Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 121

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 122

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 123

كَذَّبَتۡ عَادٌ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Adawa (ma) sun qaryata manzanni[1]


1- Domin qaryata Annabi Hudu () daidai yake da qaryata duk manzannin Allah, saboda saqo iri xaya suke xauke da shi.


Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 124

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Hudu ya ce da su: “Yanzu ba kwa riqa kiyaye dokokin (Allah) ba?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 125

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 126

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 127

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 128

أَتَبۡنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ ءَايَةٗ تَعۡبَثُونَ

“Yanzu kwa riqa yin dogayen gine-gine a kan tuddai kuna sharholiya?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 129

وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمۡ تَخۡلُدُونَ

“Kuma ku riqa gina ganuwoyi da maka-makan gidaje kamar za ku dawwama?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 130

وَإِذَا بَطَشۡتُم بَطَشۡتُمۡ جَبَّارِينَ

“Idan kuma kuka yi damqa sai kukan yi damqa da tsanani



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 131

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 132

وَٱتَّقُواْ ٱلَّذِيٓ أَمَدَّكُم بِمَا تَعۡلَمُونَ

“Kuma ku kiyaye dokokin (Allah) wanda Ya ni’imta ku da abin da kuka sani



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 133

أَمَدَّكُم بِأَنۡعَٰمٖ وَبَنِينَ

“Ya ni’imta ku da dabbobin ni’ima da ‘ya’ya



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 134

وَجَنَّـٰتٖ وَعُيُونٍ

“Da kuma gonakai da idanuwan ruwa



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 135

إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٖ

“Lalle ni ina jiye muku tsoron azabar wani yini mai girma.”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 136

قَالُواْ سَوَآءٌ عَلَيۡنَآ أَوَعَظۡتَ أَمۡ لَمۡ تَكُن مِّنَ ٱلۡوَٰعِظِينَ

Suka ce: “Mu duk xaya ne a wajenmu; ko ka yi wa’azi ko kuwa kada ka zamanto daga masu wa’azi



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 137

إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا خُلُقُ ٱلۡأَوَّلِينَ

“Wannan ba wani abu ba ne in ban da halayyar mutanen farko



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 138

وَمَا نَحۡنُ بِمُعَذَّبِينَ

“Mu kuma ba waxanda za a yi wa azaba ba ne.”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 139

فَكَذَّبُوهُ فَأَهۡلَكۡنَٰهُمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Sai suka qaryata shi, sannan Muka hallaka su. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 140

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 141

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Samudawa sun qaryata manzanni[1]


1- Domin qaryata Annabi Salihu () daidai yake da qaryata duk manzannin Allah, saboda saqo iri xaya suke xauke da shi.


Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 142

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ صَٰلِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Salihu ya ce da su: “Yanzu ba kwa yi taqawa ba?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 143

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 144

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 145

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 146

أَتُتۡرَكُونَ فِي مَا هَٰهُنَآ ءَامِنِينَ

“Yanzu (zatonku) za a bar ku ne cikin abin da yake a nan (duniya) cikin kwanciyar hankali?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 147

فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

“(Watau) a cikin gonaki da idandunan ruwa?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 148

وَزُرُوعٖ وَنَخۡلٖ طَلۡعُهَا هَضِيمٞ

“Da shuke-shuke da dabinai masu taushin ‘ya’ya?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 149

وَتَنۡحِتُونَ مِنَ ٱلۡجِبَالِ بُيُوتٗا فَٰرِهِينَ

“Kuma kuna fafe duwatsu kuna yin gidaje kuna masu nuna qwarewa?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 150

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni