Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 61

فَلَمَّا تَرَـٰٓءَا ٱلۡجَمۡعَانِ قَالَ أَصۡحَٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدۡرَكُونَ

To lokacin da jama’ar biyu suka ga juna, sai sahabban Musa suka ce: “Lalle tabbas mu za a cim mana.”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 62

قَالَ كَلَّآۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهۡدِينِ

(Musa) ya ce: “A’a; Ubangijina Yana tare da ni, zai kuwa shiryar da ni (hanyar tsira).”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 63

فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡبَحۡرَۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرۡقٖ كَٱلطَّوۡدِ ٱلۡعَظِيمِ

Sai Muka yi wahayi ga Musa cewa: “Ka bugi kogin da sandarka;” (da ya buge shi) sai ya dare, kowanne yanki sai ya zama kamar qaton dutse



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 64

وَأَزۡلَفۡنَا ثَمَّ ٱلۡأٓخَرِينَ

Muka kuma kusantar da waxancan (watau mutanen Fir’auna) zuwa can (kusa da kogin)



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 65

وَأَنجَيۡنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

Muka kuma tserar da Musa da waxanda suke tare da shi gaba xaya



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 66

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka nutsar da sauran mutanen (watau Fir’auna da mutanensa)



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 67

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 68

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijika tabbas Shi Mabuwayi ne, Mai rahama



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 69

وَٱتۡلُ عَلَيۡهِمۡ نَبَأَ إِبۡرَٰهِيمَ

Kuma ka karanta musu labarin Ibrahimu?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 70

إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦ مَا تَعۡبُدُونَ

Lokacin da ya ce wa babansa da kuma mutanensa: “Me kuke bauta wa?”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 71

قَالُواْ نَعۡبُدُ أَصۡنَامٗا فَنَظَلُّ لَهَا عَٰكِفِينَ

Suka ce: “Muna bauta wa gumaka ne, sai mukan duqufa wajen bautarsu.”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 72

قَالَ هَلۡ يَسۡمَعُونَكُمۡ إِذۡ تَدۡعُونَ

(Ibrahimu) ya ce: “Shin suna jin ku kuwa lokacin da kuke kiran su?



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 73

أَوۡ يَنفَعُونَكُمۡ أَوۡ يَضُرُّونَ

“Ko kuwa suna amfanar ku ne, ko suna cutarwa?”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 74

قَالُواْ بَلۡ وَجَدۡنَآ ءَابَآءَنَا كَذَٰلِكَ يَفۡعَلُونَ

Suka ce: “A’a; mun sami iyayenmu ne suna aikata kamar haka.”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 75

قَالَ أَفَرَءَيۡتُم مَّا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ

(Ibrahimu) ya ce: “Yanzu kun ga abin nan da kuka kasance kuna bautawa



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 76

أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُمُ ٱلۡأَقۡدَمُونَ

“Ku da iyayenku da suka gabata



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 77

فَإِنَّهُمۡ عَدُوّٞ لِّيٓ إِلَّا رَبَّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“To lalle su abokan gabata ne sai fa Ubangijin talikai



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 78

ٱلَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهۡدِينِ

“Wanda Ya halicce ni, to Shi ne Yake shiryar da ni



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 79

وَٱلَّذِي هُوَ يُطۡعِمُنِي وَيَسۡقِينِ

“Kuma wanda Shi ne Yake ciyar da ni kuma Yake shayar da ni



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 80

وَإِذَا مَرِضۡتُ فَهُوَ يَشۡفِينِ

“Idan kuma na yi rashin lafiya, to Shi ne zai warkar da ni



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 81

وَٱلَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحۡيِينِ

“Kuma wanda zai kashe ni sannan Ya (sake) raya ni



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 82

وَٱلَّذِيٓ أَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لِي خَطِيٓـَٔتِي يَوۡمَ ٱلدِّينِ

“Wanda kuma nake kwaxayin Ya gafarta min kurakuraina ranar sakamako



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 83

رَبِّ هَبۡ لِي حُكۡمٗا وَأَلۡحِقۡنِي بِٱلصَّـٰلِحِينَ

“Ubangijina Ka hore min ilimi, kuma Ka haxa ni da (bayinka) na gari



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 84

وَٱجۡعَل لِّي لِسَانَ صِدۡقٖ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

“Kuma Ka sanya min abin kyakkyawan ambato cikin ‘yan baya



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 85

وَٱجۡعَلۡنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ

“Kuma Ka sanya ni cikin magada Aljannar ni’ima



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 86

وَٱغۡفِرۡ لِأَبِيٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ

“Kuma Ka gafarta wa babana, lalle shi ya zamo cikin vatattu.[1]


1- Ya yi masa wannan addu’a ne tun gabanin a hana shi, kamar yadda ya zo a cikin Suratut Tauba, aya ta 114.


Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 87

وَلَا تُخۡزِنِي يَوۡمَ يُبۡعَثُونَ

“Kada kuma Ka kunyata ni ranar da za a tashe su



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 88

يَوۡمَ لَا يَنفَعُ مَالٞ وَلَا بَنُونَ

“Ranar da dukiya da ‘ya’yaye ba sa amfani



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 89

إِلَّا مَنۡ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلۡبٖ سَلِيمٖ

“Sai dai wanda ya zo wa Allah da lafiyayyar zuciya.”



Sure: Suratus Shu’ara

Vers : 90

وَأُزۡلِفَتِ ٱلۡجَنَّةُ لِلۡمُتَّقِينَ

Aka kuma kusantar da Aljanna ga masu taqawa