Sure: Suratul Mursalat

Vers : 31

لَّا ظَلِيلٖ وَلَا يُغۡنِي مِنَ ٱللَّهَبِ

Ba mai ba da inuwa ba kuma ba mai karewa daga harshen wuta ba



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 32

إِنَّهَا تَرۡمِي بِشَرَرٖ كَٱلۡقَصۡرِ

Haqiqa ita tana jefa tartsatsi kamar qaton gini



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 33

كَأَنَّهُۥ جِمَٰلَتٞ صُفۡرٞ

Kai ka ce su raquma ne baqaqe



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 34

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 35

هَٰذَا يَوۡمُ لَا يَنطِقُونَ

Wannan ita ce ranar da ba sa magana



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 36

وَلَا يُؤۡذَنُ لَهُمۡ فَيَعۡتَذِرُونَ

Kuma ba za a yi musu izini ba balle su kawo hanzari



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 37

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 38

هَٰذَا يَوۡمُ ٱلۡفَصۡلِۖ جَمَعۡنَٰكُمۡ وَٱلۡأَوَّلِينَ

Wannan ita ce rana ta yin hukunci da Muka tara ku da na farko



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 39

فَإِن كَانَ لَكُمۡ كَيۡدٞ فَكِيدُونِ

To idan kuna da wani tanadi na makirci sai ku qulla Mini



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 40

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 41

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي ظِلَٰلٖ وَعُيُونٖ

Lalle masu taqawa suna cikin inuwoyi da idanuwan ruwa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 42

وَفَوَٰكِهَ مِمَّا يَشۡتَهُونَ

Da kuma ababan marmari daga abin da suke sha’awa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 43

كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ هَنِيٓـَٔۢا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Ku ci kuma ku sha kuna masu farin ciki saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 44

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 45

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 46

كُلُواْ وَتَمَتَّعُواْ قَلِيلًا إِنَّكُم مُّجۡرِمُونَ

Ku ci kuma ku ji daxi kaxan (a duniya), lalle ku kun tabbata manyan masu laifi



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 47

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 48

وَإِذَا قِيلَ لَهُمُ ٱرۡكَعُواْ لَا يَرۡكَعُونَ

Idan kuma aka ce da su: “Ku yi ruku’u”, to ba za su yi ruku’u ba



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 49

وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ

Tsananin azaba ya tabbata a wannan ranar ga masu qaryatawa



Sure: Suratul Mursalat

Vers : 50

فَبِأَيِّ حَدِيثِۭ بَعۡدَهُۥ يُؤۡمِنُونَ

To da wane irin zance ne bayansa (Alqur’ani) za su yi imani?