Sure: Suratul Haqqa

Vers : 31

ثُمَّ ٱلۡجَحِيمَ صَلُّوهُ

Sannan ku shigar da shi (wutar) Jahimu



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 32

ثُمَّ فِي سِلۡسِلَةٖ ذَرۡعُهَا سَبۡعُونَ ذِرَاعٗا فَٱسۡلُكُوهُ

Sannan ku sa shi cikin sarqa mai tsawo kamu saba’in



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 33

إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ ٱلۡعَظِيمِ

Lalle shi ya kasance ba ya imani da Allah Mai girma



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 34

وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلۡمِسۡكِينِ

Ba ya kuma kwaxaitarwa bisa ciyar da mabuqaci



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 35

فَلَيۡسَ لَهُ ٱلۡيَوۡمَ هَٰهُنَا حَمِيمٞ

To a yau ba shi da wani masoyi a nan



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 36

وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنۡ غِسۡلِينٖ

Kuma ba shi da wani abinci sai na mugunyar ‘yan wuta



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 37

لَّا يَأۡكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلۡخَٰطِـُٔونَ

Ba mai cin ta sai masu laifukan ganganci



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 38

فَلَآ أُقۡسِمُ بِمَا تُبۡصِرُونَ

Ina yin rantsuwa da abin da kuke gani



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 39

وَمَا لَا تُبۡصِرُونَ

Da kuma abin da ba kwa gani



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 40

إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ

Lalle shi (Alqur’ani) tabbas zance ne na wani manzo mai girma



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 41

وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَاعِرٖۚ قَلِيلٗا مَّا تُؤۡمِنُونَ

Shi kuwa ba zancen mawaqi ba ne. Kaxan ne qwarai kuke yin imani



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 42

وَلَا بِقَوۡلِ كَاهِنٖۚ قَلِيلٗا مَّا تَذَكَّرُونَ

Ba kuma zance ne na boka ba. Kaxan ne qwarai kuke wa’azantuwa



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 43

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Shi saukakke ne daga Ubangijin halittu



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 44

وَلَوۡ تَقَوَّلَ عَلَيۡنَا بَعۡضَ ٱلۡأَقَاوِيلِ

Kuma da ya qaga Mana wasu maganganu



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 45

لَأَخَذۡنَا مِنۡهُ بِٱلۡيَمِينِ

Tabbas da Mun kama shi da qarfi



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 46

ثُمَّ لَقَطَعۡنَا مِنۡهُ ٱلۡوَتِينَ

Sannan da Mun yanke masa jijiyar zuciyarsa



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 47

فَمَا مِنكُم مِّنۡ أَحَدٍ عَنۡهُ حَٰجِزِينَ

Sannan kuma ba wani xaya daga cikinku da zai kare shi



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 48

وَإِنَّهُۥ لَتَذۡكِرَةٞ لِّلۡمُتَّقِينَ

Lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne ga masu kiyaye dokokin Allah



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 49

وَإِنَّا لَنَعۡلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ

Lalle kuma Mu Muna sane da cewa a cikinku akwai masu qaryatawa



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 50

وَإِنَّهُۥ لَحَسۡرَةٌ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma lalle shi tabbas nadama ce ga kafirai



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 51

وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلۡيَقِينِ

Kuma lalle shi tabbas gaskiya ce ta sakankancewa



Sure: Suratul Haqqa

Vers : 52

فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ

Saboda haka ka yi tasbihi da sunan Ubangijinka Mai girma