Sure: Suratus Saffat

Vers : 91

فَرَاغَ إِلَىٰٓ ءَالِهَتِهِمۡ فَقَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ

Sai ya saxaxa zuwa ga gumakansu ya ce (da su): “Yanzu ba za ku ci (abincin da ke gabanku) ba?



Sure: Suratus Saffat

Vers : 92

مَا لَكُمۡ لَا تَنطِقُونَ

“Me ya sa ba kwa yin magana ne?”



Sure: Suratus Saffat

Vers : 93

فَرَاغَ عَلَيۡهِمۡ ضَرۡبَۢا بِٱلۡيَمِينِ

Sai ya yi kansu yana duka da hannunsa na dama



Sure: Suratus Saffat

Vers : 94

فَأَقۡبَلُوٓاْ إِلَيۡهِ يَزِفُّونَ

Sai (mutanensa) suka fuskanto shi suna gaggawa



Sure: Suratus Saffat

Vers : 95

قَالَ أَتَعۡبُدُونَ مَا تَنۡحِتُونَ

Ya ce: “Yanzu kwa riqa bauta wa abin da kuke sassaqawa?



Sure: Suratus Saffat

Vers : 96

وَٱللَّهُ خَلَقَكُمۡ وَمَا تَعۡمَلُونَ

“Alhali kuwa Allah ne Ya halicce ku, da ma abin da kuke aikatawa?”



Sure: Suratus Saffat

Vers : 97

قَالُواْ ٱبۡنُواْ لَهُۥ بُنۡيَٰنٗا فَأَلۡقُوهُ فِي ٱلۡجَحِيمِ

Suka ce: “Ku gina masa wani gini (ku haxa wuta a ciki), sannan ku jefa shi cikin wutar.”



Sure: Suratus Saffat

Vers : 98

فَأَرَادُواْ بِهِۦ كَيۡدٗا فَجَعَلۡنَٰهُمُ ٱلۡأَسۡفَلِينَ

Sai suka yi nufin sa da mugun shiri, sai Muka mayar da su mafiya qasqanci



Sure: Suratus Saffat

Vers : 99

وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهۡدِينِ

Ya kuma ce: “Lalle ni zan yi qaura zuwa ga Ubangijina, zai ko shiryar da ni



Sure: Suratus Saffat

Vers : 100

رَبِّ هَبۡ لِي مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

“Ya Ubangijina, Ka yi min baiwa da (xa) ya zama daga (mutane) nagari.”



Sure: Suratus Saffat

Vers : 101

فَبَشَّرۡنَٰهُ بِغُلَٰمٍ حَلِيمٖ

Sai Muka yi masa albishir da yaro mai haquri[1]


1- Shi ne xansa Annabi Isma’il ().


Sure: Suratus Saffat

Vers : 102

فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ ٱلسَّعۡيَ قَالَ يَٰبُنَيَّ إِنِّيٓ أَرَىٰ فِي ٱلۡمَنَامِ أَنِّيٓ أَذۡبَحُكَ فَٱنظُرۡ مَاذَا تَرَىٰۚ قَالَ يَـٰٓأَبَتِ ٱفۡعَلۡ مَا تُؤۡمَرُۖ سَتَجِدُنِيٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

To lokacin da ya kai matsayin yin aiki tare da shi, sai ya ce: “Ya kai xana, lalle na ga ina yanka ka a cikin mafarki, sai ka yi tunani me ka gani?” Sai ya ce: “Ya babana, ka aikata duk abin da aka umarce ka, za ka same ni insha Allahu daga cikin masu haquri.”



Sure: Suratus Saffat

Vers : 103

فَلَمَّآ أَسۡلَمَا وَتَلَّهُۥ لِلۡجَبِينِ

To lokacin da suka sallama wa (Allah), ya kuma kwantar da shi ta xaya gefe na goshinsa (da nufin ya yanka shi)



Sure: Suratus Saffat

Vers : 104

وَنَٰدَيۡنَٰهُ أَن يَـٰٓإِبۡرَٰهِيمُ

Sai Muka kira shi da cewa: “Ya Ibrahimu



Sure: Suratus Saffat

Vers : 105

قَدۡ صَدَّقۡتَ ٱلرُّءۡيَآۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

“Haqiqa ka gaskata mafarkin.” Lalle Mu kamar haka ne Muke saka wa masu kyautatawa



Sure: Suratus Saffat

Vers : 106

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلۡبَلَـٰٓؤُاْ ٱلۡمُبِينُ

Lalle wannan tabbas shi ne bala’i qarara



Sure: Suratus Saffat

Vers : 107

وَفَدَيۡنَٰهُ بِذِبۡحٍ عَظِيمٖ

Muka kuma fanshe shi da abin yankawa mai girma



Sure: Suratus Saffat

Vers : 108

وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

Muka kuma bar (kyakkyawan yabo) a gare shi ga ‘yan baya



Sure: Suratus Saffat

Vers : 109

سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِبۡرَٰهِيمَ

Aminci ya tabbata ga Ibrahimu



Sure: Suratus Saffat

Vers : 110

كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Kamar haka ne Muke saka wa masu kyautatawa



Sure: Suratus Saffat

Vers : 111

إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle shi yana daga cikin bayinmu muminai



Sure: Suratus Saffat

Vers : 112

وَبَشَّرۡنَٰهُ بِإِسۡحَٰقَ نَبِيّٗا مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Muka kuma yi masa albishir da Is’haqa a matsayin Annabi daga salihai



Sure: Suratus Saffat

Vers : 113

وَبَٰرَكۡنَا عَلَيۡهِ وَعَلَىٰٓ إِسۡحَٰقَۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحۡسِنٞ وَظَالِمٞ لِّنَفۡسِهِۦ مُبِينٞ

Muka kuma yi masa albarka, da kuma Is’haqa. Daga zuriyarsu kuma akwai mai kyautatawa akwai kuma mai zaluntar kansa a fili (wato kafiri)



Sure: Suratus Saffat

Vers : 114

وَلَقَدۡ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

Haqiqa kuma Mun yi ni’ima ga Musa da Haruna



Sure: Suratus Saffat

Vers : 115

وَنَجَّيۡنَٰهُمَا وَقَوۡمَهُمَا مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ

Muka kuma tserar da su da mutanensu daga babban baqin ciki



Sure: Suratus Saffat

Vers : 116

وَنَصَرۡنَٰهُمۡ فَكَانُواْ هُمُ ٱلۡغَٰلِبِينَ

Muka kuma taimake su, sai suka kasance su ne masu rinjaye



Sure: Suratus Saffat

Vers : 117

وَءَاتَيۡنَٰهُمَا ٱلۡكِتَٰبَ ٱلۡمُسۡتَبِينَ

Muka kuma ba su Littafi mabayyani (Attaura)



Sure: Suratus Saffat

Vers : 118

وَهَدَيۡنَٰهُمَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلۡمُسۡتَقِيمَ

Muka kuma shiryar da su hanya madaidaiciya



Sure: Suratus Saffat

Vers : 119

وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِمَا فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

Muka kuma bar (kyakkyawan yabo) a gare su ga ‘yan baya



Sure: Suratus Saffat

Vers : 120

سَلَٰمٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

Aminci ya tabbata ga Musa da Haruna