Sure: Suratul Muddassir

Vers : 31

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ

Ba Mu kuwa sanya masu tsaron wutar ba sai mala’iku, ba Mu kuma sanya adadinsu ba sai don fitina ga waxanda suka kafirta, don kuma waxanda aka bai wa littafi su sami yaqini, waxanda kuma suka yi imani su qara imani, waxanda aka bai wa littafi da muminai kuma kada su yi tababa, don kuma waxanda suke da raunin imani a zukatansu da kuma kafirai su ce: “Me Allah Yake nufi da yin misali da wannan (adadin)?” Kamar haka Allah Yake vatar da wanda Ya ga dama, Yake kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Ba kuma wanda ya san (yawan) rundunar Ubangijinka sai Shi. Ita (Saqara) kuma ba wata abu ba ce face wa’azi ga mutane



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 32

كَلَّا وَٱلۡقَمَرِ

A’a. Na rantse da wata



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 33

وَٱلَّيۡلِ إِذۡ أَدۡبَرَ

Da kuma dare idan ya ba da baya



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 34

وَٱلصُّبۡحِ إِذَآ أَسۡفَرَ

Da kuma asuba idan ta bayyana (da haskenta)



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 35

إِنَّهَا لَإِحۡدَى ٱلۡكُبَرِ

Lalle ita (Saqara) tana xaya daga manya-manyan (bala’o’i)



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 36

نَذِيرٗا لِّلۡبَشَرِ

Gargaxi ce ga mutane



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 37

لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَتَقَدَّمَ أَوۡ يَتَأَخَّرَ

Ga wanda ya ga dama daga cikinku, ya ci gaba ko ya ci baya



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 38

كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ رَهِينَةٌ

Kowane rai jingina ne ga abin da ya tsuwurwurta[1]


1- Watau jingina ne ga ayyukansu, ko dai su hallakar da shi ko su kuvutar da shi, su ‘yanta shi.


Sure: Suratul Muddassir

Vers : 39

إِلَّآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡيَمِينِ

Sai dai ga ma’abota dama[1]


1- Watau waxanda za su karvi littattafan ayyukansu ta hannayensu na dama.


Sure: Suratul Muddassir

Vers : 40

فِي جَنَّـٰتٖ يَتَسَآءَلُونَ

(Su kam suna) cikin gidajen Aljanna suna tambayar juna



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 41

عَنِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Game da manyan masu laifuka



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 42

مَا سَلَكَكُمۡ فِي سَقَرَ

(Suna cewa): “Me ya shigar da ku cikin Saqara?”



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 43

قَالُواْ لَمۡ نَكُ مِنَ ٱلۡمُصَلِّينَ

Suka ce: “Ba mu zama daga cikin masallata ba



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 44

وَلَمۡ نَكُ نُطۡعِمُ ٱلۡمِسۡكِينَ

“Kuma ba mu kasance muna ciyar da miskini ba



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 45

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلۡخَآئِضِينَ

“Mun kuma kasance muna kutsawa (cikin varna)[1] tare da masu kutsawa


1- Watau suna faxar qarerayi game da Annabi () da Alqur’ani.


Sure: Suratul Muddassir

Vers : 46

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

“Kuma mun kasance muna qaryata ranar sakamako



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 47

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلۡيَقِينُ

“Har mutuwa ta zo mana.”



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 48

فَمَا تَنفَعُهُمۡ شَفَٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ

Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane su ba



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 49

فَمَا لَهُمۡ عَنِ ٱلتَّذۡكِرَةِ مُعۡرِضِينَ

To me ya same su ne suke bijire wa wa’azi?



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 50

كَأَنَّهُمۡ حُمُرٞ مُّسۡتَنفِرَةٞ

Kai ka ce su jakunan jeji ne da aka firgitar



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 51

فَرَّتۡ مِن قَسۡوَرَةِۭ

Da suka guje wa zaki



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 52

بَلۡ يُرِيدُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُؤۡتَىٰ صُحُفٗا مُّنَشَّرَةٗ

A’a, kowane mutum daga cikinsu yana so ne a ba shi takardu buxaxxu[1] (kafin su bi Annabi)


1- Watau a ba shi buxaxxen littafi wanda zai ba shi labari cewa Annabi Muhammadu () Manzon Allah ne.


Sure: Suratul Muddassir

Vers : 53

كَلَّاۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ

Faufau! A’a, su dai ba sa tsoron ranar lahira ne



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 54

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذۡكِرَةٞ

Tabbas, lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 55

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

To duk wanda ya ga dama sai ya wa’azantu



Sure: Suratul Muddassir

Vers : 56

وَمَا يَذۡكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ هُوَ أَهۡلُ ٱلتَّقۡوَىٰ وَأَهۡلُ ٱلۡمَغۡفِرَةِ

Ba sa kuma wa’azantuwa sai idan Allah Ya ga dama. Shi ne Ya cancanci taqawa, kuma Shi ne Ya cancanci yin gafara