَّذِي خَلَقَكُمۡ وَٱلۡجِبِلَّةَ ٱلۡأَوَّلِينَ

“Kuma ku kiyaye dokokin (Allah) wanda Ya halicce ku da kuma al’ummu na farko.”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 185

قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ

Suka ce: “Kai dai kana daga waxanda aka sihirce ne kawai



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 186

وَمَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ ٱلۡكَٰذِبِينَ

“Kuma kai ba kowa ba ne sai mutum kamarmu, kuma ma lalle muna zaton kana daga maqaryata!



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 187

فَأَسۡقِطۡ عَلَيۡنَا كِسَفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Sai ka jeho mana da yankuna (na azaba) daga sama in ka kasance daga masu gaskiya!”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 188

قَالَ رَبِّيٓ أَعۡلَمُ بِمَا تَعۡمَلُونَ

(Shu’aibu) Ya ce: “Ubangijina Ya fi kowa sanin abin da kuke aikatawa.”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 189

فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمۡ عَذَابُ يَوۡمِ ٱلظُّلَّةِۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٍ

Sai suka qaryata shi, sannan sai azabar yinin girgije (na wuta) ta kama su. Lalle ta kasance azabar wani yini ne mai girma



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 190

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; sai dai kuma yawancinsu ba su kasance muminai ba



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 191

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai rahama



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 192

وَإِنَّهُۥ لَتَنزِيلُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Kuma lalle shi (Alqur’ani) saukarwa ce ta Ubangijin talikai



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 193

نَزَلَ بِهِ ٱلرُّوحُ ٱلۡأَمِينُ

Ruhi amintacce (watau Jibrilu) ne ya sauko da shi



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 194

عَلَىٰ قَلۡبِكَ لِتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُنذِرِينَ

A bisa zuciyarka don ka zamanto daga masu gargaxi



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 195

بِلِسَانٍ عَرَبِيّٖ مُّبِينٖ

(Ya saukar da shi) da harshen Larabci mabayyani



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 196

وَإِنَّهُۥ لَفِي زُبُرِ ٱلۡأَوَّلِينَ

Kuma lalle shi yana daga cikin littattafan farko



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 197

أَوَلَمۡ يَكُن لَّهُمۡ ءَايَةً أَن يَعۡلَمَهُۥ عُلَمَـٰٓؤُاْ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Yanzu bai ishe su aya ba cewa, malaman Banu- Isra’ila sun san shi?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 198

وَلَوۡ نَزَّلۡنَٰهُ عَلَىٰ بَعۡضِ ٱلۡأَعۡجَمِينَ

Da kuwa Mun saukar da shi ga wani wanda ba Balarabe ba



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 199

فَقَرَأَهُۥ عَلَيۡهِم مَّا كَانُواْ بِهِۦ مُؤۡمِنِينَ

Sannan ya karanta musu shi, to da ba za su yi imani da shi ba



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 200

كَذَٰلِكَ سَلَكۡنَٰهُ فِي قُلُوبِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Kamar haka ne Muka shigar da shi (qaryata Annabi) cikin zukatan manyan masu laifi



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 201

لَا يُؤۡمِنُونَ بِهِۦ حَتَّىٰ يَرَوُاْ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَلِيمَ

Ba za su yi imani da shi ba har sai sun ga azaba mai raxaxi



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 202

فَيَأۡتِيَهُم بَغۡتَةٗ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Sannan (azabar) za ta zo musu ba zato ba tsammani, ba tare da suna sane ba



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 203

فَيَقُولُواْ هَلۡ نَحۡنُ مُنظَرُونَ

Sai su ce: “Yanzu za a saurara mana?”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 204

أَفَبِعَذَابِنَا يَسۡتَعۡجِلُونَ

Yanzu azabarmu suke neman gaggautowa?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 205

أَفَرَءَيۡتَ إِن مَّتَّعۡنَٰهُمۡ سِنِينَ

Ka ba Ni labari idan Muka jiyar da su daxi na tsawon shekaru



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 206

ثُمَّ جَآءَهُم مَّا كَانُواْ يُوعَدُونَ

Sannan kuma abin da ake yi musu alkawarin narko da shi ya zo musu



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 207

مَآ أَغۡنَىٰ عَنۡهُم مَّا كَانُواْ يُمَتَّعُونَ

Abin da ake jiyar da su daxi a da ba zai amfana musu komai ba



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 208

وَمَآ أَهۡلَكۡنَا مِن قَرۡيَةٍ إِلَّا لَهَا مُنذِرُونَ

Ba Mu tava hallaka wata al’umma ba face sai ta samu masu yi mata gargaxi



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 209

ذِكۡرَىٰ وَمَا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

(Wannan) tunatarwa ce (gare su), ba Mu kuwa kasance azzalumai ba



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 210

وَمَا تَنَزَّلَتۡ بِهِ ٱلشَّيَٰطِينُ

Kuma shaixanu ba su sauko da shi ba